Showing 66001 words to 69000 words out of 165653 words
daga can ta turo baki gaba tana amsa sallamar, ha'di da cewa.
“Abiena I miss you fatan kana lafiya? Ya gajiya? Jiya nayi bacci marar da'd, pls Abie ka biyo Espagne na ganka pls karka wuce Chad.â€
“Alhmdllh Babyna hope kina lfy ya shirye² tafiya? Na miki alqawali zuwa nima bazan iyaba nayi kewarki sosai Habibaty Ummiâ€
Ashagwa'be ta ce“Uhmm! Anjima ka'dan ne Abie zamu tafi, ok sai kazo, rabin raina.â€
A tausashe ya ce“Masha Allah babyna sai na shigo jibin insha Allah ki kularmin da kanki zan kiraki OK? Pls kici abinci nasanki bakya cin komai cikin jirgi.â€
Asanyaye ta ce“Ok Abiena bari na kwanta ka'dan bye.â€
Murmushi yay ya sumbaci wayar ya ce“Allah saukeku lfy bye baby Abienta.â€
Asakalce ta kirasa.
“Abienah!â€
“Na'am babyna! Oya kwanta kiyi bacci ki huta kafin lokacin tafiyarku.â€
Abie Dr Moha ya Kira ya ce ya ya qara hkr zuwa dare ko yamma zasu shigo hospital. Daga nan ya Kira Jaddatu da Hanan and Abie 2 suka sha fira.
Misalin 9 Abie ya kirasu Tanko duk suka fito sukayi breakfast wanda kukun Abie ya musu breakfast mai da'di da ha'daddan tea, bayan sun gama Abie ya ce suje su kwanta su huta, su jirayi tashin Ibtisam.
*Tchad*
Misalin 'karfe 11 na safe jirgin su Rahma ya 'daga zuwa 'kasar Espagne, bayan ta yi sallama da 'yan gidansu Latifa harda kukanta.
Abie da Hanan har airport suka rakata sai da jirginsu ya tashi suka dawo gida.
Jaddatu zaune tana mitar tafiyar Rahma.
“Wlh gidan yau ba da'di duk da daman sai ta ga dama take zama 'kasa amman banajin da'di. Oh! Wai Latifa harda kuka samun waje.â€
Ummu Adnan da take yanka mata kanka da apple ta gintse dariyarta tana fa'din.
“Jaddatu sabo akace tirken wawa.â€
'Karan doorbell na falo ne ya Hana Jaddatu mgna ta ce“Je ki bu'de.†Abraham ne tsaye bayan sun gaisa ya ce.
“Yauwa ka ce da Ummi baqon malamin yazo an sauke shi ya jima na bari ya hutane yanzu sai amasa iso ya ga marar lafiyar.â€
Ummi Adnan ta amsa da“Toh ba damuwa.â€
Gaban Jaddatu ta zube tana mata bayani.
Jaddatu ta lunquma kankana bakita ta ce “Toh toh ba laifi je kicema Saratu ta shirya sai afito da ita falo ayi komai agabanmu kamar yadda me gidan ya fa'da.â€
Ummu Adnan ta amsa da “Toh an gama.â€
Miqewa ta nufi bedroom 'din.
Raiyana zaune Saro ta shiyarta da kyar, sai wasu irin fizge² take tana zabura tana taune bakinta, tana jujuya idanu duk ta ko'de ta rame.
Da sallama Ummu Adnan ta shigo.
Amutunce suka gaisa da auntie Saro, ta mata bayanin komai.
Saro ta ce“Ok kamata muje tinda ashirye take, naga kamar da sauqi jiya zuwa yau gaskiya.â€
Afalon suka zauna da ita saman carpet.
Jaddatu ta tsira mata idanu tana tauna tufa ta girgiza kanta tana fa'din.
“Wallahi Raiyana kin cutar da kanki matuqa na miki sha'awa zama da Abdul. Ummu Adnan je kice su shigo, amman kira min Hanan idan kuma bacci take barta karki tasheta.â€
Cikin girmamawa ta amsa ta nufi corridor 'din da zai kaita bedroom 'din Jaddatu. Bacci ta iske sunayi ta fito ta sanar da Jaddatu ta tafi kiran Abraham da baqon.
