Showing 150001 words to 153000 words out of 165653 words
ta fara bin airpor 'din da kallo wani irin shegen sanyi taji ya fara ratsata duk ta gaji, ashagwab'e ta ce“Abie qafafuna ciwo wollahi.â€
Gefen fuskarta ya shafa, cikin rad'a ya ce.
“Nasani My baby ina ankare yi hkr mu isa masaukin mu zan gasa miki sai na miki massage Ok?â€
Kanta ta d'aga tana jin sanyin k'asar na ratsata sosai, duk da ta Saba shiga k'asashen duniya amman sanyin k'asar nan na daban ne.
Bayan an gama duk abinda zasuyi na shigowa k'asar da ba takuba a Abie ya kwashe kayansu ya zuba cikin abin turawa suka nufi wajan tarbar baqi.
Wani matashin balarabe yazo tarbarsu, daga nesa Abie ya gane shine sabida sunansu b'aro b'aro.
Takardar da take riqe ahannunsa da sunan Abie and Rahma ajikinta yasa Abie ya isa wajan da sallama, saurayin ya amsa yana sakin fuska ya 'daga takarda wacce aka rubuta WELCOME.
Abie yana riqe da hannun Rahma ya ce“Thank you.â€
Kayan naso ya amsa yana turawa ya musu jagora zuwa wajan mota.
Wata irin mota mai masifar kyau, ya bu'de musu baya suka shige ya rufe, ya bu'de booth ya shigar da kayan ya zagaya ya shiga tayar da motar ya sulale yabar airport, cikin nutsuwa yake driving.........
Whtspp number😊
_*+22796515805*_
_*🤲ðŸ¼Ya Allah ka jiÆ™anmu kayi mana rahama badan halinmu ba.ðŸ™ðŸ¼*_
5/18/22, 10:58 - Buhainat: ```D A```
```100```
_Rahmerh Ladingo😉_
Cikin dauriya ya bud'e qofar ya fito falo, ya d'auko mata ruwan.
Kamar yadda ya barta haka ya sameta, ya zauna gefen gadon, ya tallabo kanta, ya bud'e gorar ruwan ya ce.
“My Honey haaaaaa.â€
Ba musu Rahma ta bud'e d'an qaramin bakinta, wanda ya yi wani irin ja ya d'an tasa.
Sannu ahankali take shan ruwan tana sauke numfashi, yana shafa kanta had'i da mata sannu.
Fiye da rabi tasha ta kauda kanta tana maida numfashi.
Abie ya ajiye sauran ruwan, ya kwantar da ita ya mik'e ya nufi bathroom.
Ruwa masu zafi ya ciki bathtub dasu, ya sakata aciki.
Ihun zafi tai tana riqe hannunsa ta saki qaramin kuka tana kiransa “Abie! Zafi.â€
Tsawonsa ya rage yana shafa kanta ya ce,“Am sorry my baby bari ki gasu zaki fasa jin ciwon Ok.â€
D'an qaramin bakinta wanda ya qara jajir ta turo gaba tana sake damqe hannunsa cikin nata, tana matsar hawaye.
Abie cike da tausayinta ya shiga lallashinta yana shanye hawayen fuskarta.
Sai da ruwan ya surke ya cireta aciki, ya sauyawa wasu, ya koma gefe ya sakarwa kansa shower, ruwa masu d'umi, suna zubo masa, sai da yay wankan tsarki tasss ya d'aura towel, ya koma wajan Rahma wacce tinda tama Abie kallo d'aya bata yarda ta sake kallon wajansa ba, ta runtse idanunta gam.
Jin ruwan sun sirke ya mata wankan tsarki da kansa, ya nad'ota a towel, ya fito da ita.
Jikinta ya goge mata ya busar mata gashinta ya shafeta da lotion mai laushi da k'amshi, ya sanya Mata wata ficiciyar riga ta bacci sai ya d'orata doguwa ta sanyi.
Sumbatar goshinta yay ya kwantar da ita ya ce“My baby na saka akawo miki tea me kauri?“
Qamqameshi Rahma tai tana hucin zazzab'i ta d'aga masa kai alamar Eh.
