Showing 105001 words to 108000 words out of 108894 words

Chapter 36 - NOOR ALBI COMPLETE

Start ads

08 Aug 2025

41

Middle Ads

sallar isha baccin Dole ya dauketa sbd cikin maganin da aka Bata hardana bacci sbd yanayin datake ciki duk tabi takasa samun nutsuwa.




********Qarfe biyu da mintuna ashirin cif na dare baqar motar Honda ta Parker bayan gidansu Abban daga nesa.

Haj Zinat ce zaune aciki tareda Na'ima data Gama bankawa wasu irin mahaukatan qwayoyi masu qarfin gaske dasuka qarasa buga qwaqwalwar Ms Na'ima gabaki daya sai abinda Allah ya rage..

Tana cikin motar zaune yaran datazo dasu Suka fita Suka tunkari gidan.

Babbar katangace kewaye da gidan gakuma security electric wire Dake zagaye da katangar Amma Haka Suka zagayafa suka fara disconnecting CCTV cameras Dake zagaye da bayan gidan kafin suka kame katangar Suka fada gidan sbd qwararrine a harkar na karshe.

Mintuna kusan goma Sha shiga da fadawarsu gidan wuta ta tashi take koina tafara ci Kuma tako Ina.

Masu gadin gidan guda biyu Koda suka Ankara Suka firfito tuni wutar takama sosai Tako ba halin tunkarar ciki Dan Haka Suka fito waje suna neman daukin jama'a a fito.

Yanda wutar ke ci sosaine yasa jamaar dasuka fara firfitowa ihun neman agaji da taimako.

Momy da Allah yasa tanada rabon fitowa Daren a gurin Abba ta kwana sbd tashiga quncin da Bata taba Jin zuciyarta tashigaba a ranar,
Maganganun Yan uwanta sun Kama sakata cikin tsananin dacin zuciya da kunci Wanda yasa Abba da kansa ya kirata dakinsa ya zaunar da ita tareda qasqantar da kansa yabata hakuri sbd koma menene shine suke ganin ya cutatar da momyn.

Yanda ya qasqantar da kansa yakuma Bata zabin idan shine matsalarta da baqin cikinta idan tanaso zai sauwake Mata taje ta shirya da Yan uwanta idan tanaso.

Kalmarsa tasata sake Shiga mawuyacin halinda yakaisu ga shiryawa a Daren harma ya sauke Mata haqqinta na aure da sukafi shekaru masu yawa Basu samuba.

Wutar zafi da tsananin hayaqi ya sanya Abban fara farkawa yaga wutace takeci harta fara shigowa dakin dasuke sosai.

Tayarda Momy yayi yace tayi maza idata keda lafiyayyan kafafu ta fita takira su Sa'adah su fito.

Gigice Momy ta tashi tana tarin hayaqin daya fara fin karfinsu tana kokarin kamasa su fita ko Babu kujerarsa tunda Amma yayi Mata nauyi Dan haka yace ta sakesa taje ta dubo su Sa'adah idan wutar batakai can ba.

Kasa tafiya tayi tabarshi Dan Haka tafara jansa cikin wutar cikin tsananin azaba wutar Dake cinsa din suna kaiwa kofa ya turata waje da sauran qarfinsa daya rage.

Kokarin dawowa takeyi Amma wutar taci karfi ita kanta take kanta yafara juyawa sbd haqayqi da zafi Bata gani batansan inda kanta yakeba Haka taita jefa qafa har wutar taci karfinta ta Fadi a inda take.


Wuta Kam sosai takecin gida tako Ina ba damar Shiga ceto sbd tagama mamaye koina na gidan...

Kallon Ms Na'ima Zinat tayi bayan tasake wani mamalacin murmushin kawarda matsalar Laylah a rayuwarsu tace"

Na'ima kinga ga wutar gidansu Laylah can tanaci suna konewa jeki ki tabbatarwa idonki.

Bude mota tayi tareda janyo Na'iman ta fito Kai Tsaye kuwa ta nufi gidan ta wuce jama'a tana cewa"

LAYLAH Kinga sakamakon cin Amanar da kukaimin Nan....
Turaki nawa ne Ni daya bazai taba zama nakiba kije lahiranki ke daya.....

