Showing 18001 words to 21000 words out of 133328 words

Chapter 7 - BAKAR WASIKA complete

Start ads

24 Aug 2025

457

Middle Ads

ke zubar da jini. Kamin su karasa inda suke zaton dakin da Sanusi yake ne, Isah ya fito yana kuka.

“Lafiya?”

“Baba babu Sanusi, Sanusi ya tafi sai dai idan mun isko shi, Allah ya jikanka Sanusi...”

Ya fada yana kuka, sai ga gawarsa an fito da ita. Aminatu bata san lokacin data saki rigar Baba ba ta ruga da gudu gurin gawarsa, duk ita duk tsoron gawa da take yau ta manta da wannan.

“Wayyo Allah na shiga uku, Ya Sanusi”

Sai kuma ta juyo da gudu gurin Baba dake kuka ta rike shi.

“Baba kai yi wani abu dan Allah Ya Sanusi ya tashi”

Baba ya girgiza mata kai yana wasu irin hawaye masu zafi.

“Ba ni da rayuwa Aminatu, sai hakuri”

Sai ta sulale kasa ta fashe da kuka.

“Wayyo na rasa Yaya mai sani dariya, yayana mai tsokanata, Yayana mai so na”

Baba ya duka kamar zai mata magana sai dai shi ma bashi da zuciyar yin haka a yanzu, sai ya kara fashewa da kuka.

“Allah ya Isar mana Allah ka isar mana”

Isah ya fada yana kuka, duk wani mai sauran imani da tausayi sai da idonsa ya cika da hawaye saboda tausayi. Zunbur tai ta tashi tsaye.

“Baba ku duba kila be mutu ba...”

Rugawa tai zata tafi gurin gawar sai Isah ya riketa, wani irin tsalle tai tana son ta kwaci kanta daga rikon da yai mata amman ta kasa, ta fisgi kanta ta fisga ta sake fisga ta sai fashe da tana jin kamar ace yau akwai abun da zata iya yi ta dawo da rayuwar Sanusi.



>>>>>>

If you want to subscribe pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, and send the evidence to 08036126660, zan yi adding dinki paid group In-sha-Allah.


________

Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata. Akwai dan wata bakwai.
Ga masu bukata za su iya tuntubar number nan 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah.

Serious Buyers Please idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci.
*💔 BAKAR WASIKA 💔*


By Khadeeja Candy


Page -6️⃣

Bakincikin mutuwa, da damuwar rasa rai, wani irin bakinciki ne da yake ma kansa muhalli a zuciyar bawa, baki yayi kadan ya bayyana yadda zuciyata take ji, haka zuciya ma ba zata iya daukar abun ita kadai ba har sai da taimakon idanuwa da gangan jiki.
Taya Aminatu zata fadawa kowa yadda take ji? Taya zata rasa yayyu biyar maza kuma ta kasa kuka? Taya za a maida garinsu da gidansu kamar kufai kuma ta kasa kuka? Taya za a keta haddi mahaifiyarta a gaban idonta kuma ta kasa kuka?
A tsakanin rasa yan'uwanta da kone musu abinci da keta haddin mahaifiyarta bata san wani yafi wani zafi ba. Anya zata iya dauka?

“Duk ni kadai?”

Ta furta wasu hawaye mazu zafi na sauko mata, kana ganin yanayinta da kuma jin kalaminta kasan bata cikin hayyacinta, ruwan hawayen dake mata zuba har ya canja launin fatar idonta, ya kumbura mata ido, kwayar idon kuma ta mata ja sosai.