Bakinta ya sumbata ya kwantar da ita yana jeromata sannu, ya kira wayan sadarwa da akema 'yan hotel d'in mgna, ya sanar abinda zasu kawo musu yanzu, ya ajiye wayan ya shirya.
Ba jimawa yaji ana Danna doorbell d'in falon ya fita yaje ya bu'de ya amso.
Cikin lallashi ya bata tea had'e da cake taci ba laifi ya bata ruwa me d'an gumi tasha ya kwantar da ita, yaci shima ya kalli lokaci k'arfe d'aya na dare.
Yana son yin sallah amman agajiye yake ga zazzab'i ga Rahma na buqatar d'umin jikinsa ya kwanta ya rungumeta gam ya lullub'esu da bargo.
Yawo yake da dukkan hannunsa acikin jikinta yana mata massaging.
Tai luf ajikinsa tana sauke ajiyar zuciya sbd dad'in massage 'din.
A cikin kunnenta ya mata rad'a.
“My Honey Allah ya miki albarka nagode Allah ya biyaki da gidan aljanna, nagode da tsaremin mutuncikin da kikayi Allah ya saka miki da mafificin alkahiri, ngd ngd ngd I love you My baby my Ruhi my Honey, my heart beat. â€
Ya qarashe mgnar yana sumbatar kunnenta a sannu.
Rahma ta ce.
“Abie bacci nakeji.â€
Labb'an nata ya kamo ya tsotsa kad'an ya Saki ya qara mannesu waje d'aya ya ce“Oya muyi bacci naji zazzab'in namu ya ragu sosai Allah ya bamu lafiya my Honey. â€
Rahma bata iya amsawa ba ta sake luf jikin Abienta.
Ahaka wani dadda'an baccin ya kwashesu.
★★★★★★
*Tchad*
Jaddatu zaune da casbi ahannunta tana Ja, Hanan gefenta, tana gyarama iman gashinta, Haleesa na waya ummiterh na gyarama Zainabu faratanta, yayin da su Latifa ke kai koma wajan shirya musu abincin rana akan dining area.
Jaddatu ta ce.
“Yanzu sabida Allah yaron nan yau kwana biyu amman ace sau 'daya ya Kira tin jiya banji muryan takwara ba tana lafiya ko akasin hakan ban saniba.â€
Hanan ta ce“Kai Ummi dan Allah ai lafiya take b'uya zasu kiraki ki kwantar da hanalinki ai daman yanzu kira sai sun bushi iska.â€
Zaimabu ta ce“Oh! Rahamu kina son rigima kibar yaran nan sun sarara zasu kira ki ai.â€
Jaddatu ta ce.
“Uhmm! Ai kam shi kenan Allah yasa takwara tana lfy.â€
Haleesa ta ce.
“Ameen har Abie ma kuji Ummi da son kai.â€
Hanan ta kwashe da dariya, Jaddatu bata tanka taba.
Meerah ta zo wuce riqe da basket Wanda ake kai Abie2 abincinsa, Jaddatu ta kirata.
“Meerah!â€
Ta amsa cike da ladabi tana juyowa zuwa ga Jaddatun.
Daga nesa ta ajiye basket d'in ta qaraso cike da girmamawa ta rusuna ta ce.
“Ga ni Jaddatu.â€
Jaddatu ta ce, “Yawwa ki kiramin Abien idan kin kai masa abincin.â€
Cike da ladabi ta amsa da.
“Tom Jaddatu insha Allah.â€
Ta qarashe mgnar tana miqewa, ta 'dauki basket d'in ta wuce.
Zaune Abie 2 yake dawowarsa daga masallaci kenan, wayansa yake latsawa bakinsa na motsawa alamar yana tasbihi ga ubangijinsa.
Knocking k'ofar yaji anyi.
Ya 'daga kansa yana kallon qofar.
Wayan ya ajiye saman kujera ya miqe yaje ya bu'de 'kofar.
Idanunsu ya sarqe da na juna, yay saurin kauda kansa, kamar yadda tai tana gaishesa.
Saurin bata hanya yay, yana amsa gaisuwar tata.
Kamar yadda ta saba ajiye masa nan saman carpet, dan baicin abinci akan dining hakan tai masa ta rusuna ta ce.
“Abie2 Jaddatu na Kira ta ce na sanar maka.â€
Ta k'arasa mgnar bakinta na rawa.
