Showing 78001 words to 81000 words out of 108894 words
din kafin aka sallamesu kafin result na test din su fito.
Bayan dawowarsu gida tayi waya da Laylah wadda ba'a fadawa abunda yafaruba sbd karta damu,
Itakuma Sa'adah abin dayasa ta nace akan Kar afadawa Laylan sbd yanayinta da lafiyarta..
Ms Na'ima ko data iso Nigeria anriga an sallami Sa'adah daga asibiti Dan Haka tana isowa Bata shigo gurin Anne ba sai data kwana ta wuni tagama danne kanta da zuciyarta sbd karta Bari Annen tagane tasan da komai sbd tunda Sa'adah ta dawo gida bazata iya komai akantaba Kai tsaye Saida wata dabarar.
****Tafiyar mum da kwana uku Abban yadawo daga tasa tafiyar murna gurin Laylan Bata boyu ba musamman dayake mum Na'ima da siddika tadawo Nigeria tunda itace Mai aikinta Koda yaushe Dan Haka Yana dawowa da kanta ta fito da gudu tayi kansa
Ba Bata lokaci ya dauketa Kan jikinsa Yana kallon haske da cikar data qara Bai sauketa koinaba sai palonsa na sama Yana kallon fuskarta datasha simple makeup sai qamshi takeyi,
Ga wata qaramar chiffon free half gown a jikinta data qara Mata kyau kaman yarinya Yar Sha uku.
##MAMUH#
[6/27, 10:56 AM] MG💋: *_Mamuhgee 42_*
Yasan Ms Na'ima Bata Nan ta tafi Nigeria sbd ta sanar Masa da suna waya akan zata tafin, Bai Saba hanata fita ko tafiyaba shiyasa baice komaiba Bayan Allah yakai lafiya Dan fitarta Bata fada Masa dama tafiyarce dai wasu lokutan take sanar Masa bayan tagama tsara abarta.
Hutawa yayi sosai bayan dawowarsa wannan tafiyar sbd sakewar dasuka samu dagasu saisu sai Cindy wadda take tamkar secretary din Laylah Dan yanzu maganinta ma Sofia ta damqa Mata ita ke Bata anan gida tana Sha Amma a dakinta yake boye sbd gudun tsautsayi.
Samun wannan sabuwar damar dasukai yasa suqa qarasa lalacewa juna Dan kuwa yanzu tamkar wasu chewing gum suke musamman da cikinta yaqe qara Masa Jin nutsuwa da ita duk da baisan tana daukeda cikinba,
Itama cikin yasa taqarasa lalace masa,
Babu inda basa shaaninsu musamman dayake ba sauran wata kunya a tsakaninsu bayan kamewarsa Dake motsawa wani lokacin musamman idan Yana tuno Amininsa sai yanajin wani iri duk ranarda shaidar abinda ke faruwa tsakaninsu ta fita wato ciki idan tasamu.
*****Babbar ranar farin cikinta tasameta ne lokacinda Abban ya sanar Mata an sallami abbanta sbd saukin daya samu Yana iya magana yanzu harma da motsa jikinsa yayi komai
Tafiya ce kawai bayayi yanzu Yana Kan kujera sai antura Amman tafiyarma zaiyi ahankali wata Inshallah.
Rumgumesa tayi tana kukan farin cikin samun lafiyar abbanta,
Jin takeyi inama zata zauna guri daya da abbanta,
L.A Suka tafi inda mum tuni ta wuce samun labarin tsautsayin Sa'adah Dan Haka ba kowa agurinsa Saida suka Isa,
Harhada komai sukai Suka Gama duk wasu formalities na sallamar Suka tarkata suka kaisa wani lafiyayyan hotel da Turaki yasa A Abdoul yayi Masa booking.
Acan suka barta ta wuni da abbanta suna magana akan yanda zamanta yake da Ms Na'ima cewan batasan ita Matar Turakin bace.
