Showing 12001 words to 15000 words out of 108894 words

Chapter 5 - NOOR ALBI COMPLETE

Start ads

08 Aug 2025

12

Middle Ads

qaraso ya ajeta Kan table din gabansa Dan yaduba dakyau ya koma ya zauna kujerar daya taso.

Shiru palon yayi sai Yar sautin makekiyar TVn Dake palon tana aiki yake tashi kadan.

Ahankali yake duba sakunan harya Gama kafin ya dago fuskarsa cikin nutsuwa ya kalli A Abdoul Kai tsaye da wata irin muryarsa Mai amsa Amon tsabar nutsuwa da kwanciyar hankali tareda wani irin kamewa yace"

Samun bayanan Amb Arabi nada matuqar mahimmanci Dan Haka cikin awa ashirin da hudu idan Babu wani bayani daga garesa ka shirya kaje da kanka din.

Yes sir,
Zan fara Shirin tafiya kafin mu samesa din.

Gyada masa Kai kawai Turakin yayi tareda Kai hannu ya dauki wayarsa Dake gefe aje tanata blinking light alamar Kira nata shigowa tun dazun din,
Zubawa sunan Kiran daya shigo wayar tasa idanuwansa batareda ta dauka Kiranba har Saida ta katse Kiran
Ya dago ya kalli A Abdoul daya zuba Masa ido Yana satar kallonsa Yana tunanin da ace mace ce wayar AB Turakin da tuni ta Dade da haukace tuburan sbd idanuwansa wani irin Hasken kwarjini da rikitarwa garesu Wanda shi kansa daya Jima Yana aiki tareda dashi kullum idanuwan Turakin suka kallesa rudewA yakeyi yaji baya iya ko dagowa,
Duk manyanci da shekarun Turakin bayajin Nan kusa akwai inda samari masu sabon jini ajiki zasu Shiga Bai shiga ya takesu ba Dan kuwa shi din wani irin ingarmane Mai cika idanuwa ga ladaftarwa.

Miqewa yayi cikin girmamawa yace"

Zan qarasa office na duba sauran schedules dinka na gobe,
Ahuta lafiya.

Ficewa yayi daga palon Yana Ciro wayarsa daga aljihu da aketa Kira shima yanajin vibration dinta ba Daman dauka Yana magana da Turaki.

Bayan fitar A Abdoul sake daukan wayarsa yayi yana kallon numbern Amininsa na har abada da baida tamkarsa Dan kuwa tamkar iyaye daya suka haifesu Haka sukejin suna saigashi banbancin rayuwa yasa sunyi nesa da juna duk da dai rashin lafiyar Mahmoud din tasake nesantasu da juna sbd tun farko yasa ya daukesa gabaki daya ya maidosa Nan qasar Amma issues na familyn Mahmoud din yasa abun Bai yiyuba Dan kuwa Basu aminceba sbd daga danginsa har na uwargidansa zainab Babu Wanda ya amince da hakan sbd suna tsananin fushi dashi akan aurensa da 'dayar zainab din Wanda shine sanadin auren Dan kuwa shine yakamata ya aureta Amma yarasa meyasa Sam alokacin ko kallonta yayi sai yanajin wani irin yanayi na Jin nauyi da kawaici,
Da kansa yakejin ko kalmar aure a tsakaninsa da ita ta haramta tashiga bare har akai ga yin shine dalilin dayasa Mahmoud din ya aureta Kuma har Allah yayi rasuwarta Bai dainajin yanayi na nauyin dayakeji akantaba duk da sun girmeta sosai saidai ya alaqanta hakan da kamuwar kanta da kawaicinta tareda tsananin girman datake basa.

Dan qaramin numfashi ya sauke ahankali tareda kallon agagon _patek phillippe_ dake daure a hannunsa yayi yana tunanin time na Nigeria adaidai yanzu
Ya saka Kiran Numbern tareda Kai wayar kunnensa ahankali har lokacin qafafuwansa na harde da.

*******
Abdullahi dayaga yanata Kira ba'a dagaba saiya kalli Abban cikin sanyi yace"

Ba'a daga Kiranba Amma kila zai Kira daga baya kasan irinsa Bai cika daga wayaba kowane lokaci.

