Showing 81001 words to 84000 words out of 108894 words
feelings da tsantsar nutsuwa yakeji na wanzuwa cikin ransa.
Harsuka Isa gida Babu wata magana daya furta
Dan Haka A Abdoul na ganin yafito motar ya Ciro takardar da tuni ya sanyata cikin envelope ya miqa Masa a ladabce Yana cewa"
Mu kwana lafiya.
Karban envelope din yayi tareda wacewa ya nufi hanyar shiga makeken palonsa Dake sashensa dayafi na kowa girma a gidan ya shige.
Yana shigewa A Abdoul ma motarsa Dake gidan yanufa ya bude ya shige tareda tayarwa yabar gidan ya nufi gidansu Dan Mahaifiyarsa anan Abuja take zama duk da mahaifinsa ya Jima da rasuwa.
Bai tsaya palonsa ba Kai tsaye bedroom dinsa ya nufa ya shige tareda nufar jikin drawer gefen gadonsa ya janyo ya sake tareda rufewa Yana aje wayar hannunsa ta nufi toilet yashige.
Wanka yayo yafito sanye da farar bathrobe ya nufi gaban mirror ya tsaya Yana goge jikinsa da qaramar towel fara.
Abubuwan daya Saba na kafin kwanciyarsa yayi kafin ya Sanya fararen pyjamas da slippers masu taushin gaske
qamshinsa na Bois elite na sake mamaye dakin ya nufi Kan sofa Dake dakin ya zauna anatse tareda daukan wayarsa Dake silent sbd rashin son damuwa
Kai tsaye numbernta dake sama yasaka kira.
"Hello Abbah" tafada cikin muryarta Mai taushi dake son bayyanarda kewarsa datai.
Boyayyan numfashi ya sake sbd koyaushe muryarta ta sauka kunnensa tana motsa duk wani jini dake yawo jikinsa.
Ahankali ya bude Baki Kai tsaye ya sakar Mata tambayar"
Are you pregnant?
Wata nawa ne?
Yana Nan ko kuwa?
Tsit tayi Jin tambayar data zuwar Mata a bazata
Kuma cikin yanayi na kamewarsa yayi Mata tambayar Dan Haka sai jikinta yayi Sanyi tana neman daburcewa,
Cikin kame kame tace"
Abbah kayi.....
Akaro na farko a rayuwarsu daya sakar Mata tsawa Yana cewa"
Amsa nake fara so, are you pregnant, yes or no¿
Ahankali tayi qasa da murya cikin sanyin jiki tace"
Yes Abbah.
Rufe ido yayi ahankali cikin yanayinda yakasa fassarawa tsawon mintuna kafin ya bude idon ya sake bude Baki ahankali yace"
Meyasa bansaniba?
Tsawon wane lokaci¿
Abba Ina tsoron mum ne tasani,
Nima bansan dashiba farko
Daga baya ne nasani
I'm sorry abbah, kayi hkr Dan Allah"" hawaye ne Suka balle Mata Jin yanayinsa kaman ransa ya baci akan rashin fadar Masa din.
Lumshe ido yayi yanajin yanda numfashin kukanta ke sauka cikin kunnensa Yana taba zuciyarsa
Sai daya sauke ajiyan zuciya ahankali kafin cikin nutsuwa ya bude Baki yace"
Ya Isa Haka,
Daina kukan,
tell me, is everything okay? I mean the baby, kinajin komai lafiya?
Ki taba ganin likita?
Share hawayenta tayi tanajin kewarsa na sake kamata sbd cikinta yafara motsawa yanzu,
Gabaki daya cikin tsoro da tashin hankalin dawowar mum take ta bude Baki ahankali cikin yarinta tace"
Abba yayi girma Ana ganinsa,idan mum tadawo zata gansa,
Bansan me zataceba..
Babu abinda zai faru okay¿
Zan dawo da wuri zan kaiki kiga likita da kaina,
Ki ringa kula sosai yanzu, and ki daina saka su skinny jeans dasu kayanki masu matsewan nan Zaki takura kanki da babyn.
Zansaka akawo Miki nurse dazata ringa kuka Dake kafin nadawo.