Kallonta jama'a Suka fara cikeda son tabbatarda abinda take fada sbd kuwa idan itace jefata zasuyi a wutar kafin fireservice sugama kashe wutar....

Juyawa tayi tabar gurin da sauri kamar yanda Zinat ta sanar da ita karta Bari a kamata aikuwa tana zuwa da gudu ta fada motar suka ja sukabar gurin,

Murmushi Haj Zinat tayi sbd dama burinta da amfanin tura Na'iman sbd aganta asamu shaidar itace ta kunnawa gidan wuta,
Itace tayi kisan kenan Kuma takardunta na hauka bazata taba bayyanardasuba sbd kafin agano Na'iman batada lafiya ta Jima a gidan yari ko lahira shikenan ta rufe babin Turaki da matansa duka,
Dukiyar Na'iman dama tajima da zama tata, batada sauran wata matsala a rayuwar Kuma.
##MAMUH#
[7/5, 2:09 AM] MG💋: *_Mamuhgee 56_*
Cikin bacci Kiran A Abdoul yashigo wayarsa,
Baya kwana da waya a kunne Amma ranar mantuwa ta sanyashi kwana da wayar a kunne.

Dayake baccinsa baiyi karfiba sbd Laylan daketa firgita cikin bacci gabaki daya ta kasa kwantar da hankalinta Kan abunda yafaru..

Daukan wayar yayi da mamakin ganin Kiran karfe hudu saura na dare.

Cikin tashin hankali da firgici duk da Yana kokarin controlling kansa Amma yakasa akaro na farko daya fasa kuka arayuwarsa gaban Turakin yace"

Turaki wutan gobara ya tashi a gidansu Sa'adah,
Abbansu da Sa'adah da sauran masu aikin duk sun.... Kasa qarasawa yayi sbd kuka Mai qarfin gaske dayake Yi.....

Da sauri Turakin ya miqe Yana zare Laylah daga jikinsa ya sauka daga Kan gadon Yana cewa"

Innalillahi wainna ilaihirrajiun,
Innalillahi,
Ganinan zuwa yanzu,
Masu kashe wutan sunzo?
Dan Allah ayi gaggawar fidda kowa daga gidan ganinan zuwa yanzu.

Jallabiya fara qal ya janyo ya saka Yana kokarin daukan keys ya fice Laylah Dake kwance tana jinsa ta tashi zaune gabaki daya jikinta yagama mutuwa ta kallesa daqyar ta iya hada kalmar"

Gidansu Abbane yakamata da wutan?

Dakatawa yayi batareda ya waiwayo ba yace"

Ki jira zanje na dubo.

Ficewa yayi yabarta zaune takasa ko qwaqwaran motsi sbd jikinta yagama Bata gidansune gobarar,
Wanna quncin dataketa faman ji tun safiyar ranar na wani abun ne kila zai samesu.

Yaye rufarta tayi tareda zuro qafafunta ta sauko dasu qasa ta miqe tsaye ahankali sbd bayanta dayake riqewa.

Kujera ta nema ta zauna tareda qurawa kofa Ido tana sake Shiga tsoro da fargaba.



Ko daya Isa hankali tashe wutar saura kadan agama kashewa gashi har anafar Kiran sallar fari a wasu masallatan,
Cikin tsananin tashin hankali da firgici daya Shiga shima yake tambayar Ina mutanen Dake gidan...

Momy da Abba da aka samu damar fitarwa da sauran Rai kawai aka nuna Masa sauran kuwa Babu Wanda Allah yayi zai fita wutar.

Wani mummanan jiri ne ya debesa aka taso za'a riqesa ya dafa motar Dake bayansa Yana cewa"

Innalillahi wainna ilaihirrajiun
Innalillahi wainna ilaihirrajiun

Ana Gama kashe wutar ba'a samu damar fidda gawar jamaar gidanba saida gari yayi haske sosai aka jeresu su uku.

Momy da Abba sun kone sosai ta yanda gabaki dayansu sun sabule musamman Abba har gwara momyn,

Daukarsu su tun kafin sallar asubar aka nufi asibiti dasu cikin gaggawa.