Aje wayar yayi gefen Abban Yana cewa"

Bari naje nadawo kafin anjima sai asake kira.
Ficewa yayi Yana daga tasa Yar wayar da aketa Kira tun dazu daga chemist dinsa dayake aiki.

Fitarsa ba wani jimawa wayar tafara ringing
ta gefen ido Abba da yayi nisa a tunani ya kalli wayar yaga sunan TURAKI baro baro akai take zuciyarsa tahau tsalle jikinsa yahau karkarwar son adaga Masa wayar Amma Babu kowa akusa,
Hannuwansa Dake Dan motsawa suna karkarwa yafara kokarin dagawa suna rawa sosai Amma yakasa kaiwa Kan wayar bare ya iya dagawa
Haka yanaji Yana gani Kiran ya katse
Wani Kiran yakuma shigowa daga Turakin Amma Sam Abban baida halin dagawa,

Zufane ya jiqe Abban tako Ina sbd tsananin azabar kokari da tilasta kansa dayake akan daukan wayar sbd zuciyarsa datai rauni akan yarsa da batada kowa sai shi,
Hankalinsa yarigada yayi matuqar tashi akan maganar aurarda Sa'adah dazaai da abar Laylah da umma Jamila ke maganar dauka,
Dan Haka zuciyarsa Bata cikin nutsuwa ya dimauta sosai da maganganunsu Dan kuwa ko kusan karamin kisa akace umma Jamila zataiwa Laylah yasan zata iya sbd tsanar datai Masa shida Laylan bazata taba iya daukanta Dan aikiba kawai.

Yanaji Yana gani Kiran yaringa shigowa Yana katsewa Amma baya iya dauka take hawaye suka ciko idanuwansa suna gangarowa ga azabar ciwo daya taso Mata ataken sbd tilasta kansa dayayi gurin son daukan wayar Bai ankaraba sai fadowa yayi sosai daga kujerarsa zuwa qasa
Momy data fito daga palonta tana waya taji karar faduwar tasa duk da Bata tabbatarda ko shidin ne yafadin ta katse wayar tareda juyowa tana kallon kafar palon nasa kafin dai taqarasa ciki da tunanin menene ya fadin,

Ganinsa qasa zube yanata neman juya kansa cikin azaba yasata qarasowa gurin tana kai hannuwanta duka biyu ta kamasa da dukkanin qarfinta daqyar ta dorasa Kan kujerarsa idanuwanta akansa cikeda mamakin ta yanda ya Fadi saidai ganin halinda yake ciki da hawayensa dasuka kasa tsayuwa yasata kasa magana tafara gyara Masa zamansa.

Wayarsace takuma daukan wani ringing din da Dan sauran karfinsa daya rage Masa ya kalli wayar Yana bayyarda buqatarsa ta tadaukar Masa wayar Dan Allah.

Juyawa tayi ta kalli inda wayar take
take gabanta ya buga da ganin sunan Mai Kiran ta zubawa screen din wayar ido.

Hannunsa Dake rawa yafara kokarin dagawa da neman nuna yanayi magiya akan ta taimakesa ta daga Masa Kiran.

Har saaidata kusa tsinkewa takai hannu ta dauka wayar tareda receiving Kiran tana kaiwa Kan kunnensa Abdullahi na shigowa da sallama Dan Haka ta fasa ta miqawa Abdullahin wayar tareda juyawa ta fice daga palon.

Da sauri abdullahi yaqaraso gurin abban tareda Ciro earpiece ya jona a wayar ya sakawa Abban ya Dan fita Dan basa guri yayi waya Dan idan zaiyi waya da Turaki bashi guri akeyi har saisun Gama.