Kwantawa tayi Kan kujeran datake zaune tana Jin son Abbanta na sake shigewa koina nata musamman cikin jikinta yanzu duk lokacinda ta Dora hannu akansa Abban takeji har cikin jininta sonsa na sake kamata.
Ahankali ta furta"
"Abbah, are you happy with th...."
kasa qarasawa tayi sbd nauyinda kalmar Tayi Mata saidai Kamar daga sama taji saukan muryarsa Mai dadi da Kamala cikin kunnenta yace"
I love the baby,and I love his mother....
I love you both.
Cikin tsananin farin ciki da nutsuwa
jikinta na mutuwa da kalamansa tace"
We love you too Abbah.
Ms Na'ima Dake tsaye bakin kofar bedroom din nasa kasa tsayuwa tayi sbd wani jiri jiri datake gani,
Me take ji Abu kamar a mafarkinta.
I love you taji abakin Turaki,
Maganar baby da uwar baby yake bayan saninta Sa'adah na asibiti Kuma tabbas sun biya kudin gaske likitan asibitin da aka fara kaita ya tabbatar musu da Babu ciki ajikinta suna murnar ya zube me take Shirin ji yanzu??????
Innalillahiiiii"" tafada a fili idonta na rage ganin haske ta juya da sauri Takoma inda ta fito tana bude idanuwanta da hannuwanta Dan bakin Rai Bata gani Sosai.
Tana Shiga palonta a haukace ta zubawa siddika Kira tana cewa"
Kaini dakina bana gani Sosai.
Da sauri siddika takaita daki ta fito sbd ganin masifar Dake cikeda idon dayasa Bata gani Sosai...
Hannu ta Dora akai tanason kurma ihu Amma maqoshinta yaqi budewa ta zube bakin kujera tana cewa"
Wace kaddararrarce Turaki yake cewa I love you harda baby?
Neman Mata Turaki ya fara kokuwa wani auren yayi Basu saniba?
Nashiga goma na lalace,
Mata nawa Turaki yakeson nabi Ina hallakawa¿
Walh bazan yarda da wannan masifarba,
Ko ba aure yayiwa koma wacece wannan cikin bazata Bari a haifesaba,
Ta yarda tayi koma menene Amma wlh bazata yarda wata ta haifawa Turaki 'yayaba.....
A haukace ta dauki wayarta tafara neman numbern Zinat....
Tana dauka cikin yanayin tashin hankali Mai tsanani da rudewa tace"
Zinat abun yamun yawa Turaki zai cinnamun hauka,
Zinat Turaki wata yayiwa ciki wlh,
Zinat Turaki I love you yake furtawa wata.... Zuciyata bugawa zatai..
Cikin gajiya da wannan masifa itama Zinat din tace"
Ki nutsu Na'ima tunda kema kingano Cinna Miki hauka al'amarin Turaki zaiyi,
Tashin hankali bazai Bari musan abinda mukeson saniba...
Turaki yagama bamu mamakin duniya tunda yayi aure bare yanzu Dan yayiwa wata Mai rubutacciyar qaddara a hannunmu ciki,
Fatan dai kin gano wani Abu akanta ba haukar banza kikayoba Kika dawo?
Kasa magana Ms Na'ima tayi sbd batama San Mai zataceba,
Da alama gwara shaanin Sa'adah shi data san komai akan wannan da batamasan ta Ina zata faraba saidai Abban abin data sani shine koma yayane itace ta Los Angeles da khairat ta fada Mata Dan Haka sake tattarawa zatai Takoma Dan sai tana Atlanta zatafi Gano wani abun Dan idan zata mutu tadawo duniya Turaki bazaice Mata komaiba akan lamarin Koda ta tambaya kuwa sai lokacinda yaga Dama yaso fada.
Cikin takaici Haj Zinat tace"
Koma meyene Anne tasani Amma dayake batada adalci shine tayi shiru tabarsa ya rufeki a baibai saidai kawai akawo miji jaririn 'da ace Miki gashi na Turaki ne tsabar a nuna bakida wani amfani bayan tun farko shi tukarin ai shine Mara amfanin,
Tunda ya warke yanzu Dole zai ringa tsalle tsallen zuwa gurin Mata bazai iya tsayawa akan wadda ta zauna shekaru dashiba.... Mtsss Ni ke kanki Na'ima wani lokacin kayan takaicine Dake,
Ki tattare dukiyar ki rabu dashi yaje ya nema matan duniya idan zai iya Amma kin tsaya ke acikin bacin Rai Nima aciki...