Sauran gawarsu Sa'adah ma asibitin aka nufa dasu.

Halinda A Abdoul yake ciki yasa hankalin Turaki sake tashi sbd Laylah komai itama zai iya faruwa da ita tana samun wannan mummunan labarin.

Haka yadawo jikinsa Babu inda baya rawa da tashin hankalin al'amarin...

Yana shigowa tana zaune inda take sallah kawai ta iyayi daqyar tadawo ta zauna tana jiran tsammanin dawowarsa.

Kallo daya tayi Masa ta sauke Kai sbd wata Ajiyar zuciya data tsinke mata batareda tasan Kota mececeba.

Qarasowa yayi ya wuceta yashige toilet yayo wanka sbd kayan jikinsa dasuka naci.

Bayan yafito Babu Wanda yayi magana acikinsu Saida ya shirya ciki suturarsa kafin ya zauna ya kalleta cikeda tsananin tausayinta da sonta,

Baya kaunar dagula zuciyarta da wannan mummunan labarin Amma Kuma Dole za'a a sanar Mata Dan Haka tea tafara Bata ta karba n
Ba musu ta Sha rabi ta aje cup din.

Magani ya sauka ya Bata shima ba musu ta karba ta shanye.

Kallonta yayi cikin kulawa da nutsuwa Yana Kuma kamo hannunta ya riqe Gam cikin nasa yace"

Qaddarar gobarace ta fadawa gidan acikin daren Amma....

Dan shiru yayi Yana jinjina girman munin labarin yace"

Kiyi hakaru ZAINAB bawa baya wuce kwanakin da ubangiji ya dibar Masa.....

Bata motsaba har lokacin idanuwanta na Kan bakinsa sbd tariga da tagama qulle zuciyarta cikin wani Hali na tsananin qunci ahankali ta bude Bakinta daya bushe Nan take tace"

Abbana ne ya rasu?????

Girgiza Mata Kai yayi yana kokarin janyota ya rungume cikin bayyanarda tsananin alhinin wannan tashin datayi gana 'yayan mutane dasuka kone daga zuwa aiki murya a karye yace"

Abbanki na asibiti tareda Zainab....

Wani mummanan faduwar gabe ya risketa ta janye jikinta cikin mummunan yanayi da rawar da jikinta yafara dauka tace"

Anty Sa'adah ma na asibitin????

Girgiza Mata Kai yayi Kai tsaye yana cewa"

Kiyi hakuri Zainab
Sa'adah Allah ya karba ranta....

Kafin halinda take Shirin Shiga tashiga wani mummanan ciwon marane yataso Mata gadan gadan cikin tsananin azaba da tashin hankali..

Cikin sauri ya riqota Yana Kiran sunta Amma Ina ciwon nakuda ya taso Mata Kai tsaye ba shiri Kuma lokaci baiyiba.

Cikin gaggawa da wani sabon tashin hankalin akayo asibitin da ita itama
Suna dubawa kuwa Suka tabbatarda nakuda ce bakwaini zata Haifa.

Hankalin Turaki Bai taba tashi irin na ranarba sbd ganin bayan duk wannan abubuwan da rashin rayukan da akai ga Kuma nakudarta alokacinda ake cewa cikin Bai Isa haihuwa.

Koda su Anne Suka iso garin hankali tashe tuni Laylan ta haifi jaririyar 'yarta Yar qarama da ita ansaka cikin kwalban aje yara irinta.

Laylah tasha matuqar wahala sosai gurin haihuwa duk da hakan tana haihuwa abin data fara shine sakin wani tsimammen kuka Mai taba zuciya na rashin Yar uwarta Rabin jikinta datayi,

Kuka takeyi sosai wanda tasaka harsu Annen kuka dasuma dama da kukan rashin Sa'adah sukazo,
Halima tayi kuka har idonta Baya budewa sosai.

A gidan umma Jamila data ringa Suma tana farfadowa Kan rashin Sa'adah da halinda Momy ke ciki akayi jana'izarsu aka kaisu makwancinsu take Kuma aka watse sbd Babu zaman gaisuwar dasu Anne zasuyi.