Abie ya ce“Ok insha Allah.â€
Miqewa tai ta fice, ya bita da kallo dan haka kawai tinda Rahma tai masa tayinta yake jin wani irin yanayi akanta.
Gidan Ja'afar 9 pm.
Zaune Ibtisam take tana kallon Tv,
tana sanye da Riga da skirt na atamfa, shud'i me ratsin fari ta mata cif gwanin kyau, sai k'yalli takeyi abinta, kana kallonta kasan hankalinta akwance yake sai wani irin kyau, idanun k'urrr akan Tv tashar Télé Sahel Niger an saka waqar 'yan Tal national, wadda sukawa 'yan Tahoua ta Norou.
Ahankali Ibtisam take rausaya kanta tana had'a yatsunta suna bada k'washhh² SBD yadda waqar take tsumata kasancewar adarawa akama wato yarensu haka anwasa matan adarawa.
Ja'afar sanye da 3 quarter sai singlet, sai baza k'amshi yake, waya yake fitowarsa daga bedroom kenan, ya hangota tana rawa azaune tana murmushi.
Kai ya girgiza ya ce.
“Nasir Ngd insha Allahu goben zamu qarasa mgnar kamar yadda kace, Allah ya qara qaremu da dukkan sharrin abun qi.â€
Shiru yay yanajin abinda ake sanar dashi,can ya numfasa ya ce.
“Ok Merci beaucoup bon nuit.â€
Ya katse kiran ya zura wayan cikin aljihun 3quarter d'insa ya sad'ad'o ta bayan kujaran, ya zura hannayensa ya zagaye cikinta ya rankwafo da kansa ya leqo yana hura mata iskar bakinsa,ahankali can k'asa ya furta.
“Mon cÅ“ur! Duk dad'in waqan ne?â€
'yar dariya tai ta ce“Eh Mon amour ai dole bakaji ana waqemu ba, matan adarawa ga kud'i ga kyau ga fararen mata. So duk da mu talakawane Hamdan ba muni ga fari Tass.â€
Ta k'arashe mgnar tana shafa sajan fuskarsa.
Zagayowa yay ya zauna kusanta ya ware mata hannayensa.
Da sauri ta shige jikinsa tana dariya.
Ja'afar ya ce“Tabbas hakane Bebyna, amman ina ce tin ranan da abin nan ya faru nace ki daina kallon waqoqi koh?â€
Muskutawa tai ajikinsa, tana kallonsa ta ce.
“Afuwan Mon amour na daina daman ai ba wani kallon waqoqin ba sosai, kawai dai naga an saka ta garinmu ne fa!â€
Hancinta ya lakata ya ce“Na miki uzuri amman ki rage, gwada muyi abunda zai anfanemu duniya da kuma lahira ba wai nace kwata² karkiji waqaba amman ayanzu ki daina dudu yau kwana nawa da akaso asabauta min ke.â€
Ibtisam ta sumbaci labb'ansa tana kallonsa ta ce“an daina Ogana bari ma kaga.â€
Ta fad'a tana baqa hannunta tana Manne jikinsa ta janyo remote ta canza Tasha zuwa tashar sunnah Tv.
Ja'afar ya ce.
“Yawwa Matata Allah miki albarka, tashi muje yawon shan iska d'auko hijab bari na saka jallabiya saman kayana...â€
Ibtisam ta ce“A'a ni dai ka canza riga kawai mutafi wandon ya maka kyau.â€
Ta k'arasa mgnar tana shafa gashin da yake kwance k'wabrinsa tana had'awa da na k'irjinsa.
Iska mai d'umi ya fesar yana zura hannunsa cikin rigarta, ya shafo kyawawan k'irjinta yana lumshe idanunsa.
Itama lumshe idanun tai ta ce.
“Wayyo Mon amour karfa fita ta lalace...â€
Bata rufe baki ba ya ce“No! Bazata lalace ba ai ke tawace koda yaushe naso, oya je d'auko hijab ki biyomin da rigan.â€
Ya qarashe mgnar yana zaro hannunsa yana kallonta.
Kunya tasa ta miqe tana sanya gudu.
Kai ya girgiza yana binta da wani irin shu'umin kallon so and Ƙauna.