Zinat wallahi bazan iya rabuwa da Turaki ba tun wuri daina maganar rabuwar Nan,
Zaunawa zanyi naringa cin uban duk wadda tayi gangancin shigowa rayuwarmu nidashi tunda kwadayin abun duniyar kowa a zuba Masa a zuciya.
Haj Zinat tafi Jin zafin Anne Akan Turaki sbd Babu kalar asirin da basuyiwa matarnan ba Amma yaqi ci,
Idan suka mallaketa tamkar sun mallaki Turaki ne sbd a duniya ba maganarta dayake tsallakewa saidai tsohuwar tamkar wadda take kwana rungume da Qur'an Dan kudin dasuke narkawa bokaye da malamai bama gaskia bane Amma a banza Dole Suka watsar sbd basa Wasa da lissafi, bazasu iya cigaba da hasararda Babu riba acikiba.
Cikin son Kai qarshen matsalarsu kowa ya huta Haj Zinat tace"
Zan Kira khairat mugun bincike za'ai Mana asan koma wacece daga Nan sai asan matakin dauka...
Cikin zafin Zuciya Na'ima tace"
Bazan iyaba kasheta zanyi har ita har cikin..
Idan kin kasheta acan saikiyi bankwana da Turakin da kikai kisar dominsa Dan kina gidan yari ko lahira zai aura wata Matar.
Zinat meyasa bakya fadar alkhairi yanzu koyaushe muguwar data kikemun,Wai ko mun fara samun matsala ne?"" Tafada ranta na baci Sosai akan baqin datake ciki.
Cikin takaici itama Zinat din tace"
Aiki da hankalinkine bakyayi koyaushe irin Haka ta taso kedai maganarki kisa,
Kinsan hukuncin kisane?
Kin aikata Abu Dan wani Amma kinaji kina gani za'a rabaki da duniyar Kuma Babu abunda zaiyi miki,
Ni bana komai ba lissafi kin sani,
Inada 'yaya idan Ina rufe Ido Ina biye Miki gurin yin komai da tuni mun Jima da zama Yan gari a lahira,
Dan Haka bazan biye Miki mu hau jirginda ba saukaba sai filin Danasani da lahiraba Dan hake kema ki nutsu cikin ruwan sanyi zamu zuba rashin arzikinmu batareda mun barwa kanmu abun fada ba.
Naji zancen ya Isa Haka sbd Zinat yanzu kin daina gane ciwona,
Kedai idan magana Bata fitowar kudi bace batada babban mahimmanci agurinki,
Yanzu kisa Fahad yamun komai cikin gaggawa inason komawa,
Tunda Turaki ya fara fadar I love you kinsan Yana gap da gane mace ciki da wajenta da halayensu da kyau Wanda kema kinsan hakan nada barazana agun mu daga lokacinda yafara karantar son dukiyarsa a jinina yake.
Zamuji da wannan idan mungama da wannan babbar matsalar dake gabanmu Dan Nima ko a mafarki bana Mana fatan wata macen da haifawa Turaki 'yaya idan bakeba to kowama bazai masaba a zauna ahakan yafi tunda kunada 'yar riqo.
##MAMUH#
[6/28, 12:40 PM] MG💋: *_Mamuhgee 44_*
Anne shiru tayi Bata sake tada maganar al'amarin takardar cikin ba sbd batasan wa zata Kama zancen dashiba,
Sa'adah dai batace komaiba sai cewa ba nata bane Haka kawai tace musu tabarsu a duhu,
Momy Bata damuba sbd tasan Babu abun daya hada sa'adahnta da wani zancen ciki Dan Haka itama tayi watsi da zancen tunda cikin Laylan Bai shafeta ba.