Abie da Mal Adamu tsaye suna mgna da Abraham akan baqon.
Ummu Adnan ta sanar da Abraham su shiga.
Abraham ya Kira baqon.
Masha Allah babban mutum ne kana kallonsa kasan malamine wanda yasan abinda yake ba muna malami ba, Qur'ani ce ahanmunsa da wata roba mai 'dauke ruwan addu da bulala lafceciya wacce taji addu'in ayoyin Allah.
Sallama yay musu suka amsa sukayi musabaha, Abraham ya masa jagora zuwa ciki har da Abie sbd idan ta Kama ya temaka masa sai ya temaka masa.
Mal Adamu ya koma ciki ya zauna wanda Abie ya roqi alfarmar ya jirasa har ya dawo.
Suna shigowa falon cikin kamilalliyar muryasa yay sallama.
Raiyana ta zabura ta 'kurma wani irin ihuui jikinta na rawa ta arta aguje tana neman wajan 'buya.
Jaddatu ta ce.
“Maza Saro Ummu Adnan akamota.
Malam ya ce“A'a Ku barta.
Wata irin tsawa ya daka mata ya ce“Maza kuzo nan kumin bayani kafin yanzu jikinku ya fa'da muku.â€
Raiyana da ta shige 'kasan kujera jikinta ma rawa ta fito ta nufo wajansa ta zube gabansa tana ha'ada hannayenta........
*Pls kuyi manage ina busy ne.*
_💃ðŸ»'Yar Ajin Tubarkallah🥰_
_*🤲ðŸ¼Ya Allah ka jiÆ™anmu kayi mana rahama badan halinmu ba.ðŸ™ðŸ¼*_
3/3/22, 15:25 - Buhainat: ```D A```
```49&50``
_*My Sisters Don Allah Don Darajar Annabi Karki Karanta Idan Baki Biya Ba, Na Ku'dine Idan Kinga Yana Yawo Na Satane Ga Hanyar Da Za Ki Samu Naki Akan.😟👉ðŸ¼300N +22796515805*_
Cikin wata irin murya marar da'din sauraro, ta fara mgna tana sake ha'de hannayenta.
“Mun tuba malam karka 'karasu duk an 'konemu, karka 'karasamu.â€
Malam ya zauna ya na kallon Raiyana baiyi mgna nazartar ta yake sosai, tabbas aljannun gaskiya ne ba na 'karya ba, addu'a ya fara ya bu'de roba me ruwan addu'a ya 'dan watsa mata.
Ihu ta saki tana qoqarin tashi amman ta kasa dan ya 'dauresu tam awajen.
“Kukuwa me ya kawoku jikin baiwar Allah nan? Lallai ku fa'damin gaskiya idan ba haka ba zaku 'kone tsaf zan 'kone ku 'kurmus.â€
Ya na idar da mgna bai jira komai ba ya bu'de Qur'ani ya fara karatu.
Rawa jikinta ya fara tana wata irin lauyewa azaba suke sha sosai, daman an 'kone musu rabin jikinsu lkcn suna jikinsu Rahma.
Wani ihu suka saki suna fa'din.
“Zamu fa'da zamu fita karku rabamu da 'ya'yanmu.â€
Dakantawa Malam yay ya ce.
“Muna jiranku me ta muku?â€
Cikin azaba da fitar hayyaci suka zayyanewa malam dukkan abinda ya faru tiryan-tiryan.â€
Malam ya ce“Subahanallahi! Haba! Me yasa za'a ha'da baki daku acuci 'yan Adam? Jansin mu ba 'daya ba da ku, dukkanmu Allah ya haliccemu ne dan mu bauta masa, amman dayawa daga cikinku bakuda komai sai zalumci sai cutar bil'adam. Toh yanzu abinda nakeso daku kuji tsoron Allah ku tuba ku koma ga Allah, ku daina ha'da baki da bokaye dan bazan Kira malamin tsubbu malami ba, ku daina shiga jikin mutane kuna cutar dasu.
Ku fita fita ta har abadan baku ba ita.â€
Kai Raiyana ta shiga 'dagawa alamar yarda.