Akaro na farko da Momy taji zuciyarta takasa nutsuwa da wayar Abban da Turaki sai zuciyarta ke Bata Kamar akwai wani abun daban dan kuwa zaquwar Abban da yanayinsa daya bayyanarda 'dacin zuciya fiyeda kullum yasa taji tanason Jin abinda yake faruwa Dan Haka ta fasa komawa ta juyo ta dawo tana sako qafarta palon taji abinda Abban ke fada cikin kakari da kakkarwar muryarsa dake fita daqyar cikin tsananin azaba duk da likita ya hanasa takura kansa gurin mgn sosai Dan zai iya yiwa kansa illa Amma shine ya dage a hakan yake magana Dole?
Tabbas Yau tasake shaidawa da tabbarwa da Abban baya qaunarta da 'yarta tun farko shiyasa ya zabi yaci amanarta gashi ayauma tanaji da kunnuwanta ya fifita kaunar 'yarsa akan Sa'adah,
Ta Yaya zai bude Baki ya roki Turaki akan yabasa auren 'yarsa.....

Tu.raki.....akwai...alqa..wa.rin aure tsaka..nin yayana...da..naka..idan ba..ka man..taba?
Allah..Haka..yayi damu..Akan cewan...hakan...bazata...Yi..yuba...tunda.. Allah...bai...kawo....naka...rabon...na haihuwaba...
Ayau...Ina..rokonka..Alfarma ta qarshe...wadda banda...buri ko fatar data wuce wannan alfarmar....
Nasan Allah yabaka girma....da daukakanda...kafi karfin Abinda Zan rokeka sbd banbance....da dama....
Ka cika... alqawarin hada...zuria Dani daka dauka akan...hada yayanmu auren nabaka....'yata ka aureta.....wannan itace Alfarma mafi girma dazakamun da har abada...bazan daina... gode makaba....

Innalillahi wainna ilaihirrajiun" momy yafara fada cikin mutuwar tsaye da mamaki da firgici tareda zallar mamakin Abban Dan kuwa kobai Kai zancen qarsheba tasan 'yarsa daya ambata ba babbar yarsa yake nufiba 'yar Dayafi dauka 'ya ita yake nufi.

Dan Haka Bata tsaya qarasa Jin sauran zancenva ta juyo tadawo idanuwanta na rufewa cikin tsananin takaicin kanta da haryanxu taki yarda da Abban baya qaunarta tun farko shiyasa take qara haduwa da baqin ciki,
Tayaya zaiyi tunanin bawa Turaki auren yarinyarda ba itaba hatta uwarta ya girma?
Ta Yaya zaiyi tunanin bawa Turaki auren 'yar Aminiyarsa Dan kuwa akwai shaquwa sosai a tsakaninsu Kamar yanda tasamu bayani?
Tayaya zai bawa mutuminda ko manyan masu kudi ba kowa yake samun damar ko gaisawa dashiba sai daqyar bare wannan da Babu abinda yake cikin kanta bayan aiki Dan Bata gane kowane yare saina aiki bayan ga Sa'adah Nan duk da itama turakin ya haifeta amma tanada ilimin bokonda zai iya Dan nunawa duniya ita matsayin matarsa duk matarsa tafi gaban akawo macenda zata nuna Mata komai a rayuwa sai ikon ubangiji.

Daqyar qyashin da shedan ya saka Mata ya barta takai kanta dakinta duk da tsoro ma na abun yafi yawa Dan kuwa Turakin tasan Koda kalau Abban yake shi kansa yanzu Turaki saidai a waya badai ya ringa ganinsa ba
ta zauna bakin gado tana aje numfashinta dake fita daqyar daqyar.
##MAMUH#

👇👇👇Kuyi following Dina Dan samun posting akan lokaci dama sauran novels Dina complete 👇👇

Mamuhgee @Arewabooks

*_Rabo sai Mai shi...Bata taba saka ran shigowarsa ko zama jigo a rayuwarta ba sbd kallon datake Masa amatsayin Uba,Abokin mahaifinta,Amininsa Kuma Mariqi.!_*
*_Soyayyace tashiga tsakaninsu Mai girma da qarfi batareda sun ankare da hakanba bayan dukkaninsu sun haramtawa kansu hakan,Shin ta yaya zata kalla mijin yayarta,Yar uwarta wadda ta riqeta tamkar yanda uwa me riqon 'da amatsayin nata mijin TAYAYA ZATA KALLA AMININ MAHAIFINTA A MATSAYIN MIJINTA?_*
*_Qaddararsuce wannan kokuwa itace rabonsa tun farko?_*

