Showing 162001 words to 165000 words out of 165653 words
bazai barsu a motarsa zasu zo wacce aka dubata sabida yasan abanza zasuci kwana uku ahanya.
Lokacin da yazoma Abie sallama zai tafi ba qaramin alkahiri Abie ya masa ba duk wata hidima da za'ayi ta suna ya d'aukar masa nauyinta komai ya basa yaqi karb'a sabida ayanzu yannada rufin asirinsa, amman ganin Abie ya b'ata ransa dole ya amsa, yay godiya.
Ai kuw kwanansu uku ahanya kafin su iso.
Inna sai tattalin Ja'afar ake an kasa zaune an kasa tsaye.
Ibtisam na shayar da yaron taji daga tsakar gida Laraba tna fad'in.
“Ah Ja'afar zauwar yaushe?â€
Zazzaqar muryasa taji yana gaisheta ya ce.
“Yau d'azu muka shigo Anna fatan mum sameku lafiya ya masu jiki?â€
Laraba ta amsa da lafiya bismillah ka shiga tana d'akinsu.â€
Ibtisam tai saurin zarema yaron nono ta kwantar da shi tai saurin kwnciya ta rufe idnunta.
Da sallamaa ya shogo d'akin kallo d'aya yay mata ya gane baccin qarya takeyi.
Murmushi yay ya d'auki yaron ya zauna dab da ita.
Idanu ya qurama yaron sam baiga wani banbancinsa ba da yaron, komai nasane yaron ya d'auko.
Bakinsa ya manna kunnen yaron yay masa addu'a duk da yasan anyimasa, sannan yay masa huduba da sunan mahaifinsa Adam.
Kuka yaron ya tsala, yay saurin mirgino Ibtisam ya janye rigarta ya saita masa abincinsa ya kuwa kame yana tsotsa.
Ibtisam ta qyalqyale da dariya ta ce.
“Idanuna biyu fa! Mon amour sannu da zuwa ya gajiya?â€
Rungumeta yay ya ce“Hahaha nasani Mon cherie, sannunki nagode sosai fa kinyi qoqari haifomin gwarzon namiji Allah yasa bad'i warhaka ki qaromin twins... â€
Dukan wasa ta kai masa tana kwab'e fuska ta ce“A'a gaskiya...â€
Masha Allah ranan suna anyi suna mai qayatarwa, suna yayi armashi Ja'afar da iyayansa sunyi komai na bajinta anci ansha, kowa na son barka yaro yaci sunan mahaifin Ja'afar Adam, ana kiransa da Rafael.
Ja'afar satinsa d'aya ya koma tchad wajan aikinsa Inda ya tafi yabar Ibtisam da iyayansa da 'yan uwansa da kewarsa.
Haka Ibtisam taci gaba da wankan ruwan zafi tana samun kulawa sosai ita da yaronta Rafael.
Acan kuwa Chad.
Rahma nada sati biyu da haihuwa akayi suna, an yanka raguna anyi abinci an raba sadaka tinda Rahma da Yara na asibuti anabasu kulawa.
Sai da suka kwashe wata biyu a hospital ana kulawa da yaranta wandan ayanzu sunyi mulmul sunyi wani irin qiba kamar ba bakwaini ba amman doctor ya ce baza'a sallamesu ba sai yaran sun cika wata uku sunga ba wata matsala.
Rayyana cikin wata hud'u da aure tayi wani irin kyau sabida wani irin so Nafi'u yake mata, sabida yadda ta kwantar da hankalinta tana binsa sau da k'afa, tana bin matansa a kullun sai ta shiga b'angaransu sun gaisa haka tana son yaransa hakan ba k'aramata kima yay wajansa ba.
Yau ita ce me girki tin k'arfe uku ta shiga kitchen ta fara shirya masa dadd'an abinci.
Misalin k'arfe 9 zaune take a falonta Wanda yasha turaren wuta sai qamshi yake, taci kwalliya tsaf abinta, sai yamutsa fuska take sabida mugun tashin zuciyar da ya sakata gaba tin yamma dakyar ta kammala girkin da yamma.
Kanta taji ya Sara mata ta dafe tana fad'in.
“Washhhh! Anya ba ciki gareni ba?â€
Ta tambayi kanta tana miqewa tsaye jin qaran buga qofar falonta.
Tana bud'ewa suka had'a idanu da Waheeda, wani irin tsalle tai ta dire gefe ta ce.
“A'uzubillahi minan shed'anin rajin bismillahi rahamanir rahim. Dan ubanki fitarmin agidana.â€
Waheeda ta zube qasa tana riqe k'afafun Rayyana tana fashewa da kuka ta ce.