“Auta dan Allah ki yi hakuri, haba kowa ba yana da tabon mutane nan a garin nan”

Anty Aina'u matar Bashiru ta fada tana kai hannu ta dafa ta. Aminatu ta kalleta kamar tace mata shiga zuciyata ki gani, sai kuma ta dauke kai ta hadeye yawu.
Har aka yi gaisuwar kwana uku aka watse Amintu bata daina kuka ba, kukan da ta sha ko Inna bata yi ba, domin Inna ta bar komai a zuciyarta ne, idan ta yunkurin kukan ma baya zuwa mata, sai dai bata iya komai ko bandaki zata zagaya sai an rikata. Idan kuma ta zauna ta sanda kai kasa bata iya dagowa sai an rika kan nata an dago da ita. Kana ganinta ka san kukan zuci take wanda ya fi na ido illa.
Washe garin Ranar da aka watse Aminatu na tsakar gida tana wanke wanken kayan abincinsu, sai kawai ta fashe da kuka, rayuwarsu take tunawa kwana hudu zuwa biyar da ya wuce, a da idan tai wanke wanke kowa zubawa ake, amman yanzu daga ita sai Isah da Inna da Baba kawai suke ci, ba kamar da ba. Tunawa da tai da maganganun da mutane suke mata cewar ta yi hakuri ko dan ta karfafawa mahaifiyarta guiwa yasa tai saurin share hawayen. Ta cigaba da wanke wanke bayan ta gama ta dauki kayan ta kai a inda suka saba ajewa ta aje. Sannan ta fara sharar gidan, tana yi tana ta ganin inda aka aje gawarwakin yan'uwanta, ta kasa daina ganin abun a idonta.
Bayan ta gama sharar ta dauko tabarma ta shimfida daga bakin kofar sannan ta shiga ciki ta riko Inna dake kwance.

“Inna muje waje ki sha iska”

Daman zaman dakin ya fara isarta, sai ta yunkura, Aminatu ta taimaka mata ta mike tsaye tana takawa a hankali har suka fito, Aninatu ta zaunar da ita a hankali, sannan ta koma ciki ta dauko filo ta jingina mata a jikin ginin na kasa, ta jinginata. Take Inna ta sauke wata irin sanyayyiyar ajiyar.

“Allah ya miki albarka”

“Amin”

Aminatu ta amsa hawaye na sauko mata ganin yadda rayuwata ta sauya mata ita da mahaifiyarta a lokaci daya. Inna ta sakar mata murmushi sannan ta soke kai kasa. Madafa Aminatu ta nufa ta kunna wuta ta dora tukunya ta zuba ruwa. Sannan ta koma ta auko shimkafar da yayanta Bashiru ya siyo musu ta fara tsinta.

“Ji dan Allah ko tsintar shimfar bata iya ba...”

Ta lumshe ido da sauri tunawa da yayanta Sunasi da tai, yana yawan tsokanarta komai take sai yace bata iya ba. A hankali ta daga kai tana kallon ginin da yai domin yana daf da aure shi da Isah. Duk yadda ta so ta tana kanta hawaye sai ta kasa, hannunta ta saka ta share hawayen tana jin kamar wani nauyi a zuciyarta.

“Ashe haka ake ji idan aka rasa rai”

Ta furta a hankali tana kokarin tsayar da kukanta, sai kuma tai murmushi da yafi kuka ciwo.

“Mutuwa bakin takobi mai raba uwa da daya, ta raba yan'uwa ta raba mata da miji, kin maida mana gida kamar kufai”

Ta damki shimkafar a hannunta wasu hawayen na sauko mata kamar ba gobe, a dole ta aje gyaran shimfara saboda hawaye ya hana ta ga komai.

“Auta...”

Ta juyo da sauri jin kamar muryar Inna ta kirata, sai dai ganin kanta a noce ya tabbarta mata ba kiranta tai ba, muryar dai ce take jin kamar ta Inna. A take ta fashe da kuka ta bar gaban murhun ta mike tsaye wanda hakan yai sanadiyar barewar shimkafar da ke jikinta ta nufo inda ta gudu ta fada jikinta tana kuka. Sai Inna tai saurin lumshe idonta da sauri tana jin kukan Aminatu har cikin ranta, tana son tace mata yi hakuri amman bakinta ya mata nauyin da take jin kamar maganarta ta kare a duniya, sai kawai ta daga hannunta ta dora a jikin Amimatu tana shafata alamar rarrashi.