Bulala ya zuba mata sau uku, tai wani irin 'kara ta zube kwance wajan tana atishawa ba qaqqautawa ajere wajan sau hamsin wani irin baqin hayaqi ya dinga fita bakinta da hancinta da wasu irin ruwa masu yauqi su ba blue ba su ba baqi ba.
Shiru kakeji sai bacci Raiyana take tana sauke numfashi.
Malam ya ce“Alhamdulillahi! Komai yazo 'karshe insha Allahu bazasu dawo ba, ga wannan ruwan idan ta tashi abata tasha, insha Allah bazu sake cutar da ita ba...â€
Jaddatu ta fashe da kuka tana fa'din.
“Amman mu ai ta cutar damu, Allah ya isa Raiyana wlh kinyi asara Allah da nasan kece kika ha'da wannan masifar tsakani takwara da Ja'afar bazamu barki ki zauna agidan nan ba, wlh yau 'din nan sai kun fita kun barma na gidanmu Ashe ba dan Allah kike zaune damuba kema irinsu Zuwaira da Hanifa ne daman Naja'atu ba yauba Allah ya tsine mata albarka, dan ta kwashe kayanta daga gaban ma'aiki.
Tin bayan Naja'atu sai da yaron nan ya ce ya haramta aure naqi nake tirsasa masa har ya sake sau uku amman kowa da mugun nufinta kafin ya gama jarabasu sai Allah ya tona musu asiri toh wlh yanzu an qare matarsa zata bayyana ta Abadan nagaji da abinda ake masa.â€
Ta 'karashe mgnar cikin kuka sosai.
Abie 2 hkr yake bata Hanan ta fito ta zauna tana binsu da kallo ta rungume Jaddatu tana tamabyarta.
“Wai ummina me ya farune?â€
Hanci taja ta face majina tana fa'din.
“Hanan ashe duk mugun abun da ya samu Rahma kwanaki wannan annamimiyar wacce na 'dauka MATAR arziqi na saka ya aureta itace tahaddasa komai.â€
Malam yay gyaran murya ya ce“Ayi hkr dan Allah addu'a zaku mata Allah yasa ta shiryu sanadin hakan, Allah ya kiyaye gaba, Abraham muje zan wuce insha Allah.â€
Ya qarasa mgnar yana miqewa.
Har Abie suka fito suna jimamin abinda Raiyana ta yi toh me take nufi da hakan.
Saro kuka take kamar zata ha'di zuciya, ga kunya ta lullu'be ta yi da ta sanin kasancewar Raiyana 'yar uwarta sabida iyayansu basu 'dorasu akan turba marar kyau ba.
Jaddatu ta ce“Wlh ko kukan jini kike sai kunbar gidan nan yanzu munafukai azalumai...â€
Hanan ta rufe mata baki ta ce“Haba! Ummi kiyi hkr aka kashe miki miji ma kika hkr bare wannan, sannan don Allah ki bari wanda ya ajiyeta yazo sai kiji irin hukincin da zai yanke ba ruwanki dasu, Saro kamata ku shiga ciki.â€
Ummu Adnan ta kamata mata suka cicci'beta suka nufi bedroom.
Jaddatu sai kuka take dakyar Hanan ta lalla'bata.
Abraham ya sallami Malam yana masa godiya har tashar mota ya kaisa.
Abie 2 ya jima yana mamakin al'amarin akan me Raiyana ta ha'da Rahma da Ja'afara soyayya?
*Australia*
Misalin shabiyu Ibtisam ta farka.
Ahankali ta fara qoqarin bu'de manyan idanunta, wanda taji sun mata nauyi sosai ga wani irin zafi da sukeyi.
Jinta manne ajikin mutum ga wani irin 'kamshi mai masifar da'di ya mamaye dukkan 'kofofin hancinta tai saurin qarasa bu'de idanunta.
Basu sauka ako ina ba sai saman kyakkyawar baqar fuskar Ja'afar, yana manne da ita ya zagaye 'kugunta fuskarsu dab da juna suna jin bugun numfashin juna sosai.
Baccinsa yake anutse.
Manyan idanunta ta zaro tana fa'din.