Abba Bai wani ja zancen da tsayiba sbd yanda zancen ke sanyata kasa hada ido dashi,
Hakama shima zancen baya Jin sakewa acikinsa tunda 'yarsa ake magana da Amininsa dayasan haryanxu baigama karban aurenba,
Ya riqeta ne saboda inganta rayuwarta harma data 'yar uwarta,har abada bazai daina gode Masa akan hakanba,
A taqaicema ya karba auren ne sbd halinda shi yake ciki yanzu kuma tabbas bazai takura Aminin nasaba zai basa tabbacin zai iya sauwakewa Laylan aurensa tunda ba Kamar taimakone yayiwa Wanda yake halin ciwo da rashin gata,
Yanzu Kuma alhamdllh yasamu lafiya, Kuma Laylan tasamu ilimi Mai zurfi ko ahaka zasu iya tallafar rayuwarsu.
Da wannan tunanin Abban ya yankewa kansa shawaran idan ya natsa bayan komawarsa guda zai bawa Turaki damar ya sallami Laylan tunda dama Babu Wanda yasan da aurenta dashi Kuma yasan bazai taba karbanta amatsayin matarsaba sbd shi da Zainab Dan 'yarsu tamkar 'yarsa daya haifane.
Sai dare A Abdoul yazo ya dauketa suka koma gida sbd Turakin Bai dawo gurin abbanba barinta yayi ta sake da mahaifinta suyi magana yanda yakamata sbd a kusancinsa da ita yagama fahimtar irin girman kauna dake tsakaninta da Abbanta Wanda duk ya kalli hakan ranarda ya biyawa Mahmoud sadakin zainab take Fado Masa Rai irin yanda suke tsananin son junansu baitaba saka ran ya biya sadakin da za'a hadu a Haifa Masa Mata bane...
Bayan sun kwanta tana cikin jikinsa kwance da wata qaramar fingilalliyar rigar bacci data Gama barkewa ta Samanta sbd irin yamutsar dasuka Gama Amma dayake tanason bacci da rigar sbd rashin nauyinta yasa ta maidata ahakan sbd saman ne ya Gama fincike hannuwan rigar dasuke sirara.
Cikin sigar roko da Yar yarinta ta bude Baki ahankali tace"
Abba, zanbi Abbana Nima Dan Allah naje Nigeria..
Ahankali ya lumshe fararen idanuwansa masu Dan girma ya budesu akan bakinta da yayi maganar kafin ya bude Baki ahankali cikin nutsuwa yace"
No.
Marairaice murya tayi tareda sake shigewa jikinsa tana zagaya hannuwanta zuwa bayansa tasake Dan rugumarsa Suka manne fiyeda yanda suke tace"
Please Abbahhh.
Nayi kewan gida,dasu Anne,
Inason bin Abbana gida Dan Allah.
Zakije Amma ba yanzu ba saikin Gama exams dinki tukuna na wannan session din,
Karki manta kina last year dinki.
Sanyi jikinta yayi tace"
To waye zai kaisa gidan tunda momy ta tafi?
Tare zamu tafi Inshallah gobe Zaki koma Atlanta daga Nan zamu wuce ki zauna gida kiyi karatun exams.
Sanyi jikinta yakuma yi ta kallesa tana Jin kewarsu duk su dukan shida abbanta tun Basu wuce ba ahankali da sanyin murya tace"
I will miss everyday Abbah....
Please kadawo da wuri tunda mum tace ba yanzu zata dawoba zanyi kadaici da yawa bakanan mum batanan ga abbana ma ya tafi.
Kissing lips dinta yayi ahankali tareda gyada Mata Kai batareda ya bude Baki yayi maganaba Dan kewarta zaiyi Kamar sabuwar haihuwa yasani shima saidai ba Daman nunawa shiyasa yake wahala yanzu duk yayi tafiya sbd rashinta Yana azabtar da zuciya,Ruhi da gangar jikinsa.
