Showing 63001 words to 66000 words out of 133328 words

Chapter 22 - BAKAR WASIKA complete

Start ads

24 Aug 2025

480

Middle Ads

yana gurin Ali a asibitin ya kan cewa Daddy yana asibiti, hakan yasa Daddy yai zaton ko yana tare da Ali ne?

“An bata maka rai ne? Could we talk?”

“No Daddy ina wata magana ne mai muhimmanci, bata shafe ka tsakanina ne da Ali”

“Okay”

Daddy ya fada sannan ya kashe wayar, Talba ya cikawa bakinsa iska ya busar a hankali yana kallon Nurse din data doso inda yake.

“Dan Allah kai ne mijin yarinyar nan? Ko dan'uwanta?”

Tsaye Talba yai kamar an dasa shi ya kasa amsa mata.

“Tana bukatar jini da gaggauwa”

“A ina zamu samu?”

“Lab amman for now za mu bincika mu ga ko za'a samu jinin da zai dace da nata”

Ya gyada mata kai a hankali cike da natsuwa, sannan ya bi bayanta suka nufi cikin ward din, ita ta nuna masa dakin da suka saka Aminatu. Ita ta fara shiga shi kuma ya bi bayanta ya tsaya jikin kofar yana kallon fuskar Aminatu dake ta bachi kana gani kasan bata san inda take ba. Nurse din ta yi abun da zata yi ta fita Talba yana tsaye jikin kofar idonta akan Aminatu, takawa yai a hankali ya karasa kusa da gadonta still ya kasa kauda idonsa akanta.

“You need to survive”

Ya furta yana jin kamar ya tashe ta ya tambaye ta waya mata haka, kuma ayi sa'a ta amsa masa cewar Leila ce. Yana tsaye akanta har na kusan mintuna talati, sai ga nurse din ta dawo tare da likitan daya karbi Aminatu a dazun.
Sake dubawa yai sannan ya kalli Talba.

“Ba mu da kalar jininta a yanzu, sai kaje babbar asibiti ko kuma ka samu wani daga familynta idan zai iya bada jinin”

Uffan Talba be ce ba har sai da Likitan ya nufi kofar fita.

“Ko zaka iya gwada nawa? O ne”

Likitan ya juyo ya kalleshi.

“Yes why not amman zamu fara maka test mu tabbatar baka dauke da kowace irin cuta gudun samun matsala”

Ya daga masa kai kamar an masa dole, sannan ya bi bayan Nurse din dake nuna masa kofa.

“Bismillah Malam”



LEILA POV.

Wani irin kuka take wanda ita kanta ba zata iya fadar dalinlinta na yin kukan a yanzu ba, na zargin da Talba yake mata ne ko kuma na laifin ne da yake kokarin dora mata? Taya zai zarge da da abun da bata san wanzuwarsa ba? Miyasa ma zai yi maganar wata yarinyar a gabanta? Ko kuma dai tana kukan ne saboda zuwan Shamsu? For now she can't tell, all what she know is dukansu is painful, daga zargin har zuwan Shamsu har zancen yarinyar da Talba yake.

“Tun dazun kike ta kukan nan? Haka zaki yi ta yi a gaban mutane ki daure kanki?”

Momy ta fada cike da tausayin yarta.

“Wai wace yarinya ce ma yake magana akai?”

A take ta amsawa Momy hawaye ma sauko matan

“Wata ce, wata yar gudun hijira ce”

“Yar gudun hijira kuma? Shine har zai zarge ki da kashe ta? Ke kin santa ne?”

Ta daga kai tana goge hancinta.

“Na santa amman Wallahi ban ma taba ganinta balle har na yai yunkurin kasheta? Miyasa zai zarge ni?”

“Ke kika bashi fuska ai! Kina ta son bada kofar da za a zarge ki, koma dai miye ai be kamata yai wannan tunanin ba, and ko da kin aikata be kamata ya sameki kai tsaye da maganar ba!”

Momy ta fada a fusace, sannan ta mike tsaye yana wani kashe ido.

