Showing 78001 words to 81000 words out of 165653 words

Chapter 27 - DATTIJON ARZIKI

Start ads

Rahma   

15 Aug 2025

862

Middle Ads

night ki ci abinci OK? â€
Kai ta jinjina tare da amsawa“Toh Abienah.â€
Kiran ya dates yana sakin lallausan murmushi.

Musalin 11 Ja'afar zaune gefen bed yana waya dasu Harisu cikin nisha'di yana gayamu su gobe zasu taso.
Ibtisam sai turo baki take wai ya hanata bacci.
Bayan ya gama yay shirin bacci ya hauro gadon ya rage hasken 'dakin ya kwanta, ya matso jikinta ya sanya hannayensa ya zagaye 'kugunta ya tura fuskarshi tsakanin wuyanta yana jujjuyawa ya Kira sunanta cikin wata irin murya.
'Kam'kame jikinta tai tana sauke ajiyar zuciya.
Murmushi yay bai mata komai bakinsu kawai ya ha'de yana mata wani irin fitinannan kissing wanda ya zautar da ita ta rungumeshi 'Kam tana maida masa martani, har bacci ya 'dauke su.

Washegari cikin shirin tafiya suka ta shi, Abie ya saka an zagaya gari dasu sunyi kalle² laraba idanunta kamar xasu fa'do waje sayayya sosai Abie ya musu yana taka tsantsa da Ibtisam sbd yadda take qoqarin shige masa shiyasa wajan siyayyar yaqi shiga wajan yana mota Pa 'din Abie ne yake biye dasu.
Tanko ganin irin ku'din da Abie ya kashe musu harda kuka ya riqe 'kafarsa yana masa godiya.
Misalin 'karfe 1 na rana jirginsu Ja'afar ya 'daga zuwa Chad Abie shi kuma nasu 2 na Rana ya 'daga Australia.

Espagne
Rahma yau ta ci sa'a 'karfe 3:30 na yamma suka dawo daga school.
Murna ta hanata zaune ta hanata tsaye, da kanta tinda tai sallar la'asar ta shiga ma Abienta girkin da ta San yana so fiye da sauran abinci.
Sai da ta kamamla komai Meerah ta shiyar kan dining area ta shiga wanka.
Bayan ta yi sallar Maghreb Wata irin kwalliya ta cancara wuyanta da kunnen and hannunta ta zuba gold haka yau ta canza sarqar 'kafarta ta saka ta diamond har tafi waccan kyau da tsari.
Riga da wando na Pakistan ta saka maroon sunyi mata masifar kyau wani irin 'kamshi take na ban mamaki, ta tufqe gashinta ta Saki jelar har gadon bayanta, ta yafa mayafin kayan.
Meerah kanta da take mace ta yaba kyan da Rahma tai da tsarin surata, sosai take mamakin tsantsar 'kaunar da Rahma takewa mahaifinta kamar dai saurinyata ko mijinta irin wannan girkin da 'daukar wanka.
Zaune take tana duba lokaci.
Zabura tai ta ce“Wayyo na makara zuwa airport maybe muje kusan tare, Meerah na tafi sai na dawo.â€
Ta 'karashe mgnar tana tafiya abinda taji a Tv yasa tai saurin dawowa baya ta qurama Tv 'kananun idanunta masu matuqar haske da kyau tana kallon labarun da ake, cikinta taji ya hautsuna zuciyarta tai wata irin bugawa lokaci 'daya taji duniyar na juya mata idanunta suna lumshewa kafin ta fahimci sauran bayani ta sulale nan 'kasa sumammiya...

