Showing 96001 words to 99000 words out of 108894 words

Chapter 33 - NOOR ALBI COMPLETE

Start ads

08 Aug 2025

39

Middle Ads

da kanta saita dauka mataki mummunan gaske akan Laylan...
Ko ahakan tabbas saisun dauka fansar wannan Cin Amanar da wannan toazarcin....

Sam Na'ima batajin zafi ciwukan Dake jikinta da fuskarta datai jajir sbd Girman Marin datasha,

Zafi zuciyarta ke Mata sosai,
Bata taba dauka abin zaizo ahakan ba sbd Koda Zinat ke fada Bata taba yarda da hakan zai tabbataba LAYLAH DA CIKIN TURAKINTA ajikinta,
Abokin mahaifinta, mijin Yar uwarta hakama mijinta ita uwar datai Mata riqon da Matar ubanta batai Mataba...

Yanda Na'iman ke kuka sosai ya Kuma tada hankalin Zinat jikinta duk yabi ya mutu sbd a fili yake bayyane alamarin daki Na'iman sosai sbd Bata taba kawo hakan zai faruba.


Daqyar allurar ta sanyata baccin qarfi da yaji tanayi tana fizga kadan kadan Kuma badan idonta ya daina tsiyayar hawaye ba.

Fitowa Palo Haj Zinat tayi ta zauna tareda Shiga tunanin mafita dakuma yanda zasuyi ta tafi da Na'ima gidanta su samu zuwa ganin likitanta Dan wannan karon abun yayi nisa saisun hada da ganinsa
Daf Na'ima take da bayyanarda haukarta afili asani...

Daga lokacinda Turaki yasani ta tabbata ko ganin Na'iman bazai Bari kowa yasake yiba sai ya nemar Mata lafiya,
Itakuma idan tabari ta warke sarai yanzu suna cikin gagarumar matsala sbd ba kudi a hannunsu sosai,
Komai nasu yayi qasa sbd wainnan fitintinun dasuketa faruwa
Komai tsaya Mata zaiyi.
##MAMUH#
[7/2, 3:32 PM] MG💋: *_Mamuhgee 52_*
A gidan zinat ta wuni tana saqa da warwara,
Ga Na'iman cikin baccin sai Dan fizgawa takeyi lokaci lokaci,
Kanta ya dauka zafi sosai ita kanta yanzu komai ya tsaya cikin kanta,

Na'iman takeson fara dawowa da ita saiti kafin tafara tunanin abin Yi akan Laylah tun kafin afara Ankara da halinda suke ciki.

Sai dare tabar gidan bayan tabawa siddika kyakkwan gargadi akan kula da Na'iman karta Bari ta fita idan ta farka.


*****Laylah ma a daki tayi wunin ranar idanuwanta sun kumbura iya qarshe sbd kukan datasha,
Gabaki daya kewa da kadaicin rayuwa takeji gashi ta kashe wayarta sbd Kiran da Abban keyi Mata cikin damuwar halinda take ciki sbd yakasa yarda da lafiyarta kalau...

Abinci ma kasa ci tayi Haka ta wuni cikin damuwa,
Gab da magriba Anne tadawo ta tadda wannan tashin hankalin sbd zazzabin gaske daya sauka ya rufe Laylah Dake dunqule a daki jikinta na rawa.

Fada sosai Anne taringa Yi Akan su halima Basu kirataba sun sanar da ita abun dayake faruwa ta dawo..

Ba Bata lokaci ko zama bataiba ta Kira dr Meenah tace ta taimaka tadawo tasake duba musu laylan.

Koda Dr Meenah ta iso da daddare jikin Laylan yayi tsanani sosai da zazzabin,

Magani aka Bata tareda tea Mara zafi Sosai
Dr Meenah na tafiya ta ringa zuba Amai a gabaice.

Damuwa sosai Anne tashiga ta Kira Turakin a waya ta sanar dashi yace a a shirya Laylan ta fito zasuje suga wani likitan.

Da Taimakon Ruky ta shirya suka fito ta kaita har jikin motar dayake zaune Yana jiranta da kansa zai ja motar Wanda rabonsa da driving bama zai iya tunawaba.