“A'uzubillahir minan she'danir rajim! Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un! me kamin? Ina ne nan kamar na mutu ina aljanna? Wayyo na shiga uku ina ka kawoni bayan ka gama zalumtata? Wayyo Anna wayyo Baba ku yafemin sakammakon bijire muku anci amanata, an 'batamin rayuwaâ€.
Ta 'karashe mgnar tana fizge jikinta cikin zafin zuciyar da bata san tana ita ba.
Amman ko gezau ta kasa amshe jikinta daga Ja'afar.
Tattausan hannunsa ya sanya ya rufe mata baki, ya mata rumfa da faffa'dan 'kirjinsa.
Wani irin kallo ya watsa mata wanda abaya yake sakawa ta shiga hankalinta.
Sosai taji tsoronsa, amman sai ta dake tana ture shi tana dukan 'kirjinsa hawaye yana shatatowa kan fuskarta.
Fuskarta ya riqo da hannunsa ya zuba mata kyawawan idanunsa, wanda suke rikitata, cikin sansanyan murya ya fara mgna yana shafa lips 'dinta.
“Mon cÅ“ur kiyi hkr kinji, ba da gangan naci amanarki ba,ki yafemin sanin kanki ne ni bazan ta'ba cutar dake ba ko kwanciya waje 'daya dake ba tare da kin halatta agareni ba.â€
Ya 'karashe mgnar yana sumbatar goshinta da idanunta yana lashe mata hawayen fuskarta, wanda hucin numfashinsa yake sauka saman fuskarta tana shaqo 'kamshin bakinsa.
Ture shi ta shiga yi tana kuka, tana fa'din.
“Kai macucine na tsaneka sakeni bana sonka na tsaneka...!â€
Baki ya rufe mata cikin zafin nama yana mata wani mugun kallo amman sam Ibtisam bataji bata gani ta dage sai wani irin kuka take tana son raba jikinta da na shi.
Cak ya 'dauketa ya nufi toilet.
Tana bayansa sai yakushinsa take ya ha'da mata ruwan wanka ya direta fuska ba wasa yana jafa idanunsa cikin nata ya ce“Wuce maza kiyi wanka kizo na kaiki wajan Baba.â€
Bai tsayaba ya wuce.
Jin abinda ya ce ya sanya tu'bewa tana kuka tana kallon bathroom 'din wai wajan wankane nan kamar 'daki, zoben hannunta ta kalla yana walqiya kamar diamond, ta zaro idanu tana fa'din “Ina na samu wannan zoben mai kyau?â€
Ja'afar doguwar rigar atamfa wace ya dinka mata ya ciro mata da pant daman yaga ba saka bra take ba, ya feshe kayan da turare madedecin mayafin ya ajiye mata gefen bed, ya fita domin ha'do mata abinda zata ci.
Cikin sa'a falon ba kowa ya wuce kan dinning ya ha'do mata tea mai kauri ya zubo mata soyayen dankali da kwai da naman rago wanda akayi farfesun sa ga hufzah gefe ya 'daukar mata biyu, yaje kitchen ya 'dauko tray ya jera ya koma 'dakin.
Wanka tai sosai taji da'din jikinta ta 'dauro alwala ta 'daura towel amman ta kasa fita kuma daman can Ibtisma idan ta cire kaya tayi wanka bata iya maidasu jikinta sbd 'kyan'kyami gareta.
Ja'afar jin shiru ya saka ya biyota.
Tsaye take tana rarraba idanu hawaye nabin fuskarta.
Bai mata magana ba ya kamo hannunta, tana tirjewa cikin kuka ta ce.
“Ina ka satoni ka kawoni? Wacce duniya ce nan Ja'afar na tsaneka ban son ganinka...â€
Wata irin rikiracciyar tsawa! ya daka mata wacce tasaka Ibtisam rawar jiki ta qame waje 'daya tana shasheqar kuka.
“Wlh idan bakimin shiru ba zanyi maganin ki zo nan.â€
Kanta ta sadda 'kasa taqi zuwa wajan nasa dan ta 'dauki alqawali sai dai ya kasheta bazata sake soyayya da shi ba.