_💃ðŸ»'Yar Ajin Ma Sha Allah🥰_


_*🤲ðŸ¼Ya Allah ka jiÆ™anmu kayi mana rahama badan halinmu ba.ðŸ™ðŸ¼*_
3/12/22, 00:27 - Buhainat: ```D A```

```57&58```

_*My Sisters Don Allah Don Darajar Annabi Karki Karanta Idan Baki Biya Ba, Na Ku'dine Idan Kinga Yana Yawo Na Satane Ga Hanyar Da Za Ki Samu Naki Akan.😟👉ðŸ¼300N +22796515805*_

Meerah da take fitowa daga kitchen idanunta suka sauka akan Rahma ta zube 'kasa.
Aguje ta nufi wajanta tana salati, ha'di da kiran sunanta.
Gabanta ta zube tana 'dagota tana girgizata ha'di da kiran sunanta.
“Rahma me ya sameki? Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un!â€
Duk ta ru'de ta rasa ya zatayi da Rahma.
Idanunta ya sauka akan Tv ganin irin labarin da ake, lokacin ana sanarwa jirgin da ya taso daga Australia zuwa Singapore ya fa'di, sai jirgin Turkey wanda zaije Istanbul shima ya fa'di.
Agigice Meerah wacce sam bata fahimci garin da akace ba tsabar ru'du jin ance ya taso daga Australia, ta 'kwalla ihu mai firgitarwa wanda ya haddasa me gadi da securities Rahma suka nufo hanyar falon aguje hannunsu riqe da bindigogi.
Ki shin 'kofar suke kamar zasu 'ballata.
Meerah ta kwantar da Rahma ta nufi 'kofar aguje ta bu'de.
Aguje suka shigo suna tambayarta menene?
Agigice take nuna musu Rahma da Tv tana fa'din.
“Ya mutu itama ta mutu.â€
Wajan Rahma suka nufa, tana kwance kamar gawa.
Me gadi ya ce“Ki kawo ruwa da sauri.â€
Robar ruwan da take ajiye saman center table ta 'dauko ta 'balle murfin ta zubama Rahma tana kuka.
Bata motsa ko gezau babu alamar zata farfa'do.
Securitien ta me suna Adeel yay saurin sunkuyawa ya cicci'beta ya ce“muje hospital karta rasa ranta.â€
Meerah haka ta bisu aguje ba ko 'dan kwali akanta.
Rungume take da Rahma abayan motar tana kuka har suka isa ha'dadd'iyar privet hospital dan a'kasar ma sai wane da wane yake zuwanta.
Cikin gaggawa aka amsheta aka shiga emergency da ita.
Temakon gaggawa suka shiga bata domin su samu numfashinta ya dawo.
Meerah ta kira Anee ta gayama tana kuka ba'a rufe 30 minutes ba sai ga Anee itama kuka take suna leqen Rahma ta 'kofar glass anata fama akanta har yanzu bata farfa'do ba.
Securities hankalinsu ya yi mugun tashi jin jirginsu Abie ya yi hatsari.
Misalin 9 na dare jirginsu Abie ya diro 'kasar Espagne.
Haka kawai yakeji fa'duwar gaba sam baya jin da'din zuciyarsa.
Shigar larabawa ce tsaf ajikinsa tamkar balaraben saudiya, kallo 'daya zakawa kayan jikinsa kasa na manyan ku'dine tin daga takalmin 'kafarsa har zuwa agogon gold da yake 'daure atsintsiyar hannunsa.
Farin glass ne manne akan fuskar shi.
Cikin nutsuwa yake sauko daga cikin jirgin, yana 'ko'karin canza layi.
Rahma ya kira tanata ringing ba'a 'daga sakammakon sun baro wayan agida.
Direban Rahma ya kira bugu 'daya ya 'daga cike da mamaki, nan ya sheda masa sun iso lfy azo 'daukarsa.
Nan ya shedama Adeel suka tafi 'daukansa cikin fa'duwar gaba, basu San irin tashin hankalin da Abie zai shiga ba jin 'yarsa hospital har yanzu bata farfa'do ba.
Daga airport kai tsaye hospital suka nufa.
Abie ya ce.
“He! Ina zamuje ne?â€
Adeel ne mai 'karfin halin cewa.
“Yalla'bai kayi hkr...â€
Ya basa labarin komai.