Da Dan zazzabi ta kwana sbd kadaici data fara tun lokacin da Yar damuwar zuwa gidan dataso Yi,
Har asuba jikinta akwai zafin zazzabi irin Wanda yake Dan damunka Ahankali ahankali,
Da safe guraren 10 Da kansa ya shiryata cikin kayan sanyi da qatuwar jacket Suka Fito yakaita tayi bankwana da abbanta Amma Bai shigaba a mota ya tsaya sbd idan yashiga bazai iya fitowa kaita airport da kansa ba saidai A Abdoul yakaita Dan Haka Bai shigaba Ita kadai tashiga tareda A Abdoul Suka Gama suka fito.
Tunda suka Kama hanyar airport take kwance jikinsa Yana kissing hannunta akai akai har Suka Isa airport din A Abdoul yafita motar yabarsu.
Fuskarta ya Kama yayi kissing bakinta ahankali tareda shafa fuskarta ahankali da muryarsa Mai dadi da aji ciki yace"
Ki kula sosai okay??
Gyada Kai tayi tareda Dan shigewa jikinsa ta rumgumesa yanajin zafin jikinta ahankali.
Dagota yayi ya Kama hannunta Suka fito motar Yana riqe da hannunta A Abdoul na bin bayansu da qaramar suitcase dinta.
Yanayin yanda taketa neman rikice Masa ta sanyashi sauya ra'ayi akan rashin barinta zuwa yasa Basu jira lokacin tashin jirginsu ba suka tafi Suka barta.
Yamma sosai ta iso gida bayan sofia taje har airport ta daukota da motar gidansu sbd zazzabinta qarfi yayi kafin su iso Dan Haka suna isowa gida daqyar da Taimakon sofia tayi sallah Cindy ta kawo tea Mai dumi da cupcakescake taci guda biyu Tasha magani ta kwanta a wahalce.
***Anne ce zaune tareda baqi suna magana saiga isowar baqi halima tazo ta isar Mata dama tagama da baqin zasu tafi ne Dan Haka Kai tsaye aka shigo dasu Momy...
Momy CE tareda Haj Karima Dake zaune a Abujan suka zo gidan,
Tunda momy tadawo tana gidan Haj Karima anan Abuja sbd Sa'adah tana zuwa dubata akai akai,
Bata taba zuwa tareda Haj Karima ba sbd gudun sugano gaskiyar ayi tashin hankali batareda sa'adahnta tagama karatunta tafara aiki Mai kyau ba su Bata Mata gobenta Dan kuwa saninta ne bazasu taba barwa Allah ba Koda Sa'adah bazata aura Turaki ba sunfi son ayi biyu Babu Dan kuwa dukkaninsu qiyayyar mahaifiyar Laylah da Laylah a jininsu take mai qarfin gaske.
Qarasowa sukai Anne na musu barka da zuwa cikin mutuntawa da sakewar fuska.
Mintuna qalilan aka zagayesu da kayan tarban baqi,
Drinks ne masu sanyi da sabon madarar nono Mai sanyi sai dambun Naman kazar sai snacks.
Haj Karima duk gaisawa da firar da Anne ke Dan Jansu hankalinta nakan tsabar dukiya Dake magana koina a gidan,
Ta duba tasake dubawa Babu wani Abu a gidan da bana manya bane Dan Haka ita saima taji hankalinta yakuma tashi akan ayita Mai yiyuwa bazai yiyuba Sa'adah na aure gidan arziki irin wanna ace Basu more Mataba bayan dawainiyar dasukai da uwarta da ubanta ya lalace akwance da sunan ciwo,
Tunda gida zasu dunguma su tafi ba har Sa'adah da momyn tunda Mahmoud din zai dawo ai zasuje can ayi magana
Wlh bazata Sabu ba ko kadan,
Zainab bazai yiyu su saka Mata ido tabar yarinya tayi watsi da dangin uwarta ba,
Waccar samun wahala wato Laylan sun samu ta fita rayuwarsu tunda Ms Na'ima ance ta tafi da ita sunsan aikin wahala kawai ya Isa ya juyar da sauran qanqanuwar lafiyar qwaqwalwarta.