Follow me @ArewaBooks
Mamuhgee For my latest updates

*_KUFAN WUTA_*
_Safiyya Huguma_

*_BAQAR INUWA_*
_Billyn Abdul_

*_RAYUWAR MACE_*
_Hafsat Rano_

*_MASARAUTA_*
_Miss Xoxo_

*_NOOR ALBI_*
_Mamuhgee_

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*

*KATIN MTN*

09166221261
[6/2, 11:20 PM] MG💋: *_Mamuhgee 8_*
_ArewaBooks@Mamuhgee_

Yini sukai a asibitin sai dare suka koma gida suka Bar Abdullahi
Koda suka Isa gida Momy na kwance a daki zazzabi Mai qarfi ya kwantar da ita Dan Haka cikin daren Laylah tahau wani aikin ta Dora Mata ruwan tea da maganinta na Hausa data fiye Sha takawo Mata lokacin Sa'adah na zaune gefen gadon tana Mata sannu cikin kulawa ita ta karba maganin da tea din Laylah ta juya ta fice taje ta rufe gida tadawo tayi sallar ishai da basuyiba acan asibiti tayi dakinta ta kwanta tareda rufe idanuwanta kawai.

Washe gari tunda safe tayi dukkanin ayyukanta tayi wanka ta zauna ko anty Sa'adah zatace suje asibiti sai gashi batace din ba
Momy ce kawai ta shirya ta fice zuwa asibitin Dan ji daga likitoci dake jiranta.

Lokacinda Dr Abbakar yagama yimata bayanin Abban yariga yashiga coma sai ranarda Allah yayi ikon tashinsa shiru tayi tareda qurawa Abban idanuwanta dasukai jajir
gabaki daya kamanninsa sun sauya
Oxygen ne a bakinsa Wanda yake Dan taimakawa rayuwarsa datake hannun ubangiji Dan Jan numfashin duniya,
Fuskarsa tayi haske fayau kamar Wanda babu digon jini a jikinsa
Ta sauke Kai tana Jin inama zata iya dawo da baya gaba data dawo musu da bayarsu dasuke su kadai daga ita saishi
Tabasa dukkanin kaunarta da kulawarta data Saba basa,
Bata buqatan Yan uwanta ko nasa su kadai takeson suyi rayuwa
Idanma zaiyi aure saiya fada Mata ta rarrashi zuciyarta ta dauka
Amma duk wannan bazai yiyuba sbd wannan shine asalin hukuncinta sakamakonta na bujirewa iyaye.

Duk yanda taso kasa daurewa tayi bayan fitar Dr Abbakar Saida wasu irin hawaye masu tsananin zafi da Daci suka kubuce Mata ta Sunkuyar dakai sunata gangarowa Kan fuskarta zuwa kirjinta ta rintse ido kukanta yafara fitarda sauti ahankali Mai tsima zuciya.

Ta Jima cikin wannan halin tana kuka Mai quna da radadin zuciya kafin ta danne ta share hawayenta tareda goge fuskarta ta miqe ta fice batareda tambayar kudin lalurar asibitinba sbd sanin asibitin da likitocin asibitin duk na Turaki ne Wanda takanas sbd qarin lalurar Abban ya budeta Dan Haka komai na Abban a asibitin na musamman ne ko sisi basa biya.

Gida tadawo tashige daki tashige ta lalubo nata maganin Hawan jinin tana kokarin fitowa neman ruwa saiga Laylah tashigo dakin daukeda ruwa a jug takawo Mata masu Dan sanyi ganin tadawo cikin zafin Rana da ake kwadawa.

Qurawa jug din idanuwanta dasukai jajir tayi Momy tayi tanajin idanuwan na kokarin sake cikowa da hawaye ta miqa hannu ta karba jug din da cup ta aje tana zubawa tasha maganinta batareda ta dago ta kalli fuskar Laylah dinba wadda itama tuni ta sauke Kai tareda juyawa zuciyarta na sake karyarwa da yanayin data ga momyn aciki wadda itama ta tabbatarda rayuwar kawai takeyi ba acikin Jin dadiba sbd damuwar dukkanin komai da komai ma.
Bayan fitar Laylah komawa Momy tayi ta kwanta bakin gado tareda rufe idanuwanta dasukai ja da nauyi tanajin yanda zuciyarta ke azabtar da ita.