Iyayen hadiza dasuka zo suma anjaajanta musu wannan babban rashin kafin akayi musu duk wani Abu da akasan ya kamata ayin.

LAYLAH takasa kwantar da hankalinta sbd tasakawa ranta damuwa da qunci sosai.
Halima ma kukan rashin Sa'adah itama bazata iya barinsa yanzuba sbd sunyi wani irin shaquwa da sabo.

A Abdoul ko mahaifiyarsa datazo gaisuwa ta tausaya Masa sosai sbd Allah yasani tasa irin kaunar daukewa juna Kuma ita kanta ta yaba da nutsuwar Sa'adahn.

Anne taso kebewa ta sanarda Turaki maganar Laylah da aka gama tabbatarda itace ta bankadawa gidan wuta Amma ganin yanda komai yake neman cakudewa na halinda Laylah take ciki yasa ta dakata tareda fara Shirin komawarsu duka abuja hardasu Abban da Momy da za'a fitar waje Amma saisun fara Dan samun sauki tukuna.

Suna sauka Abuja daga airport motar asibiti aka dauki su Abba da momy aka wuce dasu
Sukuma da motar gidan Suka tafi Suma asibitin Suka nufa direct aka Kai baby aka Kuma admitting dinta.

Suna Isa gida Babu sauran Bata lokaci Anne ta gabatarwa da Turakin bayanin komai da komai sbd ganin yanda yariga yahau sosai akan tabbacin dasuka samu na Na'ima ce ta tada gobarar sbd wanna karon tabbas zai dawo da ita hankalinta idanma hauka takeyi..

Bayanan Anne da takardun daya gani da bayanin komai yasanyashi Kiran Dr faruk take agurin.

Cikin nutsuwa Dr faruk ya tabbatarwa da Turaki sakamakonsu na alluran da aka samu Sashen Na'iman dama sakamakon qwayoyin maganin allurar dasuka samu ajininta sosai tare Kuma da babbar illarsu ga qwaqwalwarta Dan kuwa zuwa yanzu idan Ana yimata ya tabbatarda qwaqwalwanta yagama juyewa gabaki daya.


Bai taba Jin takaici da baqin cikin kansa ba da rayuwarsa kamar yau daya samu wanna mummunan labarin,

Sakacinsa akanta yasa mummanar kaddarar aminya cutatar da rayuwarta ta hanya mafi Muni,

Meyasa Bai taba tsayawa yayi lamarinta kyakkyawar fahimtaba da zai iya gano lafiyarta da rashinta..

Rintse idanuwansa dasukai jajir yayi kafin ya miqe ya fita yauma da kansa ya ja mota a irin tuqin da Babu Wanda yataba ganinsa yayi ya Isa gidan Zinat Dake haukace tagama hargitsa gidanta koina bataga gwalagwalan Na'ima ba data ajiye ga siddika batanan ta gudu ga takardun asibitin Na'iman ma sun nata
Siddika ta tattara ta gudu.

Haukace take tanajin kamar zata Kama da wuta sbd sune dukiyar Na'iman datake taqamar zasu zama natan tayi arzki dasu Amma Rana tsaka ace ta rasa wlha bazata yardaba neman siddika zata tafi saita nuna Mata ba'a irin wannan gangancin da ita.

Tsallaka Ms Na'ima Dake kwance a qasa tana bubbuga kanta tayi cikin tsananin Azabar abinda takeji suna Mata yawo cikin Kai
Jin kafar mutum ta tsallakata yasata cafke kafar da sauri tana cewa"

Kece Laylah,
Kece Laylah,
Meyasa kikaci Amanata bayan Ina kaunarki da gaskia...
Meyasa?

Haqori tasa ta cafke qafar da wani irin cizo Mai azabar gske.

Ihu Zinat keyi tana dukan Na'iman da qafarta daya Amma Taki saki qafar ga jini sai fesowa yakeyi Sbd ba qaramin kafa Mata hakoran tayiba suka shiga qafar sosai.

Agogon Kan gefen gadonta ta fizgo da qarfi tareda bugawa Na'iman a Kai take azaba tasakata sakin kafar tana somewa agurin.