Dr Dawood sukaje ya dubata daqyau harda scanning yayi Mata ya tabbatar musu da lafiyan babyn kalau
Bp dintane kawai ya hau sai zazzabin sosai dayake damunta da rashin qarfin jiki na galabaitan datai.

Maganin bp na masu ciki yabata Suka fito Yana riqeda hannunta Suka dawo gida.

Yanayin da ake cikine kawai yasa yabarta Takoma bangaren Amma yanajin yanayinta a zuciyansa.


A Daren kusan dukkaninsu kowa kwanan damuwa yayi sbd Babu Mai cikakken dadin zuciya..

Washe gari tasamu saukin jikinta sosai saidai gabaki daya tashiga damuwa da sanyin jiki
Babu abunda takeso bayan zuwa gida ko zata samu kwanciyar hankali kafin tadawo idan mum ta sauko sbd tasan mum bazata taba Bari ahaka ba sai tayita kokarin Daukan mataki akanta shiyasa gabaki daya take cikin sanyin jiki da damuwa..


Qarfe goma na safe Anne ta nufa Sashen Na'ima sbd dubota dakuma magana da ita sbd tasan wannan Shirun nata bayan abinda yafaru bana lafiya bane.

Siddika ce ta tarba Annen cikin tsananin girmamawa tareda sanar da ita Ms Na'iman tana bacci magani Tasha sbd ciwon Kan data kwana dashi.

Kallonta Anne tayi cikin jinjina Kai tace"

Idan ta farka kizo ki Sanar Dani Zan dawo na dubata nakuma Yi magana da ita,
Allah ya sawwaqa yabata lafiya.

Amin" Siddika tace tana kokarin bawa Annen Hanya sosai ta wucewa.


Shigowar Haj Zinat yasa Annen dan dakatawa tana kallonta.

Cikin tsananin girmamawa Haj Zinat ta qaraso tana gaida Annen cikeda biyayya tana qarawa da cewa"

Na'iman ta tashi ne?

Aa Bata tashiba ance Bata jima da komawa bacci ba Tasha magani ne,

Cikin nutsuwa da bayyanarda Mahimmancin maganar da zatai da Na'ima idan ta farka Anne tace"

Zinat ki kula da Aminiyar taki sbd nasan halinta da zafi da fitina,
Tabbas akwai rashin kyautawa aciki Amma Kuma yanayin ne duk yazo ahakan sbd Babu Wanda yayi niyar cutatar da ita ko boye Mata komai,
Tun farko itace ta kawowa kanta rashin tsayawa fahimta,..

Turaki Bai boye Mata qarin aurensa ba, nikaina ban boye Mata ba saidai Kuma itace da kanta ta zabarwa kanta waye kishiyar tata
sbd azauna lafiya yasa ba'a sanar Mata ba Dan Babu Wanda ya dauka auren Mai dorewa ne tun farko
Saidai Kuma kaddara da rabo na ubangiji ba'a tsere musu,

Laifi dai anyi Mata na rashin fadar Dan Haka nakeson rarrashinta nabata hakuri duk wannan tashin hankalin zata sakawa kanta damuwane tunda bawa baya wuce qaddararsa....

Laylah Allah yayi dai Matar Turaki ce Kuma uwar yayansa........ Dan Allah kifara tausarta kafin nadawo
Ki Bata hakuri sosai sbd mum Mata laifi mun yarda Amma Inshallah za'a gyara komai....

Mutuwar tsaye Zinat tayi zuciyarta na neman Faso kirjinta tafado tsabar shiga tashin hankali da rudu
Amma dayake gwanace gurin riqe kanta sai Bata bayyanarba ta jinjina kai kawai sbd bazata iya magana ba bakinta rawa yake.

Anne na fita tayi wurgi da Jakarta da keys din motarta tareda dankwalin kanta tanajin kaman zata Ara hauka akaron farko.....

Wane mugun labari ne wannan takeji abakin Anne?

Kallon siddika tayi cikin tsananin tashin hankali tace"

Daidai naji Anne tace Laylah ce Matar Turaki???

Da sauri siddika ta gyada Kai cikin nata zallan mamakin da firgici Dan sai yanzu take sake tabbarda akwai masifa a kwance kenan idan Ms Na'ima ta tashi ta samu wannan sabon zancen.