Abbansu ma share zancen yayi sbd Ganin Anne batace komaiba Kuma yasan tarbiyar yaransa daidai gwargwado duk da yajima baya taredasu
Amma tunda yanxu tarbiyarsu a hannun Anne take bashida ta cewa Akan maganar yabar zancen tunda yasan sunsan abinda suke.
Umma Jamila ce ta daga hankalinta Kan ayi maganar qarshe Sa'adah da kanta tace"
Ba'a son tada zancen ne sbd matar Turakin Ms Na'ima da ake gudun fitinarta.
Wata dariyar bin iska Umma Jamila tayi tana cewa"
Akwai Wanda ya Isa aji shakkarsa akan samu da qaruwa daya samemu na farin ciki,
Ita Ms Na'iman inace da Turakin take takama? To shine ake wani boye boyen karta sani.
Haj Karima dake Shan tea ahankali cikin nutsuwa da takama tace"
Sune sukasan wata Ms Na'ima
Mu abunda yake gabanmu mukeyi,
Ciki dai tunda Allah ne ya badashi ai Babu wata Na'imar dazata sakamu kame kamen rashin fadarsa.
Cikin sanyi Sa'adah Dake sin plantains ahankali tace"
Wlh tanada ban tsoro mama,
Komai zata iya,
Dan Allah abar maganar shine yafi zama alkhairi..
Tsoronta kike kenan? "" Cewar haj Karima tana kallon Sa'adahn a zube.
Ba boye boye tace"
Eh wlh Ina tsoronta mama,
Nasan komai zata iyane.
Umma Jamila ce ta kalli Momy dake saka kayanta cikin akwatinta sbd tafiyar da zasuyi Dan ansallamo Sa'adahn suna gidan Haj Karima daga Nan zasu wuce gabaki dayansu duk da sai Sa'adah Takoma gida ta dauko kayan da zatai tafiya dasu,
Cikin mamaki da takaici tacewa Momy"
Yanzu Zainab Haka Kina kallo Kika koyarda Sa'adah tsoron kishiya?
Sbd ke Taki zuciyar ta mutu gurin jinyar mijin daya zaba Taki kishiyar akanki da yarki shine Zaki kashewa yarinya zuciya da tsoron kishiya kina kallo harda bakinta take fadar tsoronta takeyi.
Rashin Jin dadin maganar da ake fadawan Momy yasa Sa'adah kallon Momy da batace komaiba ita sai shiru datai tana cigaba da shirya kayanta cikin akwati,
Ta maida kallonta Kan umma Jamila dake fada cikin takaici zatai magana Haj Karima ta katseta da cewa"
Yi mana shiru mutuniyar banza,
Shiyasa kika kasa gaba Kika kasa baya acikin gidan,
Kinkoma tamkar Yar riqo a gidan ma Matar gidan ba,
Tsabar rashin yanci a bangaren Mahaifiyarsa aka Baki Palo da daki
Bayan ita tanada makeken bangaren guda a gidan da zata aje irinki guda nawa,
Drivers ke janta da motacin Alfarma tana yawo a agarin Abuja da wajenta Amma ke kece kike tuqa kanki Dan kina ganin ansiya Miki tsadaddiyar mota bayan motocin Turakin da ake fita da ita cikinsu daya zata siya biyar din Taki harda canji Mai yawa...
Umma Jamila da Shirun Momy ke Bata ranta ko yaushe tace"
Ahaka me tasamu bare mu iyayenta muce 'yarmu na auren Amb AB TURAKI,
Alhaji Qarami Babu shige da ficen da bayayi Dan yasamu ganin Turaki shida honourable kwangila sukeso kamar me ko manyan kudi zasu saukar musu Amma koyaushe yarinyar Nan cewa takeyi baya qasar
Ashe tsoron zuwa gurinsa take sbd kishiya,
Wlh Allah yayi wadaran naka ya lalace.
Yanzu dai tagama wannan shashancin mutafi ai muma lokacinmu yazo Dan idan muka tafi zamu bude namu asusun lissafin agurinsa tunda ga ciki
Kafin ki dawo saikin haihu tunda ba qasar yake zamaba Kuma kingama karatun ai dama Dan Haka muma Bismillahi.