“Don Allah ki yafeni wlh naga jarabawar ko nace miki naga sakayya bakiga yadda nakoma ba wlh alhakinku ne na qara nadamane Ajiya labarin irin hukincin da Allah yayima Malam yanzu haka yana yawo tsirara kasuwa² yana fad'in abubuwan da shuka arayuwarsa don Allah ki yafeni bazan sake ba na tuba wlh kowa guduna yake dan Allah ku yafemin...â€
Rayyana ta ingijeta da k'arfinta tace.
“Bani bake karki sake kallon titin gidana ma, kije na yafe miki amman babu alaqa ko ta gaisuwa tsakanina dake.â€
Rayyana ta qarasa mgnar tana turata ta janyo qofarta ta murza key taji zuciyarta na tashi ta nufi toilet aguje ta fara amai kamar zata amayar da hanjin cikinta.
Awahalce ta fito tana maida numfashi taji ana knocking.
Awahalce ta isa ta bud'e.
Ganinsa ta afka jikinsa tana sauke numfashi.
Alhaji Nafi'u ya tarairayota jikinsa yana fad'in.
“Subahanallahi Habibiya bakida lafiya ne?â€
Kai ta d'aga masa tana narkewa ajikinsa.
Alhaji Nafi'u duk ya rud'e sai tattab'ata yake ya ce.
“Muje ki saka hijab muje hospital.
Rayyana bata musaba tafison ta tabbatar da zarginta.
Aikuwa suna zuwa asibiti gwajin farko Rayyana na d'auke da cikin sati hud'u.
Wai karkaso kuga farin ciki wajan alhaji Nafi'u tamkar yau za'a fara masa haihuwa, kaf iyalansa ba wanda baiji ba wannan cikin, hajiya Sha'awanatu har mamaki take duk da tasansa mutum mai son 'ya'ya sosai.
Wannan dare sun rayasa cike da wata irin soyayya ko motsi tai zai tambayeta me takeso, Rayyana banda godiyar Allah ba abinda takeyi, dan ita kanta tazan ta samu mijin da kowace macs zataso mallakarsa.
*Gabon*
Aishatu zaune a falo tana shirya Farook yaro d'an kusan kimanin wata 4 yayi wata irin qiba me burgewa fari Tass da shi masha Allah.
Sai yakushin Aishatu yake yana dariya, tsantsar kamarsa ta sake bayyana da Ma'aruf.
Kumatunsa taja tana dariya ta ce.
“Idan ka ciremun idanu naga wa zai maka wasa ja'irin d'ana kawai...â€
Shi dai dariya yake ya fara qoqarin sanya hannunsa cikin rigarta.
“Uwani! So don Allah kamamun yaron nan naje na shirya mutafi kasuwar nan.â€
Ta k'arashe magana tana sanya masa takalmi.
Uwani ta iso tana sanya hannu zata d'aukesa ya qamqame Aishatu ya sanya kuka.
“Ai kam kin sansa da naci bazai jeba je abinki Dadynsa zai fito yanzu ne.â€
Ta k'arashe mgnar tana janye rigarta ta fara shayar da shi.
Uwani ta tattare kayan da aka ciremasa ta gyara wajan ta tafi.
Ma'aruf ya fito cikin shirnsa yayi kyau sosai ya zauna kusan Aishatu yana sumbatar wuyanta, ya ce.
“Eh lallai zaku hau taxi kuwa tafiyata zanyi idan kin biya D'an nan naki komai bazakiyi ba!â€
Ya fad'a yana Jan hancin Farook, ya saki Maman yana b'angala masa dariya.
“Yauwa toh riqesa ban 5 minutes na shirya.â€
Ma'aruf kallonta yake cike da tsantsar k'aunarta ya riqe fuskarta da tafukan hannunsa yana fad'in.
“Haqiqa da na rasa amatsayin matata nayi babbar asara wlh samun irinki aduniyar nan ta yanzu akwai wahala, banida bakin da zan miki godiya sai da na miki fatan gamawa da duniya lafiya, ubangiji ya bamu zuri'a dayyaba.â€
Ya qarasa mgnar yana sumbatar bakinta.
Aishatu ta ce.
“Ameen ya Allah Abban Farook mijin AISHA. â€
Dariya suka sanya suna rungume junansu, yaronsu na tsakiya shima dariyar yake b'angalawa, Aishatu ta ce.
“Oya je wajan Abba na shirya.â€
Ta k'are mgnar tana beqawa Ma'aruf shi ta shiga ta shirya ta Kira Uwani suka tafi akasuwa ya ajiyesu ya wuce shagon gwanjonsa Wanda yanzu abun ya bunqasa yaransa ma mutum biyar ne sari d'aurin dila kawai yake bayarwa an daina siyar da guda².