Itama laylah kasa komawa dakinta tayi ta zauna tsakar gidan sbd rashin sanin mezatai,ga Anty Sa'adah na daki sbd yauma wani irin habo tayi Mai yawa Wanda yasata kwantawa ko zata samu damarsa Wanda take ganin zafin da ake zubawa yau dinne yasata habon jinin ta hanci duk da Bata taba yinsaba sai jiya dakuma yau dinma dayazo Mata.

Yini tayi Babu kowa daya fito daga momyn har Anty Sa'adah din
Kowa da halinda yake ciki
Itama daurewa kawai takeyi Amma tana cikin tsananin pressure da wani irin yanayi datake ji Wanda ake Kira da asalin depression Dan kuwa ko numfashi tayi Jin takeyi kamar mutuwa zatafi Mata sauki akansa,
Batada Wanda zatai magana dashi kokuma muamala dashi dazai rage Mata tsananin nauyi da zuciyarta take ciki akan halinda Abbanta take ciki.

Haka aka kwana gidan Babu motsin kowa
Washe gari ma Haka suka wuni sbd ciwon Kai Mai qarfi sosai ya kwantarda Momy
Anty Sa'adah ma da ciwon gabobi ta tashi yau din sbd kwanciyar data wuni jiyan akan nosebleed din datai Dan Haka yau gabaki daya hankalinta a juye yake Haka ta juye da aikin kulawa dasu ga tunanin abbanta Dan Haka itama sai ciwon yashigeta na zazzabi Mai qarfi sbd kasa ko cin abinci datai
Koda akai kwana biyu ahakan gabaki daya ta birkice depression yayi Mata tsanani Dan kuwa ko kalma daya Bata samu Wanda ta furtawaba
Dan kuwa anty Sa'adah sosai zazzabin ciwon gabobi ya kamata har Saida Momy taga tsananin al'amarin ta tilasatawa kanta danne nata ciwon ta tashi takai Anty Sa'adah asibitin sukabar Laylah ita kadai a gidan sai alokacin ta zauna tsakiyar dakinta tareda cusa kanta cikin qafafunta wasu hawaye datafi shekara nawa Bata zubda ba suka gangaro da idanuwanta dasukai jajir Dan kuwa ko taso kuka da dama Bata iyayi Dan baya zuwa Amma yau gabaki daya Tama rasa Yaya take,
Wane yanayi takeji,
Menene amfanin wannan rayuwar tata da Babu kowa aciki sai ita kadai da zuciyarta da tunaninta tareda quncinta.
Hawayen na gangarowa daga cikin idanuwan nata wani irin kuka yazo Mata Mara sauti ko kadan Dan ko qarfin kukan batada Dan Haka ta sulale ta kwanta agurin tana rintse idanuwanta.




A asibiti Saida suka Bata layi kafin suka samu ganin likita Dan Dan sunyi lattin zuwa,
Dunata likita yayi tareda rubuta Mata magani akan Tasha idan kwana biyu Bata warware ba zasu Mata wasu test saisu gani idan wata matsalarce babba.

Cikin ikon Allah kwana biyu tanashan maganin saigashi ta warware sosai Takoma walwalarta sai Alokacin ta lura da Sosai Laylan ta firgice kamar wadda tafara samun damuwar qwaqwalwa sai Kuma hankalinta ya tashi Dan Haka saita qi cigaba da zuwa makaranta tafara kokarin ganin ta dawo da Laylan daidai.

Asibiti ta ringa kaita gurin Abban kullum suna dubosa ko hakan zaisa tadawo daidai Amma sai hakan yake qara dagula Mata komai sbd duk ta kalla Mahaifinta ahalinda yake ciki komai sake rikice Mata yake musamman da Dr Abbakar ya tabbatar musu da Abban Yana Nan ahakan sai abunda Allah yayi kodai ya tashi kokuma daga hakan shikenan Allah ne kawai yasan abunda ya yanke akansa.