Bata jimaba ta fito sanye da hijab pinky Kala, ta basa ya cire singlet ya saka ya d'auki makullin mota ya Kama hannunta suka fice.
★★★
*Istanbul*
Tsawon kwana *hud'u* Abie na jinyar Rahma, bai sake kusantarta ba, kulawa yake bata mai yawan gaske da nuna Mata zallar soyayya mai tsayawa azuciya, hakan ya saka Rahma ta sake fad'awa tarkon son Abienta, ya shagwab'ata ya sangartata da jikinsa, sosai suke zaga garin Istanbul, wuraran tarihi da wuraran shaqatawa, duk Inda sukaje sai an kallesu sabida dacewar da sukayi da juna.
Yau dai bayan sun dawo daga yawonsu Abie ya samu ya tisa wajan yasha shagwab'a da sakalci.
Yanzu ma bayan sunyi wanka tsarki ya shiryata, ya sanya mata wasu riga da wando masu kyau wandon iya cinya rigar bakin cibinta, ya baje Mata dogon gashinta ya sauka har gadon bayanta.
Zaune suke afalon yana manne da ita yana bata pizza abaki tana ci sai sangarta take zuba masa.
“My Honey rugima ko? Toh Bby haaaaa cinye wannan sai na Kira miki Jaddatu da Abienki.â€
Jin abinda Abie ya ce cikin d'auki ta bud'e bakin ya sanya mata, ta had'a da yatsarsa, ta ciza da d'an qarfi.
“Ushhhhh! My Baby zafi ni koh?â€
Kai ta d'aga masa tana masa kallon qasa² tana tauna pizza.
Murmushi mai shegen kyau ya sakar mata, ya ce“I love you sannu fa My Honey, wai kin gajine, akwai zafi koh?â€
Baki ta b'are masa zata saka masa kuka, yay saurin tura bakinsa cikin nata ya lalubo pizzar bakinta yana wasa da ita ya kwasheta ta koma bakinsa ya shiga tura mata tana had'iyewa.
Ya sanya hannayensa dukkan biyun ya qamqame bayanta yana bugawa sannu² ya tsareta da manyan idanunsa masu sakata shiga wani yanayi.
Lumshe idanunta tai tana amsar pizzar da yake d'ura mata sai da ta ha'de tass ya fara kissing d'inta yana qara aika mata wani irin salo yana murza k'ugunta zuwa bayanta had'e da manmatsa. mata kowace gab'a ta jikinta, still yana shan bakinta.
Rahma ta kasa jure kallon da yake mata, ta lumshe idanunta ahankali ta cije shi a harshensa.
Bakinsa ya zare anata ahankali, yana mata wani irin fitinannan kallon k'auna, ya furta.
“Ushhhhh! Baby love zaki cinyeni ne?â€
Da sauri ta bud'e kyawawan k'ananun idanunta, tana turo baki gaba ta ce.
“Abie Kira mun Jaddatun toh da Abie2.â€
Kissing d'in idonta yay yana shafa kumatunta ya ce“Okay my baby love gsky yau kin kusa mantar Dani ni waye zuwa dare babyna zaki qaromin pls?â€
Kukan shagwab'a ta sakar masa tana qoqarin zamewa daga jikinsa, yay saurin rungumeta qam, yana dariya ya ce.
“Sorry My Honey wasa nake miki bazan tab'a cutar da Ruhina ba, oya zo na Kira miki Jaddatunki.â€
Ya qarasa mgnar yana sumbatar tsakiyar kanta yana shafa bayanta.
Luf tai k'irjin Abienta tana jin gajiyar turmusar da yamata yanzu kusan awa 'daya yana abu d'aya sai taji yanzu duk tsamin da jikinta yay ya fara sakinta.
Hannunta ta tura cikin sumar kansa mai taushi ashagwab'e ta ce.
“Abie...â€
Bakinsa ya d'ora saman nata ido cikin ido ya ce“Na soke Abie daga yau yau kwana nawa ina bin kanki ki saka min wani sunan? Toh idan bazaki saka min wani sunan ba kina kirana da Abdulmajid sak OK? â€
Rahma ta ware kyawawan k'ananun idanunta ta ce.