“Miyasa wani zai ji bakinciki da farinciki mu? A kauye muke zaune amman muna jindadi rayuwarmu, miyasa za su ruguza farincikinmu? Na kasa saba da rashin Yaya Sanusi Inna, Inna yanzu waye zai sake tsokanata? Yaya Amadu mai min fada baya nan, yaya musu mai bamu abinci baya nan, sun kashe Yaya Rilwanu da Yaya Iro...”

Inna ta bude idonta ta saka hannu ta kama fuskar Aminatu.

“Zan tafi na barki Aminatu, yar Autana, ina son ki saba da hakuri, akwai kalubale a gaba, mace da ta tashi a cikin gata da soyayyar uwa da uba da yan'uwa irin ki, duniya ta sauya mata lokaci daya? Dole zata ji ba dadi kuma zata fuskanci kalubale, amman zan fada miki wani abu, ina son ki rike ki rika maimaitawa, a duk lokacin da kika tsinci kanki a damuwa ko kika ga wani abun tashin hankali bakinki ya saba da furta Innalillahi Wa'inna Ilaihirraji'un, ri rike wannan kin ji”

Aminatu ta kalli Mahaifiyarta hawaye na sauko mata.

“Inna idan kika mutu kuma zai ki yi tsammani ni zan rayu? Wannan wace irin magana ce?”

“Zaki rayu Autarta, dan na mutu ba shi yake nufi ki mutu ba, Allah be raya wani dan wani, kuma be kashe wani dan wani, da ya bar yayana dan ni, ko kuma ya bar su dan ke, yadda ya so haka yake”

“Inna maganar da kika fada min yanzu, ta fi min ciwo fiye da rasa rayuwar yan'uwana, kada Allah ya nuna min ranar da zaki tafi ki bar ni, sai dai ni na tafi na barki”

Ta fada cikin kuka sannan ta rumgumeta. Inna ta sake runtse ido tana jin wani kololon bakinciki yana mata yawo a zuciya. Suna haka Baba ya shigo rike da yar ledarsa ta dawo (Fura) ganinsa yasa Aminatu ta tsagaita kukanta ta daga jikin Inna tana fyace hancinta.

“Kukan dai ne be kare ba”

Ya fada yana zaunawa kusa da Inna kana ya aje mata ledar furar.

“Ga fura Auta ta dama miki na san ba iya cin wani abua kike ba”

Kallon furar kawai tai ta dauke ido.

“Baba sannu da zuwa”

Aminatu ta fada da muryarta ta kuka, wai Baba yai mata murmushi irin na su na manya domin shi kansa juriya kawai yake irin ta maza amman ya ji zafin mutuwar yayansa, da kuma keta haddi matarsa. Hannu biyu Aminatu ta saka ta dauki ledar furar ta nufi gurin da suke aje ruwa ta dauko kwanon ruwa ta zuba furar ta fara damawa da nono. Daga Inna har Baba kallonta suke, ta ba su baya amman hakan be hana ta jin abunda suke tattaunawa.

“Ko ya rayuwa zata kasancewa Aminatu idan bana raye?”

Baba ya kalleshi da sauri jikinsa yayi mugun sanyi, Aminatu kuma ta juyo ta kalli Inna hawaye na bin fuskarta.

“Rayuwa zata kasance mai wahala Inna, zan zama marar gata marar yanci, dan farinciki da yai saura a rayuwata zai tafi ya bar ni, iskar da zan shaka ma sai na yi kamar na mutu sannan na same ta, Baba dan Allah ka yi mata magana ta daina irin wannan maganar”

Ta karasa tana duban mahaifinta, Baba ya kasa cewa komai domin jikinsa yayi sanyi sosai idonsa har sun cika da hawaye, Inna ta kalleshi tana murmushi ita ma hawayen ne a idonta.

“Yayanka sun fika jarumta Malam”

“Wannan ba maganar Jarumta bace, magana ce marar dadi, kuma da na san abun da zaki fada kenan da ban shigo gidan nan yanzu ba”

Ya karasa yana kai hannunsa aljihu ya ciro wayarsa dake ringing. Ya kara wayar a kunne tare da sallama sai dansa Bashiru ya amsa ta dayan bangaren...




BATURIYA POV.