Ranar da akai musu wannan bayanin duk da anty Sa'adah tashiga wani halin itama Amma ganin halinda Laylan tashiga duk da Bata cewa kala sai hakan yayi mummunan daga Mata hankali da kuwa a bayyane tafara fahimtar depression ne yake neman juya kwakwalwar Laylah din
Haka tashiga mayuyacin halin neman mafitar tallafawa rayuwar Laylah din Dan kuwa alqawarine ta dauka zata cikawa Abba burin bawa Laylah kyakkyawar rayuwa Inshallah.

Ta bangaren Momy ganin yanda kowa yake cikin mummanan Hali na rayuwa yasa ta Amincewa umma Jamila Akan buqatar ayi auren Sa'adah ko ita zata samu ta fita daga wannan qaddarar rayuwar tasu taje gidanta tasamu rayuwar kwanciyar hankali da nutsuwarda su suka rasa ahaka suka share kusan wata biyu.

*****
Zaune suke a palon gidan Momy na zaune shiru ta zubawa Sa'adah da duk ta lalace sbd rashin kwanciyar hankali ido tanaji tsananin tausayinta Dan kuwa a yanzune ta tabbatarda son da Sa'adah kewa Laylan Mai qarfi ne Dan kuwa wani irin so taga tanai Mata tamkar Wanda uwa kewa danta,
Ta tattara karatu ta daina zuwa tsawon watan biyu ta tattara rayuwarta gurin kokarin dawo da Laylan daidai wadda yanzu bayan idanuwa datake zubawa kowa ko magana Bata iyayi Dan kamar qwaqwalwarta ta tabu gashi basuda wani kudi ko arzikin nema Mata magani sai momyn ta zubawa sarautar Allah idanuwa Dan kaf Yan uwanta tasan bazasu bada taimakonda za'a nemawa laylan lafiya ba sai itama yanayin laylan yafara tabata sbd Sa'adah da al'amarin ya taba sosai Dan hatta ayyukan gidan sun dawo Kan Sa'adah da kula da laylah wadda ba jinyar kwanciya takeba jinyar qwaqwalwa take.

Cikin 'dan zafi umma Jamila ta kalli Momy kafin ta maida kallonta Kan Sa'adah dake zaune gabansu tace"

Yanzu Zainab kina kallo Sa'adah zata lalata rayuwarta da kanta gurin kulada Mai ciwon qwaqwalwa bayan tanada rayuwa Mai kyau datake jiranta Amma ta kafe akan bazatai auren ba matuqar baza'a barta ta tafi da wannan Mai Kama da Marmaid din ba,
Ta Yaya kike tunanin za'a Kai budurwar Amarya dakinta ace anhadata tafiya da wata budurwar?
Waye mijin zai kalla a tsakaninsu?
Waye Zaifi Shiga ransa tunda kinsan ko a kyau da sigarsu ba daya ba
Waccar din kinaga daukan idone da ita duk da batada lafiya ga maza yanzu baka Basu Amana,
Gskia nidai ban amince ba
Babu inda za'a tafi da wannan yarinyar musamman yanzu datake kamar Mai ciwon qwaqwalwa..

Numfashi Momy ta sauke tana rintse idanuwanta cikin yanayi na gajiya da komai da komai na rayuwa ta bude Baki ahankali tace"

Sa'adah banida wani sanyin idaniya a yanzu bayan ke Dan Haka fatana da burina ganin kinyi aure kin samu ingantacciyar rayuwa,
Naga qaunar da kikewa Laylah nayi Miki alqawarin har abada bazan rabaku ba saidai aure Dole zai rabaku
Idan inganta rayuwarta kikeson Yi Dan ki rabata da zama Dani bayan tafiyarki namiki alqawarin barin ta tafi tayi tata rayuwar gidan nata auren Dan kuwa Abbanku ranarda ciwon Nan zai kwantar dashi Aurenta yaso badawa Dan dauketa daga gareni sbd kuna ganin nice ukubarta....

Shiru tayi wani Daci da qunci na sake mamaye zuciyarta sbd ita kadai tasan radadin datake ciki na duk abubuwan dake faruwa.

Da mamaki umma Jamila take kallonta da cewa"

Aure Kuma?
Hala dai Abdullahi zai bawa aurenta?
Amma kuwa za'a tauyesa da yawa yaron Nan
Yana fama da jinyar uban Kuma yanzu

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login