“Karki fito cin abinci, saboda Daddynku zai tambaye dalilin danuwarki, so ki zauna a nan zan fada masa kanki yana ciwo”

Leila ta daga kai, sai Momy ta juya ta fice daga dakin tana mamakin yadda Talba yake son sauyawa.
after like 40 minutes da fitar Momy wayar Leila tai ringing, hannu ta kai ta dauka tana duba number Ali dake kiranta, da kamar ba zata daga ba sai kuma ta daga wayar ta kara a kunnenta tai shiru tana sauraren abun da zai fito daga bakinsa.

“Kuka kike yi ko?”

Ta daga masa kai kamar yana gabanta, wasu hawayen na sauko mata. Be damu da yaji abun da zata fada ya sauke ajiyar zuciya daga can cikin wayar.

“I know na san abun da ya faru, can we talk? Gani a hanyar gidanku akwai maganar da nake son fada miki, please ki daure ki fito zan tsaya a gate”

“Okay”

Ta amsa masa tana jin wani sabon kuka na taso mata, sannan ta aje wayar ya lumshe ido, fuskar Baaba ce ta fara mata gizo, hakan yasa tai saurin bude idon ta mike tsaye ta nufi gurin windows din dakinta dafe kai wasu hawaye na sauko mata.
17

*Khadeeja Candy*

Ko kin san kamshi na daga cikin abun da yake daga darajarki? Kamshi yana saka a ga kimar mutum a girmamashi musamman ma na Ramla incense, tana da turaruka kala ka kama daga na jiki dana daki da na tufafi, irin su Halud
Sandal flakes
Sandal wood
Signature
Kajiji
Damboun kajiji
Halud ball
Wardrobe ball
Coconut sandal
exclusive gowe
Black humra
Body milk
Kulaccam
Misik humra. Ramla Incense ta shirya tsab domin aika muku da turarenku har garin sa kuke, da kudinki kalila ki samu turare mai kyau mai dadin kamshi da sanyaya zuciya domin siye ko sari ku tuntu Ramla incense ta wannan number +234 703 839 2576 tana aikawa har wajen Nigeria. You can check her Instagram handle ramla_incense. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1fl5k3wnc4opb&utm_content=43xtopa

*Dan girman Zatin Allah karki karanta idan baki biya ba. Masu sharing Allah yai muku yadda kuke min! Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*

Madina ta jimmm bayan da Leila ta gama labarta mata abun da ya faru, gaba daya sai ta ji jikinta ya mutu.

“Yanzu dai ki fita ki ji abun da Ali zai fada miki”

“Zan je yanzu”

“Ki kwantar da hankalinki komai zai wuce, amman da zaki dauki shawarata da kin fadawa Talba gaskiyar komai, barin kashi a ciki baya maganin yunwa Leila, kuma yanzu zaki yi ta samun rashim fahimta a tsakaninku ne”

“Madina wannan sirina ne, Momy ma bata san na fada miki ba, amman na fada miki ne saboda na yarda da ke”

“Babu wanda zai taba jin wannan maganar daga gareni Leila, amman ina baki shawara ne akan abun da nake ganin zai zame miki masalaha”

“Yanzu dai bari na tafi Ali yana jirana”

“Okay”

Leila ta aje wayar sannan ta sauka saman gadon ta dauki wani karamin mayafi ta rufe kanta, sannan ta saka talkaminta ta nufi kofar fita idonta a kumbure saboda kukan da ta sha.
Ko da ta sauko falon babu kowa, dukansu suna bangaren Daddy, yan aikin Momy kuma Momy bata basu damar zama a falonta hakan yasa idan ba wani aikin zasu ba abu ne mai wahala ka gansu a main house din kullum suna BQ. A hankali ya bude kofar falon ta fita gabanta na faduwa, domin ji take kamar zata yi arba da Talba ne, domin a yanzu bata son ganin fuskarsa, ba dan bacin rai ba sai dan bata da amsar tambayar da zai mata. Tun kamin ta karasa gurin gate din police din ta bude mata karamar kofar ta fice, tana fitowa ta ga motar Ali fake sai ta nufi inda motar take. Ali na zaune cikin motar yana kallonta har ta karaso gaba daya sai ya ji tausayinta ya kama shi, a da can yana bata laifi kamar yadda yake bawa abokinsa sai dai a yanzu ya fahimci abokinsa ne mai matsala ba ita ba. Bude motar tai ta shiga sannan ta rufe ta kalleshi da idonta da suka kumbura.