Zama Zinat tayi tana fifita fuskarta da hannunta Dan wani zafi taji tanaji
Cikin shiga rudin tunani tace"

Tabbas Basu fada Mana cewan Sa'adah Matar Turaki shiyasa shegu tsinannu suka bar Na'iman ta tafi da Laylah wato takai Masa matarsa har gidansa......

Tun farko wane Dan burauban shegen ne Yafada Mana Sa'adahn ce Matar Turaki????" Tafada tana dago da jajayen Idanuwanta ta Dora Kan Siddika da jikinta yafara rawa tana neman zancen fidda Kai tana kokarin magana Zinat ta sauke Mata wasu kyawawan Marika guda biyu tana fizgota tace"

Dama bakida sani akai Kika kawo Mana wannan zancen kokuwa da gayya kikace Mana Sa'adahn ce?

Cikin azabar Marin datasha tafara rarraba Ido tana hawayen tsoro sbd komai zasu iya Mata tunda tafi kowa saninsu ba Imani ne dasuba musamman Haj Zinat din tunda har Ms Na'iman itake fada Mata yanda za'ayi komai.

Dukan fita hayyaci Zinat ta ringa yiwa siddikan tana cewa"

Kece Kika lalatamun komai da shirina na shekaru Dana Jima Ina fafutaka akansa,
Matsiyaci wlh zanyi lokacinki idan nagama da Laylan da Na'iman tukuna..

Tattarawa tayi tabar gidan sbd zata iya kashe siddikan idan Bata bar inda take ganintaba,

Sabon tashin hankali tashiga na musamman sbd na farkon duk Mai saukine a daukansu cikin shege ne jikin Laylan ba Turaki Dan Haka komai zaizo da sauki,
Amma Jin Laylah Matar Turaki ce yasata Shiga matsananciyar tashin hankali sbd Dan halak ne wato zata Haifa masa,

Magajinsa fa kenan??

Magajin dukiyar dasuka Dade suna shirka akanta Dan su mallaketa koba dukaba su mallaka Rabin,

Magajin dukiyar da akanta taketa durawa qawarta dasuka taso tare tun yarinta maganin data juyar Mata da qwaqwalwa ita ke controlling dinta....

Amma ace Rana tsaka wata qanqanuwar yarinya ta samesu daga sama Bayan tagama lalata mata komai na wargaza gashi sanadin hakan Turaki zai iya gano halinda Na'iman take ciki Wanda Yana ganowa tasan labarinta yaqare daga Nan Kuma...

Wlh bazata yardaba,
Komai zata iyayi dan ta tsira,

Yanzu babban burinta ta fito da Na'ima daga gidan,
Sbd sai Na'iman Bata gidan zata samu damar kawar da Laylah da cikinta daga duniya Kai tsaye sai laifin ya rataya Kan Na'iman wadda ita Kuma takardun shedar haukanta zaisa hukunci bazai hau kantaba
Dan Haka duk tsanani saita fidda Na'ima daga gidan
Kuma zata fiddatane daga gidan ta hanyar da Laylah zata daga hankalinta itama ta fito daga gidan.


Washe gari da gangan tana sane taqi zuwa gidan sai dare tazo
Lokacin Na'ima ta farka Amma Bata iya komai sai Ido datake Binsu dashi Haka ta sake sakarwa Na'iman wata allurar data sake maidata halinda ta fito idanuwanta suka rufe Takoma baccin wahala.

Fitowa dakin tayi siddika na biye da ita Saida suka zo palon ta kalli siddikan cikin bayyanarda Mahimmancin aikin da zata sakata ta kalleta tace"

Aiki Mai mahimmanci Zan sakaki
Idan Kika Bata mun aiki wannan karon Wlh yanda na maida Na'ima fin hakan Zan maida rayuwarki,kina Jina????

Gyada Kai tayi tana cewa"

Zan kiyaye Wannan karon.

Ciro qaramar kwalba daga jakar hannunta tayi tareda qaramar lighter ta miqa mata..

Karba siddikan tayi tana bude idonta akan kwalban da warin fetir ke tashi acikinta
Ta hadiye wani mugun yawu tana kallon kwalban da lighter din cikin rawar murya tace"

Wannan fetur.....