Wani irin juyawa kan Abie yake yana kira sunan Allah, hankalinsa amugun tashe.
Suna zuwa Abie ya nemi abarsa ya ganta, amman har lokacin ba damar ganinta, haka ya dinga kai kome ya rasa me yake masa da'di.
Misalin 10 na dare Rahma ta farfa'do tana wani irin fizge² da ihu tana kiran Abie.
Likitocin tsaye kanta, allura suka mata nan take bacci ya 'dauketa.
Doctor yana fitowa Abie ya taresa da rawar jiki yana tambayarsa.
Zofa ya goge, da harshen turanci ya ce“Muje officeâ€
Zaune suke Abie na fuskantar Dr.
“Yalla'bai zuciyar yarinyar nan tayi mugun bugawa sakammakon razana da abinda taji ko ta gani ya gigitata, har ya hasasa mata suma wanda ta kwashi sama da 4 hours kafin mu samu ta farfa'do, dan haka akiyaye 'bata mata rai, yanzu tana bacci da zaran ta tashi zata farka normal, ga magugun da za'a siyi ta sha su tsawon sati gudu insha Allah komai zaiyi normal. â€
Baki 'daya Abie baida wata nutsuwa bare kwanciyar hankali, tinda yaga Rahma kwace agadon asibiti, sai ga shi yanzu ana mgnar zuciyarta ta buga duk sakammakon taji jirgi ya yi hatsari tin bata tsaya taji wanda zaije wata qasa bane ba.
Numfashi ya sauke ya ce.
“Ok Dr ngd bari zan siyo magugunan yanzu, sai akaini wajanta.â€
Fita yay, sukayi mgna da Adeel, ya fita ba jimawa ya dawo da magugunan masu masifar tsada.
Doctor ya nunama Abie yadda zata sha sannan ya ce da ta tashi ayi qoqarin bata koda tea ne amman abari ya huce karta Sha da zafi sosai.
Abie ya tura direba da Meerah gida ta 'daukoma Rahma kaya Kala biyu ta tawo da kayan tea da komai harda girgin da Rahma ta shiryawa Abie.
Zaune suke sun sakata gaba bacci kawai take Abie na riqe da hannunta wanda baida drip, yana aikin murzawa yana shafa fuskarta.
Kallon Meerah da Anee yay ya ce.
“Dare ya yi kuje gida ku kwanta Ku huta, Anee a fara ajiyeki sai su Meerah su isa gida OK?â€
Tana share hawaye ta ce.
“Toh Abie Allah ya bata lafiya, gobe zan shigo daga makaranta.â€
“Ameenâ€
ya amsa suka tafi.
Dr ya sake leqowa ya dubata ya fice Abie ya rufe qofar ya shiga toilet ya 'dauro alwala ya fito ya gabatar da sallolin da ake binsa.
Koda ya idar nafila ya shiga, wadda sai 2 na dare ya miqe bayan ya yi doguwar addu'a Allah ya ba Rahma lfy.
Bakin gadon ya zauna ya rankwafo yana kallon kyakkyawar fuskarta.
Drip yaga sauran qiris ya qare ya cireta ya matsar da ita ka'dan ya haye gadon ya shigar da ita jikinsa sosai ya lullu'besu da tattausan bargo wanda Meerah ta kawo.
Wata irin ajiyar zuciya yaji Rahma ta sauke tana qara shigewa jikinsa ta tura fuskarta 'kasan wuyansa tana sauke numfashi anutsu irin baccin yana mata da'di.
Zagayeta ya yi da hannayensa yana buga bayanta ya manna mata kiss agoshi ya qura mata idanu yana jin mugun tausayinta.
Ahankali ya furta“Babyna da kin mutu ina tunanin ba lallai na jimaba zan biki, baki tsaya kinji da kyau ba Abienki kawai kike tunani har kunnuwanki suka jiyo miki jirgin da zaizo Espagne ne.â€
Kanta ya shafa ya tallabo fuskarta ya kirata cikin ra'da.
“Baby ummina!â€
Ina alluran da aka mata, sosai take aiki bacci take ta qamqameshi.
Tofeta yay da addu'ar bacci ya kulle idanunsa ba jimawa bacci ya sace shi.

A can kuwa 'kasar Tchad.