Tana tsugune gaban murhu tana suyar naman kajin suka ji an kwankwasa gida. Ta kalli danta shi ma ya kalleta.

“Ko Abba ne?”

A take ta daka masa tsawa.

“Ban ce ka daina cewa Abbah ba?”

Sultan yayi saurin rufe bakinsa.

“Daddy”

“Good”

Ta mike tsaye tana mita.

“Wata kila ma yaran nan su Saifu sarakan kwadayi tun da sun ji an soyar abu kamshi ya kawo musu, shiyasa zama irin wannan area ta talakawa sai dole Wallahi”

Ta kai hannu ta bude kofar sai arba tai da kawarta Ramlee, a take ta washe baki, Ramlee ta sakar mata murmushi tana wani irin kamshin turare irin na manyan masu kudi.

“Yau gidanmu?”

“Sai kace ban saba zuwa gidanmu ba”

Ta fada a yayinda Baturiya ta kauce mata ta shigo.

“Ki ce yau na shigo a sa'a kaji ma kuke ci, lallai Faruq yayi abun kai”

Ta fada ta zigar zolaya da bugun ciki tana kallon Baturiya. A take Baturiya da bata shaye rada ta tsire baki tace.

“Kina magana kamar baki san wa nake aure ba, Faruq din ne zai kawo min kaji?”

“Ah gaskiya idan fa yana da shi yana yi”

“Idan yana da shi kika ce, ke dai zauna na kawo miki ruwa”

Baturiya ta mika mata kujerar da take zaune dazun, ita kuma ta karba ta zauna tana karewa gidan kallo kamar bakonta, ko gaisuwar da Sultan yake mata bata ji.

“Baturiya kenan duk kyau nan naki kika kare a gidan nan”

Baturiya ta aje mata ruwan a cup tana fadin.

“To ya iya, kaddara rayuwa ta kawo ni nan”

“Kika dai kawo kanki, ke kika so ai”

“Hmmm Wallahi Ramlee babu irin cin mutunci da ban masa ba, amman yaki ya sake ni”

“Ina ko zai sake ki, tun da be da kudin auro wata, kuma ya san yadda kike da kyau nan kina cika idda wani mai kudi zai aureki”

“Da gudu ma, ni Wallahi ban taba zaton zan yi rayuwa a haka ba, bawan Allah nace masa idan mun yi aure zan cigaba da karatu yace ya yarda zai dauki nauyin komai, sai gashi abincin ma wannan wahala yake mana”

“To miya hana shi?”

“Ai lokacin da na aureshi karatu yake, ni na dauka, yana gama karatu zai samu aiki mu fancama yadda muke so, ashe ashe wahala ce ke kirana, gashi gurin auren ma sauki aka masa tun da auren gida ne, kawaye da muka gama secondary school a tare daga mai aure wani shege sai mai aiki a guri kaza ni ina nan zaune a wani shegen gidan duk yabi ya rugube, kuma na haya”

Tana kai aya Ramlee ta saka mata dariya.

“Ke kika so Baturiya, tsabar kyau fa Baturiya ake ce miki, gashi manyan mutane suna son farar mace, Wallahi ba ki ga yadda mutumen ya haukace daga ganin hotonki ba”

Baturiya ta nufi namanta ta juya tana fadin.

“Ke ni fa Ramlee duk iskancina ba zan iya zina ba”

“Su kuma manyan mutane ai sun fi son matan aure saboda sun fi Sirri, wasu kuma ba sai kin fada musu cewar kina da aure ba, ki ga abun da be wuce 30-1hour ba an baki kusan 500k ko 300k”

Baturiya ta juyo tana kallonta tana zaro ido.

“Da gaske wai?”

“Wallahi kuwa, ke auren ma ba rufi asiri ba ne a gareki, wanda ta haihu har wani tsoron fadawa maza take ma, kara ma budurwa ace ko dan gaba, amman ke fa? Kuma ko kudi aka ganki da shi za a ce na mijinki ne”

“Tab humm ai sun san bakiri nake aure, shi kansa idan ya gan ni da wannan kudi sai ya tambaya ina a samo”

“Ki ce tallafi ne kika samu, daga nan sai ki kirkiri sana'a ki fara yi, kin ga idan ma wasu sun shigo ba za a zarge ki ba, Wallahi cikin Shekara daya Fee'ah har makka sai kin je, kuma duk abun da kike so zaki siya a duniyar nan”

Baturiya ta dawo kusa da ita ta zauna.