Katseta tayi da cewa"

Nafiki sani tunda nice nabaki,

Anjima da daddare ki zuba a akan gadon Na'ima Kuma ki zuba Mata kadan a jiki saiki janyota ki fito da ita daga bakin kofar dakin ki kunnawa dakin wuta,

Karki Kira jama'a sai wutar taci sosai Kuma ki tabbatarda ta shaqa hayaqin wutar saiki fita ki Nemo jama'a,

Kafin akirani idan antambayeki garin Yaya kice itace ta kunnawa dakin wuta da kanta tana cewa kunnawa gidan wuta zatai kowa ya mutu har Laylah.

Tsananin tsoro da mamakin girman rashin Imanin Zinat din da zata cutatarda Ms Na'ima sbd son abun duniya..

Cikin sake bayyanarda zata iya Mata abinda tace zatai Mata idan ta Bata Mata aiki tace"

Idan Kika aikata kuskure daya komai ya lalace wlh ke Zan cinnawa wuta kifara Isa lahiran kafin muzo.

Wucewa tayi tabar siddikan tsaye tana binta da kallon mummunan tsoro da tashin hankali...

Kasa zuwa kitchen tayi da fetir din ta nufi dakin Ms Na'iman dashi ta boye bayan Kan gadonta tana kallon fuskarta...

Akaro na farko da Tausayin Ms Na'iman ya ratsata sbd batada Mai qaunarta bare yabata shawara,

Tayi watsi da qanwar mahaifiyarta data riqeta sbd samun duniya a hannu gashi yanzu tazo tana neman Rasa komai...

Duk da Ms Na'ima Bata kyautata Mata saima izza da bossing dinta datake koyaushe Amma Bai kamata a cutatar da ita hakaba abun yayi yawa bayan arzikin dasuke ci suna Tarawa daga Haj Zinat din har ita duk qarsqashin Ms Na'iman suke samunsa...

Itadai gaskia bazata yarda tayi biyu babuba wlh ta koma rayuwar wahalar data fito,
Dan gwara Mata wulaqanci da masifa harma da bala'in Ms Na'ima akan barin gidan AB TURAKI Dan Haka Dole zatasan yanda zatai bada saninsuba ta bayyanarwa da Anne ko Turakin lalurar da Ms Na'ima take dauke da ita ko za'a rabata da Zinat a cetota tasamu taci gaba da cin arzikinta lfy kafin Zinat din ta wargaza musu Suma komai.


Ba yanda ta iya da daddare Haka ta cinnawa dakin wuta
Aikuwa wuta Mai qarfi ta tashi wadda batama tsammata ba
Tsoro ya kamata ta fito da gudu tunda wuri ta nema jama'a sbd wutar kamar jiratake a kunna koina yafara dauka.



Hankali tashe securities da kowa gidan ya fito,
Anne na dakin Laylah a Daren sbd wani zazzabin datake fama dashi na damuwar Dole data sakawa kanta,
Gashi taqi yadda ko ganin juna suyi da Abban nata sai zaman boyo take a daki duk ta Hana kanta sukunin zuciya shima ta hanasa sbd rashin ganinta yafi komai daga hankalinsa ita kanta rashin ganin nasa ne yaketa nukurkusanta.

Jin hayaniya na tashi a gidan yasa Anne miqewa daga zaunen datake tana bawa Laylah tea abaki tana Sha jiki amace.

Fitowa Palo Anne tayi tana cewa"

Halima lafiya gidan Nan kuwa nakejin hayaniya?

Wutace ta tashi Anne a bangaren Ms Na'ima sosai Kuma wlh..

Subhanallh innalillahi, yanzu?
Ina Na'iman?
Bata ciki dai ko???

Fita tayi da sauri tana faman nanata tambayar Allah yasa Na'iman Bata ciki.

Siddika ce kawai a waje takasa komawa jiki jikinta sai rawa yake hankalinta ya tashi Bata dauka wutar zata juye ta zama hakanba..


Koda Turaki ya fito gurin cikin sauri ya qaraso Yana tambayar Ina Na'ima?