Jirginsu Ibtisam misalin 8 na dare ya sauka, Yahaya direba da Abie 2 and Mal Adamu sukazo tarbansu.
Ibtisam sosai gidan ya burgeta dan yafi ma na Australia tsaruwa da kyau.
Bayan sunyi wanka sunci abinci Tanko ya nemi izinin suje gaishe da Jaddatu, Abie ya musu jagora har falon.
Jaddatu ana zaune ana jan casbi suka shigo, da sallama.
Ibtisam da manyan hotunan Abie da Rahma ta fara cin Karo akowane kusurwar bango wasu suna tare rungume da juna wasun kowa daban sai Jaddatu da wani kyakkyawan tsoho balarabe sai wani guda sun kusa su goma suna cikin anushuwa.
Ibtisam tsirawa hoton Abie da Rahma ido tai, yadda suke 'kam'kame da jina suna dariya.
Tsaki taja 'kasan le'be duk da kuwa taga tsantsar kamarsu da Rahma, baki ta murgu'da ta janye idanunta daga kallonsu.
A'kasa suka zube suna gaisheta.
Jaddatu cikin sakin fuska ta amsa tana kallon Ja'afar da yake yanzu ya iya larabci ta ce.
“Barka da arziqi Ja'afar, Ibtisam ya jikin? Allah ya 'Kara sauqi na tayaki murna amman don Allah ki kiyaye ko gaba karki sake yinqurin guduwa sbd za'a miki auren dole, idan kin tsayawa kin gayawa Allah tabbas zai miki maganin komai.â€
Ja'afar ne ya fassarama Ibtisam tinda dukkansu bayan Abie 2 da Ja'afar Tanko da Adamu and laraba da ibtisma ba mai jin larabacin.
Ibtisam tai 'kasa da kanta cikin ladabi ta ce“Ngd ummi Allah ya saka da alkhairi.â€
Laraba ma godiya tai jin yadda Jaddatun take fa'dawa 'yarta gaskiya.
Hanan ta ce“Ya Abdul sai ya wuce wajan 'Yar lelensa ko? Amman ya ce gobe zai zo.â€
Abie2 ya girgiza kansa ya ce“Da wuya har mugani.â€
Dariya sukayi.
Latifa ta ajiye musu lemo da ruwa kayan motsa baki anata hira abin gwanin ban sha'awa hira Ja'afar ne me fassarawa.
Rayyana ce ta sauko ganin harda Ja'afar ta zube tana neman gafarasa.
“Wlh ba komai na yafe miki Allah ya yafemu baki 'daya.â€
Da “Ameen suka amsa, sun jima sosai kafin su miqe Jaddatu ta ce“Ja'afar Ibtisam da mamarta ga bedroom can hanyar kitchen su zauna kafin Abdul 'din yazo su wuce.â€
Ja'afar yay godiya ya fa'dawa Laraba sukayi godiya nan aka ha'dasu da Latifa kasancewad tana jin hausa ita ta kaisu har'dakin da zasu zauna.

Ja'afar bayan sun koma 'bangaran Abie2 yamusu sallama yace zaije gidan Baba Tsalha ya kwana wajansu Harisu ya yi kewarsu sosai.
Fatan alkhairi suka masa ya tafi.
Ibtisam ta baje saman bed tana qarewa 'dakin kallo tana jinjinawa wai nan wajan saukar baqine toh ina wa 'yan gidan gaskiya masu ku'di na morewa inji Ibtisam.
Fuskar Abie take mata gezu sai tsaki take ja taji haushin ganinsa da balarabar yarinyar nan.
Laraba ta ce“Ibtisam dan Allah ki ajiye hankalin ki,kinji?â€
Kai Ibtisam da 'daga sbd tasan duk abinda zatayi dan sugane bazasu ganeba gwara ta barma zuciyarta.

Baba Tsalha ganin Ja'afar awannan daren ba qaramin farin ciki yay ba, kamar ya goyasa yana tayasa murnar samun lafiyar Ibtisam.
Yahuza ya ce“Wai Ja'afar kaga yadda ka zama kwana ukune ko nawa har ka canza baqar fatarka tana sheqi.â€
Harisu ya kauma Ja'afar duka ya ce“Ba dole ba 'kasar waja ai akwai da'di ga Hutu ga amarya agefe.â€
Ja'afar bai ce musu uffan ba bayan murmushi haka suka kwanta awannan dare cike murnar ganin Ja'afar.