Daga kasuwa suka biya gidansu Rabi'ah sun jima sosai acan kafin daga can suka wuce gidansu Ma'aruf, qarshe suka yada zango gidansu Aishatun sai dare Ma'aruf yazo ya tafi dasu gida.
Rahma yadda suke samun kulawa da yaranta abin ba'a cewa komai ita kanta tayi mulmul sai kewar soyayyar Abienta ke d'awainiya da ita, sabida bakinsa da ita sai gaisuwa Jaddatu da Ummu Adnan suke kula da ita yaran kuwa likitoci bakinsu da ita susha nono.
Ahaka Jaddatu tayi qoqarin sake shirya Rahma ta mata gyara sosai a asibitin dan tasan Ana sakinsu ba saurara mata Abie zai ba.
Abie ya qara bud'e makarutun boko da islamiyya, sadaka da manyan masalllatai biyu da sunan 'ya'yansa, an kammala ginin asibitin Rahma an zuba makaita k'wararrun likitoci, Abie ya soke karatun Rahma ya ce baya buqata ba magnar idan yaranta sunyi wayo taci gaba.
Sadaka kamar yadda ya Saba duk juma'a k'ofar gidansa acike take har gobe hakane baya fashi hakan ba qaramin d'aukakasa ya qara yiba.
Yau 'diyan Rahma suka cika wata uku cif yau aka sallamesu daga hospital idan kaga murna wajan Rahma da Abie abin baya fad'uwa.
idan kunga yadda Abdulwahab wanda suke kiransa da Dady UmmulAymana kuwa da Mamy suke kiranta masha Allah idan ka kallesu sai ka kuma bazaka tab'a cewa bakwain ne ba sunyi wani irin girma da wayo gasu da dariya Dady kuwa akwai shan yatsa.
Ibtisma ma ayau suka iso Chad Ja'afar yaje ya kawosu, masha Allah ita da 'danta sunyi wani irin girma yaron tamkar yakai wata hud'u katone sosai ga shi baida kuka.
Tinda suka iso taba Ja'afar Rafael ya kaisa gidan Baba Tsalha ita kuma ta shiga gyaran gidanta kafin yamma tsaf ta gyara ko ina ta d'aura musu girki.
Ibtisam ta fito daga wanka d'aure da towel take jiyo kukan Rafael, murmushi tai ta ce“Ai kam yaron nan yayi qoqari ai kam da ya bari naje.â€
Qaran bud'e k'ofa taji ta waigo,tana goge jikinta da qaramin towel.
Idanu suka had'a da J'afar ya shigo d'akin yana rungume da Rafael, yana tsala kuka.
Dariya tai tana fad'in.
“Mon Amour haka ake reno? Ka wani matse yaro.â€
Wani irin kallo mai cike da so da sha'awa da k'auna yake aika mata.
Fari tai da idanu tana d'aga masa gira.
Da sassarfa ya qaraso wajanta ya had'asu da yaron ya manne aqirjinsa.
D'an qara tai tana kallonsa.
Gira ya d'ga mata ya ce“Kinci bashi zuwa dare, oya basa abincinsa.â€
Amsarsa tai tana zama gefen gado ta fara shayar da yaron ashagawab'e ta ce.
“Mon amour yaushe zamu je gaishe da da Baba Tsalha da Jaddatu daga can nagano auntie Rahma?â€
“Zuwa gobe insha Allahu, yau sai kin biya bashi.â€
Ya k'arashe mgnar yana sumbatar wuyanta yana shafa fuskarta.
Dariya kawai take masa ganin yadda ya wani sakata gaba yana matsata ita dai yaronta take shayarwa.
Rahma tinda sukazo gida tai wanka ta shirya cikin riga da skirt na material tayi wani irin kyau tamkar Dady da Mamy ba daga tsatsonta suka fito ba.
Zaune suke a babban falon tana kallon yadda aka sake canza komai na falon, Merrah na wasa da Many tana b'angala dariya, Dady kuwa na wajan Jaddatu ta Hana kowa d'aukanta yaron baya gundurata.
Abie ne ya shigo yana waya.
Idanu suka taurawa juna shi da Rahma.
Kai ta langwab'ar tana tutturo masa bakinta, da idanu tana take masa magana.
Murmushi mai taushi ya sakar mata, yana d'aga mata gira ya qaraso falon ya nufi wajan Mamy tana harba k'afafu ya sunkuya ya amsheta hannun Meerah yana murmushi ya sumabceta ya ce“Aymana wayo koh?â€
Meerah tai dariya ta ce.
“Masha Allah kamar sunyi wata hud'u ko biyar.â€
Murmushi yay ya nufi wajan Jaddatu ya zauna, yana kallon Dady yanajin tsananin k'aunar yaran har cikin jininsa.