Cikin tsananin kuka da firgici siddika tace tana ciki... Aikuwa Bai tsaya Gama ji ba ya nufa kofar ya shige...

Anne da sauran maaikatan gidan da securities suka fara ihun Kiran sunansa....

Anne da sauri ta bisa zata kamo halima ta riqeta ta hanata shiga....

Ihun Kiran sunan Turakin da ake yasa Laylah fitowa Bata ko ganin gabanta sosai jikinta har rawa yake ta kallesu cikin yanayinda muryarta Bata ko fita sosai ta bude Baki zatai magana sai gashi yafito daukeda Na'iman data Gama shaqar hayaqin harta fita hayyacinta da sauri ya nufa mota da ita Yana cewa A Abdoul daya iso ya bude mota da Sauri.

Shigewa motar yayi Suka nufa asibiti
Suna fita motar kashe wuta na isowa aka fara kashe wutar.

Anne jininta ya Riga ya hau Dan Haka Dole Saida aka kamata aka maidata ciki
Laylah ma daqyar ta maida kanta ciki suka kwantar da Anne bayan anbata maganin Hawan jininta ta kwanta itama ta nufi daki ta zauna sbd bacci kam ya Riga ya qauracewa idanuwanta,
Zazzabin datake ji ma take taji yasake,
Gabaki daya hankalinta ya tashi Kuma sbd koma menene tasan wanna wutar tanada alaqa da abinda yake faruwa..
Gida takeson zuwa kowa yasamu damar samun nutsuwa.
##MAMUH#
[7/4, 8:58 AM] MG💋: *_Mamuhgee 53_*
Suna Isa asibiti aka karbi Ms Na'ima aka karbeta tareda shigewa emergency da ita sbd ta shaqa hayaqin sosai gashi har lokacin Allurar da akai Mata Bai saketaba jikinta a mace yake Sosai fuskarta da jikinta sunyi duhun hayaqi daya Bata jikinta.,

Zama Turakin yayi a office din Dr faruk daya bude Masa Dan ya zauna anan,
Sai alokacin ya sauke numfashi tareda kallon A Abdoul daya shigo office din da wayarsa a hannu sbd shi yabaro tasa wayar.

Kai tsaye A Abdoul wayar Anne yafara Kira dan sanar dasu Inshallah komai yafara daidaita tunda anshiga da Na'iman gashi dama ba konewa tayiba kawai dai hayaqin ne yashiga cikinta.

Wayar Annen Bata shiga Dan Haka saiya kalla Turakin a hankali ya sanar Masa.

Gyada Kai kawai yayi hankalinsa na rabuwa biyu kowanne da damuwa,

Laylah yakeji wadda ya tabbatarda hankalinta ya tashi Sosai ga yanayinta
Sam baya son abinda yake daga hankalinta gashi ba waya bare ya kirata,
Wayar A Abdoul bazataiji wani dadin wayar da itaba Dan Haka zai hakura harya koma gidan...

Bangare daya Kuma Na'iman ce da matsalolinta,

Tashin hankalin kishinta yayi yawa,
Sam takasa saduda akan lamarin gashi tana neman halaka kanta sbd tunanin banza,

Sam yakasa gane ace Mai cikakken hankali ne zai cinnawa kansa wuta sbd kishi,
To idan ta mutu ai tayi abanza kenan tunda Wanda take kishin tabarsa da wadda take kishin itama,Dan Haka gskia lamarin nata yayi Muni..
Tana warkewa zai maidata Lagos idan Kuma Nan takeso LAYLAH na haihuwa zata koma US ita tabar Mata Nan.

Sai Asuba Ms Na'iman ta dawo daidai bacci Mai nauyin gaske ya dauketa
Suna kokarin baro asibitin Haj Zinat ta iso cikin tsananin firgici da tashin hankali tana ganin Na'iman tafara kuka tana riqe hannunta.

Ganin zuwanta yasa Turakin samun saukin barin Na'iman tareda siddika Dan Haka ya wuce yabarsu agurinta.

Yana tafiya Haj Zinat kallo daya kawai tayiwa siddika datake firgice har lokacin ta Dan jinjina Mata Kai.