Acan Espagne misalin 'karfe 4 Rahma ta farka tana fizge² tana kuka tana kiran Abie.
Cikin bacci yake jin shasheqar kukanta tana kiransa tana karya mutu ya barta.
Firgigit Abie ya farka yana bu'de gajiyayyun idanunsa.
Riqeta yay gam yana matseta cikin jikinsa, ya tallabo kanta yana girgizawa ahakali yake kiranta.
“Baby Ummi! Oya bu'de idanunki ga Abienki tare kuke ban mutu ba.â€
'Kananun kyawawan idanunta wanda sukayi jajir ta bu'de jikinta na tsuma ta kalli fuskar Abie.
Hannunta ta sanye ta shafi fuskar shi taja dogon hacinsa ta 'dora yatsarta akan lips 'dinsa ta shafa bakinta na rawa ta ce.
“Ya Allah karka tasheni daga wannan mafarkin da nake kasa na dauwama ahaka Karna tashi ace da gaske jirgin su Abie ya fa'di...â€
Abie ya girgizata yana shafa fuskarata, idanunta ya gwala mata ya hura mata sansanyar iskar bakinsa ya manna bakinsa saman kunnenta ya hura mata da 'dan 'karfi ya kirata.
“Babyna please ki nutsu Abienki ne ba mafarki kike ba, ba jirgin Espagne ne ya fa'di ba, na Singapore ne oya bu'de idanunki kinji Baby.â€
Ya 'karashe mgnar yana riqe fuskarta da hannayensa.
Hawaye na kwaranya saman fuskarta ta mari kanta ta shafa fuskar Abie tana Jan gemunsa ta kai fuskarta dab da tashi tana sunsunawa 'kamshinsa ya cika mata hanci ahankali ta kirasa “Abie Rabin raina!â€
Cikin farin cikin ya amsa “Na'am Babyna ruhina.â€
Wani irin kukan da'di ta Saki tana qamqame Abie ta shige jikinsa kamar zata koma cikinsa ta rungumeshi sosai tana kuka iya 'karfinta.
Abie ya sauke 'katuwar ajiyar zuciya, yana fa'din.
“Ya Rabbi! Oh! Baby pls kiyi shiru nine ga ni kusanki ba abinda ya sameni, yi shirunki kinji?â€
Ya 'karashe mgnar yana matseta gam yana shafa bayanta bakinsa dab da kunnenta yana hura mata iska cikin 'kofar 'kunnenta.
Shiru tai tana sauke ajiyar zuciya tana sake maqaleshi ta tura kanta cikin 'kirjinsa tana shaqar daddan 'kamshinsa.
“Baby bari na ha'da miki tea ki sha OK? â€
Kai ta girgiza tana sake shigewa jikinsa.
Dogon gashinta ya tattare mata, ya 'daure da ribbon ya sumbaci tsakiyar kanta yana sake matseta jikinsa ya lullu'besu da lallausan bargo.
Sauka numfashinta yaji awuyansa ta kuma bacci cike da nutsuwa ta maqaleshi gam bata barinsa yay 'kwa'kwaran motsi kamar za'a amshe mata shi, ga shi anyi kiran sallah yana son ya yi sallar raka'atanil fajir.
Sai da ya bari baccinta yay nisa sosai ya samu ya janye jikinsa ya runguma mata pillow ya sumbaci goshinta ya kamo tafin hanunta ya shafa ya sumaci zoben hannunta yana murmushi yaja hancinta ya sauko ya shige toilet.

*Niger Tahoua*

Misalin 'karfe 8 na safe.
Inna na hura wuta tuyar waina, sai ga Dadda ita da Taslim, suna kwa'da sallama.
Inna Hansatu ta kallosu tana amsawa fuska ba yabo ba fallasa.
Tabarma ta shimfi'da musu, suka gaisa ta isa ta hura wuta.
Dadda ta ce“Hansatu dan Allah ko kinada labarin su Ja'afar tinda duk tare suke? Wlh hankalina ya tashi tin shekaran jiya Tanko ya ce zasu taso har yanzu bana samunsu awaya.â€
Inna ta gyara zamanta saman kujerata, tuyar wainarta, tana zuzuba mai acikin tandar.
“Eh Dadda jiya da dare suka iso Malam ya kira yana fa'damin, Masha Allah Ashe yarinya ta warke barka Allah tsare gaba...â€