“Wayyo na shiga uku Rabin raina kayi hkr, ni ina zan Iya Kama sunan garkuwata qiri² tabbb wlh bazan tab'a ba, amman kamin Afuwa zan saka ma wani sunan amman Abien yabi jinin jikina bazan Iya daina ba, zan gama ba Abienah.
“My sweet darling yayi koh?â€.
Ta qarasa mgnar agajiye tana tura kanta tsakiyar k'irjinsa.
Tattausan murmushi yay yana sumbata tsakiyar kanta, ya ce.
“Yes yayi my baby love Ngd.â€
Ya k'arasa mgnar yana dialing d'in number Jaddatu, ya sake matseta jikinsa, jin wayan ta fara ringing ya saitai nutsuwarsa.
Sallamar Jaddatu ta kard'e dodon kunnensa, tana fad'in.
“Kai Abdul! Sbd Allah duk kana ina Baku Kira idan an Kira ba'a samunku?â€
Abie ya amsa sallamar ya d'ora da cewa.
“Afuwan ummina ina wuni barka da yamma, ga baby Ummi.â€
Jaddatu daga Chan ta ce.
“Bani ita naji lafiyarta....â€
★‡★
*Gabon*
Ma'aruf ya shiga muguwar damuwa akan dukiyarsa da wuta ta cinye.
Ganin hakan yasa Aishatu ta sauko daga dokin fushin da take da shi, ta shiga masa nasiha tana kwantar masa da hankali, dangi kowa hankalinsa ya tashi, dan ayanzu Ma'aruf ko maganin rabin million 'daya bazai maka ba, dan account d'insa 'yan canji ne kawai.
Zaune take kusansa tana basa abinci abaki Wanda idan ba hakan tai ba tana lallashinsa bai ma damu da yaci ba, duk da kuwa ya fawwalawa Allah kominsa na shi yasan alhakine yake binsa.
Asanyaye ya ce.
“Masoyiya na qoshi bari nayi wanka muje gida mu gaishesu.â€
Hannunsa ta Kama ta ce.
“Don Allah ka Saki ranka bafa aja da ikon Allah jarabawace idan ka cinyeta sai Allah ya maka falalar da baka tab'a zatoba, amman idan ka damun sai ya barka da damuwarka don Allah ka manta komai.â€
Rungumeta yay yana buga bayanta yace“Wlh ba komai na barma Allah komai ikonsa ne yanada ikon yimin hukuncin da yafi wannan sabida na sab'a masa dayawa daman kuma baka tab'a Allah kace kaci bulus.â€
“Hakane amman ai ka tuba kuma Allah gafuru rahim ne, insha Allah zai kalleka da idon Rahma muje ka shirya.â€
Bedroom suka nufa sai suka Fara jin ihu, Ana buga musu 'kofa.
Ma'aruf jikinsa na rawa ya nufi k'ofar aguje hankalinsa atashe yana fad'in.
“Ko wata musibar ce ta sauko min hallau.....â€
_*+22796515805*_
_*🤲ðŸ¼Ya Allah ka jiÆ™anmu kayi mana rahama badan halinmu ba.ðŸ™ðŸ¼*_
5/24/22, 15:22 - Fiddausi Yunus left
5/27/22, 10:51 - Buhainat: ```D A```
```101```
_Rahmerh Ladingo😉_
_*Alhamdulillahi Am backðŸ‡ðŸ»*_
😅🙈🥳😒🚶ðŸ»â€â™€ï¸
Ma'aruf na bud'e k'ofar falon yaci karo da Nura direba tare da mai gadi, hankalinsu atashe.
Ma'aruf ya ce.
“Wai lafiya? Me ya faru ne?â€
Nura ya ce“Yallab'ai ga mota can ta kama da wuta a qofar gida, zanje aiken da ka kamin, ta Kama da wuta Allah yay da kwana na gaba na fito cikin hukuncin Allah, ba yadda bamuyi ba mu kasheta taqi mutuwa, ga jama'a chan na famar kashewa .â€
Ma'aruf banda sunan Allah babu abinda yake fad'a, bakida 'daya ma duk wasu addu'o'i da ya sani ya ji sun tsaya masa cak, jikinsa na rawa ya nufi hanyar wajan, suna biye da shi.