Sa'adah Bata gida ta fita karban wani sako a school Dan hakan ma suke zaune palon Anne da tuni ankaisu palon Sa'adah din
Dayake kusan bankwana Suka taho yi tareda Jin idan tareda Sa'adahn zasu tafi tunda abbansu dai dawowa zaiyi Dan Haka suka dasa sabon zaman jira,
Anne sakawa Tai halima takaisu palon Sa'adah Dan su sake yanda yakamata kafin dawowan Sa'adah din.
Tun Rana suke jiran dawowarta har kusan yamma batadawoba
Momy tayita Kiran wayarta Bata dagawa
Anne ma tayita Kira itama Bata dagawa.
Momy ce tafara Shiga damuwa sai Anne sbd magrib da aka fara Kira sbd tun dawowar Sa'adah hannunta Bata tana fita takai dareba a waje da sunan makaranta saidai idan biki ta fita kokuma tare suka fita sukai daren
Dan Haka take tasan ba lafiya ba.
Hankalinsu tashi yayi sosai Anne tafara kiran wayoyi tana tambaya ko Sa'adahn na can,
Momy tsabar tsoro da damuwa bin Anne kawai take da Ido tana jiran Jin labari Mai ma'ana Amma Babu inda ba'a buga wayaba da ake tunanin samunta acan saidai Bata can din.
Tashin hankalin dasuke ciki zuwa yanzu yagama girmama sbd har qarfe Taran dare ba labari Mai.
Kokarin Kiran M Kabir tsohon Secretary din Turaki tayi ta sanar Masa abinda yake faruwa yace Mata gashinan zuwa yanzu.
Kafin ya iso gidan yafara shigarda missing complaint sai gashi tun kafin ya isa gida aka sanar Masa ansamu accident tunda Rana na wata motar data buge motar wata budurwa.
Bai Isa gida ba Saida yaje ya tabbatarda Sa'adah ce,
Ita din ce saidai Kam tanajin jiki sbd ta bugu sosai qafafunta da hannunta dama kanta duk bandage ne
Qarin baqin cikin abin Wai Wanda sukai hakan sun tafiyarsu ba'a kamasu.... Saidai baya tunanin guduwa sukai yafi tunanin koma su waye sunada kudi sun biyane Ana barsu sun tafiyarsu ake cewa sun gudu.
Su Anne yakira ya sanar musu halinda ake ciki
Take jikin Momy ya mutu sbd yanda takeji azuciyarta gameda lamarin tasan akwai masifar da zata sameta...
Suna Isa asibitin kallo daya Momy tayiwa Sa'adah takasa riqe kanta wasu hawaye masu tsananin zafi suka balle Mata ta share tana kokarin Kame kanta sbd Anne data bayyanarda damuwarta Mai tsanani a fili Kan al'amarin,
Haj Karima kuwa cewa tayi sai an Nemo wainda sukai wannan hadarin Dan bazai yiyuba ace sun gudu ba dalili bane.
Cikin gaggawa aka sauya Mata daki raga emergency din dasuka sameta.
Suna cikin wannan tashin hankalin su Turaki Suka sauka Nigeria tsakar Daren.
Gida aka kaisa direct bayan ankai Abba lafiyayyar masaukinsa.
Dole Momy ce aka Bari ta kwana a asibitin su Anne Suka koma gida
Haj Karima ma ta wuce gida.
Washe gari tunda Turaki da kansa yakai Abban asibiti
Yakuma qi sanarda Laylah abin daya samu Sa'adah.
Sauyawa Sa'adah asibiti akai washe garin aka maidata asibitin dasuke zuwa..
Bayan sun fito yashiga mota ya zauna ya Dan dago tareda kallon A Abdoul dake gaban motar zaune cikin kamewa da murya Mai daukeda girman kamewarsa yace"
Abincika komai akan wannan abun daya faru sbd ance ko kwanaki mota tayi kanta,
A bincika komai inason sani.
Gyada Kai A Abdoul yayi Yana cewa"
Inshallah.
Barin asibitin sukai Suka nufi gurin wasu baqinsa dazai gani Dana abbansu Laylan yabar Masa Mota daya da drivern dazai maidasa masauki idan yagama.