A haukace ta fito daga gidan ko gani batayi sbd jinin da kafarta ke fitarwa Sosai ga tashin hankalin da siddika ta sakata a haukace ta fada motarta tana tayarwa motar Jamian tsaro tsayawa gaban motarta Dake kofar gidan.

Wata motarce ta Parker siddika da A Abdoul Suka fito sai alokacin gaban Zinat din yayi mummunan faduwa dan da farko Bata tsororaba tunda tasan Babu wani dalilin zuwan hukuma gurinta Amma ganin siddika tareda A Abdoul ya tabbatar Mata da komai.

Reverse tafara Yi da motarta cikin tsananin gudu sbd batada damar yin gaba tunda agabanta suke tanayin Bata Suka bita da motacinsu a guje

TURAKI daya iso gidan Tuni siddika harta janyo Na'iman Dake sume tamkar Babu Rai tareda ita ya qaraso ya dauketa gabaki daya yakai mota tareda rufewa yashiga yaja motar yabar gurin.

Sosai Zinat ke gudu da motarta cikin reverse sbd tasamu ta tserewa jamian ta hau titi,

Kwana zatasha da mugun speed
Tayoyin Suka qwace Mata motar tayi cikin wata sabuwar transformer Dake street din take kuwa transformern tafara yayyafin wuta suna zuba Kan motar
Hankali tashe tafara kokarin bude motar dukkanin jikinta na rawa tana ihun a taimaketa Azo abude Mata ta fita Amma kowa yakasa qarasawa sbd wuta tafara cin gaban motar tata,

Tana gani tafara sakin ihu tana bubbuga glass din motar,

Dole Jamian tsaron aka fara kokarin cetonta Amma Sam wutar Taki Bari kowa ya matsa sbd transformer na barin wuta motarma naci Dan Haka kowa ma guduwa yafarayi da motarsa Daga gurin ga ihunta da bubbuga glass dinta anaji Ana gani tana konewa da ranta cikin tsananin azaba
Tun Anajin ihunta har aka dainaji Haka Wutar ta cinyeta qurmus kafin akashe a fiddota.


Asibiti aka Kai Ms Na'ima itama sbd yin nasu binciken asalin akan qwaqwalwarta.

Anne da idonta ta ringa tsiyayarwa da Na'ima hawaye sbd tana cikin mawuyacin hali.

Laylah ma kusan sai dataiwa mum din tata kuka sbd tausayi,

Ga Abbanta daya taba hankalinsa uku akansu,
Rabi na Kan baby, rabi nakan mum rabi Kuma Yana kanta sbd itama har lokacin takasa dawowa daidai duk da ta sakawa kanta tawakkali yanzu fatarta abba da Momy su samu lafiya,
Har gwara Momy ta farfado sbd wutarta batai yawan ta abbanba.


A Abdoul ne ya tsaya aka rufe case din Zinat da Na'iman akan rasuwarsu Sa'adah tunnda Zinat din tabisu inda ta aikasu din.

Bincike Mai kyau tsafta ya tabbatarda Ms Na'ima qwaqwalwarta tagama juyewa Amma Basu cire ran dawowarta daidaiba Dan Haka tana Jin sauki aka sallamota gida.

A sasshen Anne take itama wannan karon dakin Sa'adah yakoma nata siddika itace Mai kula da komai nata sbd yanzu komai nata datakeyi kallo daya zakai Mata kasan tana matsalar qwaqwalwa.

Tsananin tausayinta yasa kaunarta Mai girma wanzuwa a zukatansu,

Anne har cikin ranta take Jin Na'iman sbd ba qaramar qaddarar jarabawa bace mace Mai girma kyakkwa ace kanta a juye yakeba,

Siddika Takoma tamkar uwar data haifeta takejin Na'iman sbd duk da tasamu matsalar dukkaninsu suna cikin gata da kwanciyar hankali da kauna daga kowa.

Yanayin matsalar ta me Na'iman sai tazo Mata da qaunar Laylah Babu Wanda takeson zama dashi kokuma yabata maganinta Tasha ba gardama kaman Laylan.
Shi Turaki qarfi da yaji Abbah take cemasa kaman yanda taji Laylan na fada.