“Ali”

Sai da ya sauke wani dogon numfashi sannan ya amsa mata.

“Na'am Leila, ya kike?”

Tambayar ya take da yai sai ta ji kamar ya tsokano mata kukanta, a take hawaye ya cika idonta.

“Ba Kalau ba Ali, ba Kalau ba”

“Na sani, abokina yayi rashin tunani, amman ban dauka zai miki magana ba, a thought ya bar abun a ransa ne kawai, sai dai faga lokacin dana kira ki na ji yanayinki, sai tausayinki ya kama ni, and now na fahimci irin halin da kike ciki”

Ya karasa yana kai hannu ya ciro tissue ya mika mata, sai ta karba ta share hawayenta.

“Sometimes ina kasa fahimtar waye Talba, abokinka yana da wahalar sha'ani Ali, taya wanda zaka aura zai zarge ka da kisa? How? And Why? Saboda na nuna kishina? Talba be dadin zama wani lokacin”

“Na sani, amman ban dauka abun zai kaishi haka ba”

Cewar Ali yana kallonta gaba daya zuciyarsa ta cika da tausayinta, domin gani yake Talba baya sonta ita ce kawai sonsa ke dawainiya da ita.

“And i respect your decision na cewar ba zaki auri Talba ba har sai ya canja”

Juyowa tai ta kalleshi da kyau.

“Dan Allah zaka fada min abun da ta faru da yarinyar?”

A takaice ya labarta mata komai na yadda aka samu yarinyar, sai dai be fada mata cewar Talba ya dauke ta daga asibitin ba, haka ma be fada mata cewar sun samu tsabani ba, domin yana ganin kamar sirrinsa ne da be kamata kowa ya ji ba.

“Amman me zai saka wani yai mata haka?”

“Ni ma ban sani ba, kuma a iya binciken da na yi wani be shigo ba, so dole dai sai ta farka zata iya fada mana yadda komai ya faru”

“Yanzu tana asibitinku?”

“No na canja mata asibiti, and i am here to apologize saboda ni na janyo komai, Talba be san yarinyar nan ba, ni na hada shi da ita da neman ya taimaka mata saboda yarinyar tana bukatar taimako, amman ban yi tunanin abun zai zama na rigima haka ba”

“Baka da laifi, na san ka yi ne da kyakkyawar niya, be kamata ka bada hakuri ba”

Yayi shiru na wani lokacin kamin ya kalleta ya ce.

“Amman Leila kin yi wani abun ne da zai saka Talba ya zargeki da taba yarinyar nan?”

“Ban yi komai ba, amman kasan a gurin abokinka kullum nice mai laifi, kawai dai na fahimci wani abu... Talba baya so na ni ce kawai na mutu da kaunarsa, wanda yake sonka ba zai maka haka ba, ko da gaske na aikata zai nemi hanyar kare ni ne, ba ya tunkare da wannan laifi mai girma ba, abun akwai ciwo”

Ta karasa wasu hawaye masu zafi na sauko mata, har cikin ranta tana fadawa Ali abunda ta fahimta ne akan zamantakewarta da Talba. Ali ya kawar dai yana jin irin tausayinta na kara kamashi.

“Ada can na dauka miskilancinsa ne ya saka yake min abun da yake min, amman a yanzu na fahimci kauna ta ce babu abunsa, kawai ya amince ne saboda ba zai iya cewa Daddy a a ba”

Ta runtse tana kokarin fashewa da kuka.

“Kabir yana da fada min gaskiya amman na kasa ganewa, saboda kaunar Talba ta cika min zuciya amman yanzu na fahimta...”