Dr faruk daya dubata last time shine yanzu ma take hannunsa Dan Haka ya kalli Anne da zata wuce gida yace"
Anne akwai wasu result dinta na farko da basa cikin folder dinta inaga last time dasu kukaje gida Muna buqatansu Dan result dinta na yanzu munason duba wani abun.
Ok ba damuwa inaga suna cikin handbag dinta da akazo asibitin da ita last time din zansa aduba sai akawo Inshallah.
Ok, sai abada da wuri Muna jira Dan treatment dinta zai tsaya saimunga wancan result din.
Anne na Isa gida dakin Sa'adah tafara wucewa direct tafara duba handbags dinta daya bayan daya.
Kasa ganin komai tayi Dan Haka ta nufi drawers tafara dubawa Suma.
Nanma bataga komaiba dan haka ta nufi wardrobe dinta ta bude tafara dubawa.
Handbag dinta daya tagani kicin kayanta a boye Dan Haka ta janyo tareda budewa ba Bata lokaci taga takardun asibitin aciki..
Ta kwaso ta fito dasu gabaki daya tasaka a handbag dinta kafin ta nufi bedroom dinta.
Sai dare suka tafi Kai abincin dare asibitin itada halima.
A dakin Suka tadda Abba da momy sai Haj Karima da zuwanta kenan itama tareda umma Da tuni ta iso garin yau Dan Shiga al'amarin tunda Turaki na qasar yagansu ya Sansu amatsayin dangin uwar matarsa.
Cikin girmamawa sukewa Anne barka da zuwa tana amsawa cikin yabawa karamcinsu,
Takardun Datazo dasu ta kalli halima tace"
Halima bawa Dr faruk takardun gasunan.
Dr faruk karba yayi ya fice daga dakin Dan dama yagama abinda zaiyiwa Sa'adahn data farka Amma Bata iya magana ko kadan sbd azabar ciwon da kanta keyi.
Minti hudu da fitar Dr faruk ya dawo dakin daukeda folder din Sa'adah ya Ciro wata takarda yana kallon Anne dake kallonsa ganin ya dawo
Kowama kallonsa yakeyi suna jiran Jin Mai zaice ya miqawa Anne takardar Yana cewa"
Wannan inaga ba nata bane Dan a cikin namu gwaje gwajen bamu samu ciki a jikinta ba.....
Tsit sukai gabaki daya dakin suna kallonsa,
Anne da Momy da Abba dasukasan batada aure da mamaki da suke kallonsa,
Umma Jamila kuwa cikin kasa boye halin data shiga tayi saurin cewa"
Takardar ciki ta nuna ita ko me?
Miqawa Anne takardar yakuma Yi ganin tana Masa kallon buqatan qarin ya kalli sauran Yan dakin yaga duka iyayen Sa'adahn ne ya maida kallonsa kan Anne cikin nutsuwa yace"
Takardar pregnancy test ne tareda scanning Amma banajin nata ne sbd ba'a qasar Nan akaisa ba,
A America ne,Los Angeles....
Anne najin hakan ta karba takardar da sauri ta karance tsaf taga abinda yake ciki da sauri ta dago ta kalli Sa'adah Dake zaune tanajinsu Bata iya cewa komai sai rufe Ido datai cikin yanayi na rashin abin Yi.
Qamshin Bois elite ne yafara shigowa dakin Abba da Anne dasukan asalin waye Mai wannan qamshin Suka kalla kofa kafin shigowarsa
Tukuna ya shigo A Abdoul na bayansa
Dukkaninsu suka waiwayo suka kallesa yaqaraso cikin tsananin kwarjininsa daya Hana su umma Jamila tada hayaniyar murnar batun ciki da ake lokacin....
Haj Karima ce tayi qarfin halin gaidasa tana maida kallonta Kan Anne Baki washe tace"
Barka da arziki,
Ashe ciwon dai harda juna biyu ajikinta,
Allah ya raba lafiya yasa anbude hanyar tara zuria kenan...
Kujerar da A Abdoul ya gyara Masa ya zauna Yana kallon Abba dake neman rudewa da zancen da ake...