Aishatu da take tsaye a k'ofar falon tai zaman 'yan buri, ta d'ore hannayenta saman fuskarta, tana fad'in.
“Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un! Allahumma ajirni fi musibatihi waklifni khairan minha!â€
Ta k'arashe cikin sakin kuka zuwa yanzu Ma'aruf na bata mugun tausayi tabbas ya had'u da iftila dayawa.
Miqewa tai ta koma ta d'auko hijab ta saka ta fito.
Ma'aruf yana tsaye yana kallon 'yan kwana-kwana suna kashe wutar, Wanda mak'ocinsa Salisu ne yay wannan jihadin na kiran 'yan kwana-kwana.
Motar ta k'one sosai ba lallai ta anfana ba.
Aishatu ganin yadda Ma'aruf yake tsage kamar gumki, sai jaje jama'a suke masa yana d'aga musu kai, ya saka ta isa wajan ta Kama hannunsa suka shigo cikin gida har wasu na biyosu suna k'ara masa jaje.
Mai gadi ya rufe gidan, yayin da Nura yake tsaye wajan motan da ta kusan cinyewa k'urmus, dan ba lallai ta anfana ba.
Zaunar da shi tai saman kujera a falon, taje fridge ta d'auko ruwan sanyi,ta bud'e ta kafa masa bakinsa.
“Please kasha.â€
Ba musu ya dinga kwankwad'an ruwan sanyin, sai da yasha kusan rabi, ta janye masa goran ruwan daga bakinsa, ta Kama hannayensa ta ce.
“Kayi hkr babu wani abu da yake wanzuwa adoron duniya ba tare da izinin Allah ba! Dan haka kayi hkr ka amshi dukkan jarabawarka wana Allah zai wanke ma dukkan zunubanka ne ta wannan hanyar, amman ba wai na Tara Sani ga ubangiji na bane, ka tattara komai ka barwa Allah, kayi ta maimaita.
Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un! Allahumma ajirni fi musibatihi waklifni khairan minha, Allah ya bamu ikon cinye jarabawarmu.â€
Ma'aruf ya rungumeta, gam yana sauke numfashi, cikin aro jarumtarsa ya ce.
“Wallahi Aishatu na amshi dukkan k'addarata tinda dai ina tare dake Alhmdllh!â€
Sake rungumeshi tai ta ce“Allah ya bamu juriyar cinye dukkan jarabawar da Allah zai jarabemu da ita.â€
Ya amsa da.
“Ameen ya Allah.â€
Rabi'ah zaune da cup d'in kunnun tsamiya, Wanda ta saba, duk ta rame sbd yadda cikin yake bata mutuqar wahala, sai wani uban fari da tayi.
Kunnuwa ta kasa kiskirin, tana jin mamanta da yayanta Murtala suna mgna, qasa².
“ Murtala! Wlh da akwai inda zan kai Rabi'ah da na kaita, ganinta agidan nan ba qaramin baqanta min rai yake ba, Allah kana gani kai shedane akan yadda nabawa yarana tarbiya, amman shegiyar yarinyar nan, tai watsi da tarbiyar dana basu taje ta kwaso min abun kuya, ya Allah kamun maganin wannan masifa da ta tunkaro mu...â€
Murtala ya katseta ta hanyar cewa.
“Maama dan Allah kiyi hkr, mu rungumi k'addara, ina zamu turata? Mu muna gudun abin kunya sai muturawa wasu ai sam hakan baiba, kowa yasan gidanmu munada nutsuwa da tarbiya ita da taje ta kwaso abin kunyarta ita da shi, mu rage nuna mata qyama, sabida ba wanda ya isa ya wuce k'addarasa, amman ita wannan koh, Allah ya rufa asiri kawai.â€
Mama ta amsa da.
“Ameen.†ranta duk ajagule.
Rabi'ah hawayen da take dannewa ne suka sulalo, ta sanya tafin hannunta ta goge, dakyr ta iya bud'e busashen bakinta ta furta, “Astagfirullah wa'atubu ilaik.â€
jin motsin Murtala zai shigo d'akin tai saurin ajiye cup d'in ta miqe ta shiga bedroom, tana danne kukanta.
*Istanbul*
Akwana tashi ba wuya wajan Allah
Abie da Rahma,