Mahmoud ne ya shigo da sallama yana fa'din.
“Ya Ja'afar ga Innar kana jina?â€
Inna ta washe baki tana fa'din.
“Kai Masha Allah yaron albarka tinda safe ya nemi mahaifiyarsa su gaisa.â€
Ta amsa tana kara wayar akunnenta tare da sallama.
Lokacin Ja'afar suna cikin taxin baba Tsalha zasuje gidan Abie.
Amsawa yay yana gaisheta ya 'dora da cewa“Innata jiya muka sauka Alhmdllh! Ibtisam ta warke, inna umma deluwa aban ita mugaisa.â€
Inna ta washe baki ta ce“Masha Allah yaron albarka haka akeson 'da nagari Allah ya maka albarka, ina baaban naka? Deluwa ta yi sammakon zuwa asibiti bata dawo ba 'diyar 'kaninta aka riqe. Ga Dadda zauna kakar matarka tana neman labarinsu Tanko surukinka.â€
Dadda da Taslim suka kalli juna suna mamakin lamarin innar.
“Toh gata bari abata amshi Mahmoud. â€
Mahmoud ya amsa yabama dadda.
Sallama ta amsa suka gaisa cikin mutuntaka, tana tambayarsa su Ibtisam.
Ja'afar ya ce“Wlh layinsa tin jiya bai gansa ba amman suna lafiya yanzu idan na isa sai na basa wayana ya kiraku da numberki insha Allah.â€
Dadda ta masa godiya tai masa barka da arziqin samun lafiyar Ibtisam, sukayi sallama ya kashe wayar jin innar na 'kananun magana.
Dadda ta ce “Hansatou zamu tafi mun gode sosai Ashe sun dawo Tchad sai gida.â€
Ta ce “Eh insha Allah. â€
Waina zubin farko ta zube musu duka da miya, dadda ta yi godiya inna ta saka Maimou tuyar ta rakasu har 'kofa suka tafi da mamakinta akwai kirki akwai tsiya inna haka take.
Suna zuwa gida su Aydah suka baibayesu suna tambayar labarin Ibtisam da babansu.
Taslim ta ce“Kai Ramadan kamar kafimu son Baba da Anna da auntie Ibti akanmu.â€
Labari dadda ta basu sai lokacin hamkalin yaran ya kwanta sukaci wainar suna hirasu suna jiran kiran Tankon.

Acan kuwa Tchad.
Ja'afar yana zuwa bayan sun gaisa ya basa wayan ya kira Dadda, aka kira su Laraba har su sukayi hira, dadda jin murya Ibtisam harda kukanta dakyar ta lalla'bata tai shiru.
Ja'afar sai satar kallon Ibtisam yake lokacin da take wayan.
Ku'din ne da suka qare ta basa wayansa suka koma ciki, bayan sunyi breakfast Ibtisam aka koma bacci saman lafiyayyan bed.
Ja'afar kuwa can gidansu suka koma su Harisu sun ce bazasu je aiki ba, yau.
Falmata ce ta matsa ma Ja'afar tana son ganin Ibtisam, suna son zuwa ganinta ko za'a barsu su shiga gidan?
Dole ya rakasu.
Ibtisam sosai tai farin cikin ganinsu Falmata da suka tashi tafiya ta ce zata bisu da yamma sai ta dawo, Ja'afar bai hanata ba, murna ma yay zai samu damar ke'bewada ita.

A can Espagne
Abie dakyar ya samu ya tashi Rahma ya ha'da mata ruwan gumi tai wanka, tai sallah, ya bata tea ta sha ya bata mgani ta Sha. Dr ya dubata ta koma bacci wanda fafur taqi, sai jikin Abienta dole ya hkr ya mannata jikinsa ya lullu'beta ya zagaye hannayensa gadon bayanta tana baccinta anutse.
Misalin 11 Meerah ta kawo musu ha'daddan kayan breakfast ta gaishesa ya amsa tana tambayar me jiki ya ce “Da sauqi yauwa Meerah bari naje gida nayi wanka na canza kaya kafin ta tashi zo zauna kusanta.â€
Ahankali ya zameta daga jikinsa Meerah ta maye gurbinsa.
Ai kuwa ya

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login