Anne ganin Kar rashin fahimtar tayi yawa ta bude Baki tana dauke kallonta daga kan Turaki daya Gama cika musu Ido dakin da kwarjini tace"
Ba sunan Sa'adah ne ajiki ba, takardar ba tata bace sbd ba komai ajikin Sa'adah.
Miqawa Turaki takardar tayi tana cewa"
Duba kagani ko zaka gane sakamakon waye.
Karba yayi tareda Dan kallon takardar akan sunan Mrs AB TURAKI idonsa yafara sauka kafin ya kalla date din jike jikin takardar.
Da sauri ya gangara da idonsa Kan signing dinta Dake qasan takardar.
Wani irin yanayi Mai wuyar fassarawa ya Shiga saidai mutanen Dake gurin ya sanyashi dannewa ya kame,
Miqawa A Abdoul takardar yayi bayan ya nade Yana miqewa yace"
Allah yabata lfy.
Kofa ya nufa ya fice A Abdoul na bayansa
Yan dakin duka kowa tsit yakuma Yi Dan su Kam Basu gane komaiba Kuma yanzu.
##MAMUH#
[6/28, 8:56 AM] MG💋: *_Mamuhgee 43_*
Yana ficewa Momy taqi waiwayowa ta kalli Yan uwanta da duk anbi anhansu gane komai,
Sunanson nuna mrnarsu da farin cikin wannan samu daya samesu Amma Kuma ganin daga uban gayyar Turakin ya fice baice komaiba hakama Anne takasa cewa komai Dan itama kanta duk da tana zargin cikin idan bana Laylan bane Amma Kuma da wuya hakan ta faru, ita Tama Rasa tunanin kamawa,
Abbansu Sa'adahn ma kasa Kama kowanne tunanin yayi Dan Sam Bai kawo ma Laylah a zancenba tunda yasan karatu takeyi tukuna,
Kuma Turakin ma baida ranar amsarta amatsayin Mata shiyasa ma zai nema sallamarta daga Turakin Dan gudun shiga haqqin takurawa Amininsa.
Momy ce kawai tunanin farko daya shigeta shine tabbacin cikin Laylah ce take dauke dashi ba kowaba, sbd sanin barewa bazatai gudu 'danta yayi rarrafeba,
Ms Na'ima tayi babban kuskuren daukan riqon Laylah sbd batasan cin Amana a jininsu yakeba.. yanzu gashi itada Yan uwanta za'a kunno Mata masifa Dan kuwa su umma Jamila Allah kawai yanda zasu dauka wannan al'amari da aka rufesu baibai tsabar son Rai da cin Amana irin na Kawu saidu daya daura auren.
Anne Bata Gane sauran zancen da ake a dakin sbd hankalinta gabaki daya baya Kai tunani take shiga daban daban na wannan takardar...
A saninta babu wata Mrs AB TURAKI Bayan Na'ima da Laylah,
Babu Kuma wata tsautsayi ko kaddaran dazai kawo sakamakon awon cikin Na'ima hannun Sa'adah,
Laylah ce kawai duniya sukeda kusancinda al'amari irin wannan Bata zaizo hannun Sa'adah...
Idan Natane to shi wannan ciki Kuma..... Lumshe ido tayi Ahankali tana cire zancen cikin kanta gabaki daya Dan kuwa bazata taba Gane komaiba ayanzu zata saka ido taga Inda ciki zai bullo daga Mr Turakin koma wacece acikinsu.
Gida ta miqe ta wuce tabarsu suna buqatan kebancewa da Momy Suma Amma ta Hana kanta sakat da aikin hidimarta Sa'adah da zata bawa tea Mara zafi Dole Suka tafi Suka barta ba Dan sunbar zancenba Wanda Dole ayisa ai.
Saida suka wuce kafin Abba ma ya fito ya wuce da drivernsa da motarsa da aka Ware Masa.
********
Tunda suka baro asibitin Yana zaune a motar Bai ce komaiba Yana zaune hankalinsa kwance Kamar Babu komai cikin ransa
Saidai wasu