Ali yayi saurin daukar ruwan dake cikin motarsa ya mika mata.

“Please sha ruwa”

Sai kuma ya dauko tissue ya mika mata.

“Ki daina damuwa dan Allah, kukan nan yayi yawa idonki har ya kumbura, me yasa zaki damar kanki akan Namiji?”

Sai ta kalleshi hawaye na sauko mata

“Talba be taba min haka ba, na gode”

Ta fada sannan ta karba ya share hawayenta ta bude ruwan ta sha.

“Ki je ki huta, karki saka damuwar komai a ranki komai zai wuce, kin san idan ya fusata yana aikata abubuwa amman zai sauko and ina tabbatar miki zai baki hakuri”

Ta dan yi murmushi irin na bakinciki da kuma kin yarda da maganar Ali cewar zai bata hakuri domin ta san waye Talba, sai dai bata ce masa komai ta bude motar ta fita, Ali ya bita da kallo cike da tausayi har ta shige cikin gidan, sannan ya kai hannu ya dauki wayarsa dake carji a jikin motar ya kira Talba, wayar tai ta ringing har ta gaji ta katse be daga ba ya sake kiransa nan ma shiru, haka ya jera masa kusan 4 miss calls a na biyar ya ji wayar a kashe alamar ya gaji da kiran da yake masa kenan kuma ba zai yi picking ba.

“Talba....”

Ali ya fada yana jin kamar ace yana kusa da shi yai masa dan banzan duka a yau saboda kukan da Leila ta sha akasa.

‘Ina ka kai yarinyar nan?’

Shine sakon daya tura masa sannan yai reverse ya kama hanyar gidansa.


TALBA POV.

Be dawo gidan ba sai dare, domin bayan an gama diban jininsa sai ya fito asibitin ya koma gidan marayun, daman can yakan je idan yana cikin bacin rai ko damuwa ya wuni a can, sai ya ji damuwar tasa ta ragu saboda yara suna rage masa kewa, and ko ba komai zai ji cewar ba shi ne kadai a damuwa ba, su ma sun rasa iyaye da yan'uwa amman sun zaune a inda Allah ya tsara musu rayuwarsu kuma suna farinciki, balle kuma shi da Allah yai ma ni'imar aje su da ciyarda su, bayan tarin lafiya da ni'imar yan'uwa da kuma ta uba kamar Daddy da Allah yai masa.
A can yai sallah magaba a can yai isha'i, be dawo gida ba sai ba tara saura, wunin yau bayan abincin safe be sake saka komai a cikinsa ba sai ruwa. Yana shigowa ya faka motarsa kusa da entrance din Momy sannan ya fito ya nufi kofar falon cikin yanayin da ba zai iya fada ba, kawai misaltawa yake idan har da gaske Momy da Leila suna da hannu a mutuwar Baaba ko batanta ya iyalanta za su ji? Yayanta da jikokinta? And ya ma akai komai ya faru? Idan ma kasheta sukai ina suka kai gawarta. Sau biyu yana danna door bell din sannan Amal ta bude masa kofar.

“Ya Talba welcome”

Ya amsa mata ta kai fuska ba yabo ba fallasa, sannan ya shigo cikin falon, hakan ta nuna alamar baya cikin walwala. karasa yai kusa da Kabir dake zaune a sofa yana cin tuwon samun miyar gayye ya zauna. Kallo daya yai ma tuwon ya dauke kai domin shi ba ma'aboci cin tuwo ba ne, wayarsa dake aljihu ya ciro ya kunna sai ga sakon Ali ya shigo wayarsa.

‘Ubanta ne kai?’

Shine reply din da yai ma Ali sannan ya aje wayar ya busar da iskar bakinsa.  Kabir ya kalleshi sannan ya kalli Amal dake zaune tana kallonsu dama haka take idan ta lura da ba a zaune kalau, so that ta samu abun tseguntawa Daddy.

“Amal je ki yi bachi mana”

Kabir ya fada, sai ta make kafada.