Daga Sa'adahn har momy Babu Wanda yasake cewa komai,
Suna sauraron su umma Jamila nata musu fada kokuma fade da gorin dawainiyarsu dasuke Dan taimakawa tun lokacinda Sa'adahn na qarama da Abban baya wani zama har lokacinda yake jinyarsa sune suke Dan taimaka musu.
Har dare daga ita har momyn Basu huta da fadan umma Jamila ba Saida Haj Karima ta tsayar da zancen da cewan ai yanzu tunda Sa'adahn na hannunsu zasu qaru da Turakin.
Da wannan umma Jamila ta sarara musu har drivern Anne yazo ya dauki Sa'adah a gidan Suka tafi gida.
Tana Isa gida komai na dakinta halima ta gyara ko'ina sai qamshi da sanyin AC ke tashi Bata wani zauna ba ta shige ta kwanta sbd kunyar Anne takeji batasan Mai zatace Mata gameda cikin Nan da Allah yayi bayyanarsa gaban kowaba,
Takardar acikin hanbag dinta dasukaje asibitin tun wancan lokacin take Kuma tunda tadawo take boye hanbag dinma gabaki daya sai ranarda zata fita ta janyota ta fita da ita Kuma ranar ne tsautsayi yahau kanta har tayi murnar Babu Wanda yagani a jakar shiyasa takuma boye jakar sai yanzu Allah yanufa zancen zai fita,
Kunyar Anne datake ji shine na boye Mata itama Basu fada Mata ba bayan ta cancanta tasani sbd yanda ta daukesu tamkar jininta
Kuma tasan idan Annen tasani Babu yanda zatai tabari a cutatar da Laylan gashi rashin wayonsu yasa tasamu zancen daga sama gashi taqi cemata komai akan zancen
tamaqi tayarda zancen tayi kaman ba'ayiba.
Kwantawa tayi tareda neman numbern Laylah wadda yanzu laulayinta yafara yawa ba komai take iya ciba sai fruits datake Sha kaman me,
Ringing wayar taitayi baa dagaba Dole ta hakura ta qyaleta.
Washe gari jirgin safe zasubi Dan Haka tunda safe ta tashi ta shirya Kaya cikin qaramar suitcases guda biyu ta shirya tafito sbd driver na jiranta zai kaita gidansu Haj Karima dagacan zasu dauka su umma Jamila su wuce airport Abba daban zaiyi tafiyarsa ba taredasuba saiya gana sosai da Amininsa duk da kusan kullum tunda suka zo Abujan suna tare.
Anne cikin kulawa Tace Mata ki kula Sa'adah kinji,
Allah yadawo Dake lafiya duk da nasan Zaki kwana biyu sosai acan kafin kidawo.
Rumgume Annen tayi jikinta na sanyi tace"
Zanyi kewarki Anne,
Kuma Inshallah bazan Dade sosaiba Zan dawo.
Murmushi Anne tayi tana cewa"
Ba komai ki zauna da momynki tayi kewan zama Dake idan tagama ganinki da kyau Kya dawo,
Allah ya tsare.
Amin" tace tareda juyawa ta wuce halima na bayanta.
Harta Kai kofa tadawo ahankali ta tsaya gaban Annen cikin sanyi da nutsuwa tace"
Anne,
Anne Laylah ce take daukeda cikin,
Yanzu wata cikin na biyar......
Da wani irin mamaki Annen take kallon Sa'adah,
Wani murmushin manyanci ne ya subuce Mata sai kawai tace"
Ita Laylan?
Har wata biyar Kuma shine take zaune gida daya da Na'ima?
Shiru Sa'adah tayi tana Rasa abin cewa sbd yanzu Kam kowa yasan idan Na'ima Takoma yanzu ba shakka zataga ciki jikin Laylah, saidai rashin sanin mahaifin ciki shine saukin masifar.
Wuce driver na jira karkiyi latti.
Wucewa Sa'adah tayi tabar Anne zaune tareda Shiga mamakin duniya dama jinjina zurfin ciki irin na Laylah,
Tabbas tasan Na'ima zata buga rikici na gaske idan tasamu maganar cikin mijinsu a jikin 'yar datakewa kallon Yar riqonta...
Tuno lokutan datake waya da Turaki tanajin mace tayi kusan lokuta da dama,
Kenan Laylah ce....