Kai ya girgiza ya iso wajanta ya Kama hannunta ya zaunar da ita bakin gadon ya shiga goge mata jikinta da qaramin towel yana qoqarin shafa mata mai ta riqeshi tana kuka.
“Don Allah ka rabu dani bana so zan shafa hakan haramun kakeyi.“
Bai kulata ba ya juya mata baya ta shafa man ta 'dauki kayan ta saka ta yafa mayafin ta sanyan takalmi ta ce.
“Muje na gama ka sadani da iyayena.â€
Shiru tai tana murgu'da baki ganin yadda ya tsare gida.
“Zo zauna kici abinci muje su miki bayani da Kansu.
“Zatayi mgna ya 'dora yatsa bakinsa.
Ya kamo hannunta.
Dan karta 'bata masa lokaci ya shiga bata abaki, fafur taqi ci sai da ya zaro mata idanu.
Sosai ta sha tea 'din taci farfesun hufzah 'daya taci.
Da kansa ya goge mata bakinta da tissue ya kwashe kayan yakai kitchen ya dawo.
Miqar da ita yay ya riqo 'kugunta yana mata sahihin kallo.
Baki ta zum'buro gaba tana qoqarin cire hannunsa ajikinta.
Sumbatar wuyanta yay wanda saida taji wani yamm.
Akunne ya ra'da mata.
“Ja'afar 'dinki kika tsana um?â€
Kuka ta sanya masa tana 'daga kai alamar Eh.
Murmushi yay mai tsada ya goge mata fuskarta ya kama hannunta suka fito.
Ibrisam kusan ru'dewa tai ganin falon duk sai ta qara tsorata tana qamqame jikinta ta ce“Kawai na mutum wlh siyar dani kayi.â€
Dariya yay marar sauri ganin falon ba kowa shiru yay saurin sumbatar la'bbanta ya zaunar da ita saman sofa ya kunna Tv ya zauna nesa da ita.
Abie fitowarsa daga wanka kenan ya ji wayarsa na neman agaji.
Abraham ya gani ya amsa kiran.
Cikin mutuntawa suka gaisa yana tambayarsa.
“Abraham! Baby ummina ta tafi ne?â€
Cikin girmamawa daga can ya amsa, da.
“Eh Yalla'bai ai anfi awa....â€
Nan ya zayyanewa Abie dukkan abubuwan da suka faru ya 'dora da cewa.
“Har an sallame shi ya tafi yana godiya da alkhairin ka gare shi.â€
Abie ya shafi kwantaccan gashin 'kirjinsa wanda yake baqi qirin, ya furta.
“Alhmdllh! Amman banji da'din tonon asirin nan ba gaban jama'a, Allah ya kyauta ya qara mata lafiya, Abraham zan fita meeting zan kira ka insha Allah.â€
Sallama sukayi.
Agaggauce ya shirya sabida zai gana da wasu baqi zasuyi meeting.
Tsaf ya shirya cikin suit Green sun masa masifar kyau, sai baza qamshi yake.
Kira akaro na 4 ya shigo.
Goshinsa ya dafe ya isa wajan wayar.
Sunan Jaddatu 'baro² yana yawo akan screen 'din wayar, ya rubuta *Sweet Ummina.*
Da sauri yay picking call 'din.
Da sallama ya fara yana gaisheta.
Daga can yaji Hanan tana fa'din.
Don Allah Ummina karki fa'damasa ki tayar masa da hankali bari ya dawo.â€
“Ke! Hanan wlh xan cin miki mutunci fa! Sai na fa'da ban fiki son 'Dana ba ni na haifi abina duk wanda zai so bayana ne. Wa'alaiki salam Abdul kana jina?â€
Abie yay gyaran murya wanda Jaddatun ta ankare.
Cikin nutsuwa ya gaisheta yana fa'din “Ummina don Allah ki kwantar da hankalinki nasan komai daman karki damu idan na dawo za'asan abun yi.â€
Jaddatu daga can ta ce“Abdul so nake wai da su kwashi tsunmakaran kayansu subar mana gidanmu.â€
“No! Ummina abari har na dawo har yanzu ita d'in zaman mata take gareni insha Allah idan nazo zakiga irin hukuncin da zan yanke.â€
Sosai ya kwantar mata da hankali jin ta fara kuka tana fa'din ta rasa me yawa mata kowace idan ta Shigo shi da Rahma suke son ganin bayansu.â€
Dakyar ya samu ta bar kukan ya shiga bata labarin irin temakon da ajani yama Ja'afar akan Ibtisam.