Siddika dai Bata samu damar cewa komaiba sbd hankalinta bai gama dawowa jikintaba,
Saura kadan yau tayi kisan Rai takeji,
Meya kaita wannan aikin rashin Imanin akan kwadayi?
Yanzu da Ms Na'ima ta mutu koda ba'a ganesu ba tasan wlh shikenan haukacewa zatai nauyin Rai data kashe bazai bar qwaqwalwartaba.

Hawaye ne Suka ciko idanuwanta jikinta na sake daukan rawa Amma Ta hadiyesu sbd Kar Haj Zinat tagani tasan zuciyarta ta raunana ta illatata gudun kawo Mata matsala,Dan hak ta hadiyesu tareda maidasu suka koma tana kokarin nutsar da kanta.



****Washe gari tunda safe Anne da kanta ta shirya gurin tafiyarwa dasu Na'iman breakfast Wanda su halima suka hada tunda safiyar Dan akai asibitin.,

Sai data duba Laylah Dake kwance tana bacci ta shafa kanta ahankali cikin kulawa da kauna sbd tasan Laylan Bata cikin kwanciyar hankali na wannan abun daya faru kafin ta juya ta fice Suka wuce asibitin itada halima aka bar Ruky sbd Laylah.


Cikin bacci taji qamshinsa na shigar Mata hanci
Ta dan motsa Ahankali tareda Jan numfashin kadan hancinta yasake shaqar numfashin ta bude idanuwanta ahankali tareda saukewa akan fuskarsa..

Zaunen yake bakin gadon Yana kallonta cikin nutsuwa da tsananin sonta dayake bayyane akan fuskarsa da yanayin kallon dayake Mata.

Ajiyar zuciya ta sauke ahankali tareda lumshe ido ta bude ta kallesa hawaye na ciko idanuwanta na kewansa dama kewan kwanciyan hankalinsu ta bude Baki muryarta na rawar son yin kuka tace"

Abbah.

Lumshe fararen nasa idon yayi shima sbd yayi kewan Jin sunan abakinta Dan Haka yakai hannu ahankali ya Kama hannunta ya tayar da ita zaune ajikinsa hannuwansu sarke da juna.

Kallonta yayi cikin kulawa da azabtar da zuciyarsa keyi akan rashin ganinta da jinta ya shafa fuskarta tareda taba cikinta dage gabansa cikin muryarsa data kashe jikinta da sonsa yace"

Lafiyanki kalau kuwa??

Gyada Kai tayi tana kwantar da kanta jikinta ta zura hannuwanta ta rumgumesa tana rufe Ido.

Babyn fa?
Ba damuwan komai right?

Sake gyada Kai tayi Ahankali kafin bude Baki cikin sautin kulawa tace"

We miss you Abbahh.

Hannunta yakai bakinsa yayi kissing ahankali kafin ya shafa fuskarta ahankali Yana cewa"

I love you.

Ajiyar zuciya ta sake ahankali tareda sake lafewa jikinsa,
Sun Jima a hakan Saida kowannensu yasamu nutsuwar zuciya data ruhi kafin ta dago da idonta ta kallesa A natse tace"

Yaya jikin Mum?
Hope bata samu rauni ko matsalaba a koina?

Jinjina Mata Kai kawai yayi Ahankali Yana cewa"

Ba matsalar komai bane hayaqin ne yaso yayi Mata illa Amma tana lafiya.

Ajiyar zuciya ta sauke tareda tasowa daga jikinsa ta zauna daidai ta sauke Kai ahankali tareda sake riqe hannunsa Dake cikin nata murya a Sanyaye tace"

Abbah please kabarni naje gida.¿
Mum na buqatan abata space tayi digesting wannan abun,
Ranta ya baci Sosai sbd yanda abun yazo Mata nakuma fahimci Jin zafinta sbd yanda nakejin zafin kishinka na tabbatarda idan nice mutuwa zanyi Abbah idan ka tafi gurin wata,
Dan Haka mum na buqatan abarta abata guri da lokaci ta Gama daukan dumin abin kafin ta sauko...

Dan Allah kabarni naje gida Nima zanfi samun nutsuwa kwana biyu..
Please Abbah.

Girgiza Mata Kai yayi Kai tsaye

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login