“Amman su wani irin kudin banza ne da su haka?”

“Masu kudi fa aka ce miki Baturiya, kina irin wannan area ko'ina kwata ai dole ki yi mamaki, da zaki yarda zan hada ki manya manyan yan kasuwa da yan siyasa, kuma ba haka nan ake zuwa musu ba ai, sai an gyara ki an shirya, ta yadda zai ji kamar be taba kusantar wata mace ba”

“To shi zunubin zaki daukar min?”

Baturiya tai mata tambayar rainin wayo. Sai Ramlee tai murmushi tana mikewa tsaye.

“Baki ji matsi ba ne yarinya, kin san da Allah kika chat da maza a facebook? Har kina haduwa da su kina karbar kudinsu”

“Wannan ai dabam, ban aikata ba sai dai na yi musu dadin baki”

“To yayi kyau ki cigaba”

Ta saka hannunta a jaka ta ciro 10k ta mikawa Sulta.

“Sultan a siye minti ka ji, ni bari a dauki naman tun da ba za a min ta yi ba”

Ta karasa gurin naman ta saka hannu ta dauka ta kai bakinta, Baturiya ta yi murmushi.

“To ai ke dince kika dauke min hankali ”

Bata sake ce mata komai ba ta nufi kofa, Baturiya sai kallo tsadadden lace dinta take, sai da ta fita sannan ta juyo.

“Ni baki ma fada min ina kika samu nama ba, ko wani aka yaudara”

“Wannan karon roka na yi”

“Uhm wata rana dai zasu roki abun da baki so”

“Ai da zarar na ga mutum da ruwan haka, sai na zubar da shi na kama wani”

Ramlee ta yi dariya ta juya ta kama Hanya Baturiya kuma ta rufe gidan ta nufo gurin yaronta Sultan ta karbe kudin da Ramlee ta bashi.

“Karka fadawa Daddy ka ji?”

“Toh”

Ya amsa ta yana kai hannu ya dauki cinyar kaza. Sai bayansa sallah isha'i Faruq ya shigo gidan, ba laifi ya samu masu haske har ya hada 500, tun da ya ji kofar gidan a bude ya tabbatar matarsa na cikin nishadi, domin idan tana jin rashin mutunci wani lokacin rufe gida take saboda yai ta wahalar kwankwasa a waje.
Bayan ya shigo ya maida kofar gidan ya rufe, kamin ya karasa falon ya so ma jin waka ya tashi, ko kwankwato babu matarsa na cikin nishadi a yau. Sallama yai ya shiga ta amsa masa kamar ba ita ba.

“Sannu da zuwa”

Ya dan tsaya kallonta kamin ya amsa.

“Yauwa, ya gidan”

“Alhamdulillah”

Ya zauna saman kujera yana kallonta.

“Mun samu wani abu ne kike ta nishadi haka?”

‘Tun da a sanadinka aka samu ai za a sammaka’

Ta fada a ranta a fili kuma sai ta mike tsaye tana fadin.

“Uhm wasu yan kudi ne na samu shi ne na siyo kaji na soya mana”

Daki ta shiga ta debo masa a platecikin wanda ta soya ta kawo masa ta aje a gabansa.

“Ina kika samu kudi?”

Ya tambaya yana kallon naman da zai rabin kaza.

“Allah ya ba ni”

Ta amsa masa bayan ta zauna.

“Haka kawai Allah zai baki kudi daga sama ba ta dalilin wani ba?”

“Allah ne ya ba ni”

“Ki dauke namanki, ki kawo min abinci, ba zan ci abun da ban san inda aka samo shi ba”

“Matsalar talaka kenan ai, ga talauci ga girman kai, yaushe rabon da mu ci nama a gidan nan?”

“Ba mu kadai ne a cikin wannan halin

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login