Kasa tunanin komai tayi kawai sbd daga Turakin har Laylan sun tsundumata mamaki harma batasan Mai zatace ba,
Me zata fadawa mutanen data gama tanadin gyaran Amarya agurinsu da sauran shaaninsu...
Abu daya ta yanke a ranta shine dauko Laylah kafin Na'ima Takoma.
*****Zaune suke a lafiyayyan palon Turaki Dake cikin gidan
Yana zaune 2seater sanyeda skyblue yadi Mai tsananin taushi daya sake bayyanarda kwarjininsa
Gabaki daya turaren Bois elite ne ke sanyaya palon da qamshin ga sanyin AC daya Gama Kama koina hankalinsu akwance,
hankalinsa na Kan wayarsa yana kallon sakon LAYLAH yashigo na wasu kisses data turo Masa.
Ya Dan dauke Kai Yana Kama kansa cikin basarwa sbd Abban Laylan dasuke tare Yana zaune shima suna magana.
Dan gyara murya kadan yayi sbd neman sarkewar Dake da emojis din datake sake turowa
Yadauki wayar ya kashe gabaki daya sbd zata iya rikitasa ya Rasa meyake fada gaban Mahmoud dayake basarwa sbd karya gano waye.
Cikin nutsuwa Abba ya kalli Turakin bayan yagama kashe wayarsa ya aje gefe da sautin bayyanarda zallar gadiyarsa a natse yace"
Turaki Babu abinda Zan saka maka dashi sai godiya kawai,
Kayiwa Allah,
Kayiwa abota,
Kayiwa zumuncinka da Zainab,
Kakuma yiwa marayin Allah Dan Haka Banda bakin godiya daga Kai har Anne Ina muku fatar samun sakamakon gidan Aljanna.
Cikin basar da zancen ya Dan kalli Abban yana cewa"
Inaga ai mun rufe wannan maganar right¿
Numfashi Abban ya sauke ahankali da Jin nauyin abinda zai fada
Yadai Daure tunda ba boyo tsakaninsu da Aminin nasa ya dago ya kallesa yace"
Sai maganar Laylah.....
Sai alokacin Turakin ya dago a hankali ya kalli Abban Jin sunanta.
Gyara zama Abban yayi Yana cigaba da cewa"
Nasan Bai kamata ba nashiga zancen tunda ikonta a hannunka yake yanzu Amma tunda kamar alfarmace tun farko kayimin ka amince da Aurenta
Yanzuma Ina riqon Alfarmar karka duba tarayyata dakai idan har bakada raayin auren zaka iya sawwake Mata tadawo gida ko ahakan kayi matuqar kokari da taimakawa sosai wlh........
Tunda yafara hada shimfida da LAYLAH Bai sake kallon cikin idon Mahmoud ba sai yanzu daya dago ya zuba Masa manyan fararen idanuwansa akansa batareda ya bude Baki yace Masa kala ba,
Abban yasan Turaki farin sani,
Babu halinsa da Bai saniba sai Wanda yaqara daga bayan Nan saidai duk da hakan idon da Turakin ya zuba Masa bazai iya cewa na menene ba
Dan Haka ya Dan muskuta Yana gyara zama jiran mgna ta fito daga bakin Turakin Dan Yama kasa qarasa sauran zancensa...
Ahankali Turakin ya dauke ido daga kan Abban Yana saukewa Kan Tv Dake aiki batareda ya iya cewa komaiba,.
Shi kansa Abban shiru yayi sbd yasan maganar na buqatan nazari Dan Haka ya kalli Turakin murya a mace yace"
Inaga gobe Zan wuce Nima A Abdoul yagama min booking ticket da komai...
Tafiyar safe zanyi saidai idan naji daga gareka.
Har lokacin Turaki Bai iya cewa komaiba sai gyada Kai da yayi Ahankali cikin nutsuwa.
A Abdoul ne yatafi maida Abbansu Laylan daga can ya wuce gida shima sbd dare yayi Daman.
Tunda Mahmoud yatafi Yana zaune inda ya barsa qafarsa daya Kan daya idanuwansa sun sauya sosai ya rufesu ahankali ya bude