“Bana jin bachi yanzu”

A take ya zare mata ido, hakan ke nuna ba da wasa yake ba, ya saba wasa da ita sosai sai dai a duk lokacin da yake serious magana da ita ta san yanayinsa. Mikewa tai tsaye tana kallon Talba.

“Ya sai da safe”

Ta murgudawa Kabir baki sai ya kyalkyale da dariya yai mata gwalo.

“Daddy's noy could we talk?”

Talba ya kalleshi.

“Leila ta fada maka ne?”

“Nooo Amal dai ta shinshino ta shinshina min”

Talba ya dan yi murmushi kadan yana kallon hannunsa.

“Na bada jinina yau”

Kabir ya duba shi duba na mamaki, ba zai ce ya san dukan abun da Talba yake yi ba, amman be taba jin yace zai bada jininsa ga kowa ba.

“Something new...”

Talba yayi murmushi.

“Yeah.... I feel like..... ”

Sai kuma yai shiru kamar mai tunanin abun da zai fada.

“I feel honour.. I mean it was a great joy.... to do....something like this”

A rarrabe yai maganar and he is very excited, he can't tell why amman yana jin yayi abu mai kyau.

“Yeah at least wani zai rayu da jininka, and mutumen nan ba zai taba manta ka idan ya sanka, idan kuma be sanka ba, kai zaka ji cewar wani yana can yana rayuwasa saboda ka taimaka masa da jininsa ko da kuwa siyarwa kai balle kuma ace kyauta ka bada, more especially ace mutumen nan yana cikin yanayi na bukatar jini tsakanin rayuwa da mutuwa...”

Talba yayi shiru yana sauraren kalaman Kabir, sai kuma ya soma tuna abun da ya faru a yau. Juyowa yai ya kalli Kabir.

“Idan mutum ya suma zai dauke ki awa nawa kamin ya dawo hayyacinsa?”

“Is depend on yanayin suman, ko kuma irin kulawar daya samu, but most wadanda tsoro yake saka su suma ko damuwa, ba su cika farkawa da wuri ba kamar wanda rashin lafiya ta saka shi suma, kuma ya danganta da kalar suman da mutum yai”

Shiru Talba yai alamar nazari sannan ya sake tambayar Kabir.

“Amman me ke saka mutum baya kuka da murya sai hawaye, kuma ba ya magana, baya cin abinci baya ma bude bakin”

Kabir ya aje spoon din da yake cin abinci da shi ya dauki ruwa ya sha.

“Depression... Damuwa tana saka wannan har fiye ma, tana saka hauka, rashin lafiya and so on, indai har ba wai mutum ya daman can haka aka haife shi ba, daga baya ne ya sauya gaskiya damuwa ce, tana tsoro tana saka mutum ya rika ganin abu yana imagination ko kuma zuciyarsa ta raya masa ya aikata ko ta saka shi hauka ko ya rika abu kamar mai aljannu, tana saka yawan mantuwa ko surutu ba akan abun da ake magana akai ba, you know komai n jikin dan'adam yana da limit din abun da yake iya dauka, so idan abun yai yawa ko yai kadan zaka tarar akwai irin illar da yake haifarwa”

Silently Talba ya sauke ajiyar zuciya.

“Idan mutum yana son yayi magana da mai irin wannan abu kamar ya tambaye shi wani abu ya zai yi?”

“Ya zai yi kuwa? Most important thing is ka yi kokarin cire wannan mutumen a damuwa, idan wani abu yake so ka sama masa, idan tsoron wani abu yake ka nuna masa babu abun da zai same shi kuma zaka bashi kula, ka sake jikim da shi kana bashi kulawa kana nuna masa far'a da walwala kana dauke masa hankali daga damuwar, kai ta kokarin ganin ka faranta masa rai, da haka da haka zaka ga ta saki jiki da kai, ka yi ta cusa kanka kana bata abinci tun bata ci har ta fara ci”

“Idan kuma ya ki fa?”

“Taki dai... Zata ma ci idan ta ji yunwa, idan ana saka mata maganine a ruwa na abinci ko kuma ana bata ta hanci a daina, as long as zata iya tashi zaune

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login