Toh sai ta manta wacan mgnar ta shiga mamakin lamarin daga nan ta basa Hanan suka gaisa.
Can falo kuwa Tanko ne ya fito kamar amafarki ya ga Ibtisam tsaf cikin shiri zaune tana kuka qasa².
Tanko ya kirata.
“Ibtisam!â€
Aguje ta isa wajan mahaifinta ta qamqameshi tana sakin rikitaccan kuka, tana fa'din “Don Allah Baba kayi hkr na tuba ku yafemin kuskuran da nayi na guduwa na barku da damuwa.â€
Janta ya yi suka zauna.
Lallashinta ya shiga yi yana tambayarta da jikinta me takeji yanzu?
Laraba ce jin muryar 'yarta ta fito aguje tana kiranta “Ibtisam!â€
Rungume juna sukayi suna kuka.
Abinda ya janyo hankalin Abie ya fito.
Cike da farin ciki yake fa'din.
“Ma Sha Allah Ibtisam an farka Alhmdllh sannu ya jikin?â€
Sai lokacin ta waigo tana kallonsa.
Tinda take arayuwarta zata iya rantsuwa da Allah bata ta'ba ganin namiji mai kyawunsa da cikar zatinsa ba, ga shi balarabe kyakkaywar fuskarsa mai zagaye da saja ga wata 'kazumba mai kyau, ga gemu mai 'dan tsayi, doguwar fuskar shi wacce ta 'dan saka fa'di ka'dan 'dauke take da manyan idanu farare masu lumshewa,da siririn hanci mai tsayi, sai 'dan 'karamin bakinsa jajir kamar na jariri. Dogone sosai mai cikar zati ga faffa'dan 'kirji, duk da ya fara manyanta amman tamkar ayanzu ne yake cikin zamaninsa sbd kyawun jiki ga jin da'di wanda yake bayyane afatar jikinsa.
Aranta take ta yabonsa haka tana mamakin daman za'a iya samun namijin da ya kere Ja'afar dinta akomai?
Idanu ta tsira masa babu ko 'kiftawa.
Abie yay saurin janye idanunsa cikin nata aransa yana fa'din wannan kallon na 'kauyanci fa? kamar wata halitta kiga gani.†duk acikin zuciyarsa yake mgnar.
Sam Abie bai fiye son kallo ba.
Tanko ya ce “Ibtisma bakya jin Ana miki mgna ne?â€
Firgigit tai tana sadda kanta ta gaishesa.
“Ina yini?â€
Tana mamakin ya akayi ya iya hausa duk da taji hausar ba rass bace.
Abie ya amsa yana tambayarta da jiki.
Ja'afar wani irin haushinta yaji akan yadda ya ga ta qure Abir da idanu.
Ja'afar ya sake gaishe da Abie.
Zama Abie yay yana amsawa cikin sakin fuska yana fa'din.
“Ja'afar barka da arziqi Allah ya qara tsarewa, bari na dawo daga meeting sai muje a qara duba lafiyarta idan ba wata matsala kawai sai mu juya gida idan kun huta kwana biyu.â€
Ya qarashe mgnar yana sauke numfashi yana kallon wayarsa kira na shigowa.
Bai 'daga ba.
Gyaran murya yay ya ce“Yauwa Shamsu sai kama yarinya bayani yadda zata fahimta.â€
Tanko ya gyara zama yana amsawa da “Toh Alhaji.
Ya fuskanci Ibtisam, ya mata bayanin dukkan abubuwan da suka faru har aurenta da Ja'afar.
Ya 'karashe mgnar da fa'din.
“Dan haka banson sake jin wata fitina daga gareki ki amshi aurensa da hannu biyu, daman sbd shi kika fito Allah ya yi daman can shine mijinki dan haka karki 'kullace shi ba yin kansa bane.â€
Ibtisam ta fashe da kuka tana fa'din.
“Baba ni