An sallamo Baby Sa'adah kaman yanda ta roka Abban ya sakawa babyn Dan haka sai alokacin farin ciki da walwalar gidan tadawo
Abbah ya fidda asalin tsananin kaunar dayakewa 'yarsa danma baya kwana guri daya dasu.

Dazai koma Babu yanda baiyi da laylanba su kebe taqi sbd Anne da kamar ta saka Mata ido sbd gyaran da ake Mata Wanda Bata samuba na aure
Dan Haka Haka ya lallaba ya koma yaso tafiya da Na'ima sbd asibiti da za'a kaita Amma taqi yarda ta matsa koina idan bada Laylah da baby Sa'adah za'ai tafiyarba
Dole ya kyaleta kafin Laylan ta tashi dawowa saisu dawo tare.

Momy tana samun sauki sosai sbd kullum Laylan na tareda ita a asibitin danma Anne ta Hanata kwana asibitin sbd Kar a daukowa baby Sa'adah sanyi shiyasa iyakacinta wuni kullum tadawo.

Momy tunda tasan Sa'adah ta tafi tabarta Babu Wanda yayi tunanin zatai dangana da karfin zuciya irin Wanda tayi saima kurawa baby Sa'adah Ido datakeyi Koda yaushe tana kallonta amatsayin Sa'adahnta datana jinjira.

Baby Sa'adah nada wata uku Suka Gama zamansu a Nigeria suka tattara suka koma Amma Saida Suka fara zuwa kaduna itama taje tayiwa iyayen Ruky gaisawa bayan su Turaki sunje gurinsu tun farkon al'amarin sun musu baya da duka sauran abun daya kama.

Itama alkhairi tayiwa iyayen Ruky din sosai kafin tabaro.

Sbd samun sassauncin komai na dawainiyar data hau kanta Momy da abbanta da haryanxu baya komai bayan Dan numfashin da shima sai can daqyar yake fita anan wata babbar asibiti Atlanta akai kwantar dasu.

Ms Na'ima ma kwanansu hudu da zuwa yatafi da ita nata asibitin itama sukai admitting dinta akan za'a dorata Kan treatment data fara dawowa daidai za'a sallameta sai aqarasa treatment din a gida.

Cindy tunda Suka dawo itada sofia aka Rasa waye yafi tsananin kaunar baby Sa'adah wadda yanzu kamanninta da Abbanta yake fita sosai sbd farace tas ta dauko farar fatarsa da idanuwansa harma da hancinsa.

Tunda suka dawo sai yanzu tasamu cikakkiyar nutsuwar kanta data gidan sbd yanzu itace Matar gidan.

Masu aikin gidan sunanan kaman yanda suke ada Cindy da Siddika dan Haka yanzu gidan komai anatse cikin kwanciyar hankali musamman batada wata damuwa akansu Momy sbd asibitin akusa take koyaushe ta tashi zuwa takeyi gurin momyn wadda zuwa yanza tana magana saidai komar koyaushe Bata iya kallon Laylan Sosai Amma wannan karon sbd kunyar ne da fargabar fuskar Sa'adahnta datake gani akan fuskar Laylah badan komaiba sai Dan koyaushe burin Sa'adah inganta rayuwar Laylah ne gashinan ta tafi tabarsu daga ita har Laylan basuda kowa yanzu sai juna.

Ita baby Sa'adah kuwa lokaci daya Allah ya dauki tsananin kaunarta Mai qarfi ya jefa a zuciyar momyn saidai Bata iya nunawa sosai sbd gudun zaqewa tunda tasan irin yanda suka taso da Laylan,
Ga Yan uwanta ko a waya Babu Wanda yataba Kira yaji yanayinta shikenan dai ta tabbata batada kowa sai Laylahn sai kuwa Mahmoud idan Allah ya tada kafadunsa.



********Wanka ta fito daureda qaramin towel da Bai Gama rufetaba
Duk santala santalan cinyoyinta a fili sai daukan ido sbd tsananin haske da hutun da fatarta ke samu na kwanciyar hankali.

Zama take kokarin Yi Kan kujera taji an rungumota ta baya
Tayi saurin waiwayowa

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login