“Ok Mustapah karka wani damu komai zaiyi daidai insha Allah, ngd ok bye zuwa jibi inada meeting a mexico da na dawo za'a San abunyi.â€
Jaddatu ta ce“Allah ya qara rufa maka asiri ya mama albarka.â€
Rungumeta yay ita da Dady ya amsa da.
“Ameen Ummina.â€
Ya k'arashe mgnar yana kallon Rahma wacce ta shagwab'e fuska tana kallon Mamy na harbe-harbenta, Meerah na mata wasa.
Miqewa Rahma tai irin tayi fushi Abie yaqi mata mgna ta haura sama.
Jaddatu ta ce.
“Takwara ina zaki? kije da Aymana ki bata Tasha, kinji doctor ya ce kar abarsu suna jin yunwa naga baki basu mono ba tinda mukazo madaran ma basu shaba sosai.â€
Rahma ta dawo ta zauna ta ce.
“Ummi da kwanciya zanyi kaina naji yana ciwo kad'an.â€
Abie danne dariyarsa yay yasan k'arya take fushi tai.
Jaddatu ta ce.
“Subahanallahi sannu to ki shayar dasu ki barsu sai kije ki kwanta, Abdul d'auko mata magani.â€
Rahma ta mashi Mamy ta fara shayar da ita.
Yarinyar tana Sha tana kallon Rahma k'urrr Rahma ahankali ta ce.
“Mamana kallo koh?â€
Karaf akunnen Abie.
Tana shayar dasu ta barsu ta haye sama bedroom d'insu wacce basa Iya rabawa ita da Abie ta shiga ta Mirza key tai kwanciyarta tanajinsa yazo taqi bud'ewa Abie abun dariya ya basa shi ssam baiga abinda ya mata ba Har dare Rahma fushi take da Abie,
Bayan yaran sunyi bacci Rahma kwantar da kowane saman gadonsa taje tai wanka ta shiyar cikin wasu irn kayan bacci masu masifar kyau, tana wani irin k'amshi.
Abie na falo zaune waya yake yana Danna laptop.
Wani irin qamshinta ya daki hancisa yay saurin d'ago da kansa ya kalleta.
Kai ta d'auke tana turo baki, sai wani irin taku takeyi jikinta ko ina motsawa yakeyi kayan jikinta na bacci basuda maraba da tsirara, gabansa tazo ta gifta tana qoqarin nufar hanyar fita.
Da sauri Abie ya miqe yana fad'in.
“Hamza! Wani uzuri ya taso min gobe insha Allahu zamuyi mgna.â€
Bai tsaya jin abinda Hamza zai ce ba ya katse kiran ya jefar da wayan kan sofa ya nufi wajanta da sassarfa ya damqo hannunta ya juyo da ita gabansa ya riqo k'ugunta ya mannata da k'irjinsa ya tura fuskarsa tsakanin k'irjinta yana shafa k'ugunta can k'asa² ya ce.
“My baby me nayi take fushi Dani haka? Haba my honey wata uku bama keb'ewa yau kuma kina fushi da Abienki abin sonki?â€
Kukan shagwab'a ta saka masa ta ce.
“Yo My Abieh ba kaibane ka wani shareni d'azu da yamma yaranka kawai ka kula, ni kuma inata kewarka inata missing d'inka inata sonka my Sweety darling. â€
Ta k'arashe mganr tana kallonsa tana turo baki.
Abie ya d'auketa sama yana juyi da ita tsakiyar falon ya ce“Wallahi nafi damuwa dake nafi sonki akan yaranmu ki Lura mana babyna Ummina na wajan ba daman na rungumeki na miki kiss yanzu dai yi hkr na amshi laifina OK? â€
Ashagwab'e ta ce “Ok naji toh goyani.â€
Bayansa ya sab'ata yana zagaya falon da ita tana b'angala dariya, kamar wata baby ya nufi bedroom d ita.
Kwantar da ita yay ya nufi wajan yaransu ya tofesu da addu'a ya dawo ya kashe wutan d'akin ya haye bed qamqame juna sukayi suna murmushi Abie ya fara cire kayan jikinta yanabi ko ina nata da kiss na fece sabida yau aikin babbane.
B'angaran Ja'afar ma da Ibtisam yau sun raya darwn ciki da dumbin tarihi sun gurji junansu.
Washegari Rahma jikinta ko ina ciwo yake mata sabida da asubaha ma bayan sallah sai da yay making love.
Misalin goma ta farka lokacin Abie ya shirya yaran yazo ya sanyasu gabanta ya basu abincinsu saida suka k'oshi ya kaisu wajan Jaddatu.
Breakfast tai ta sake shayar da yaran ta ta barsu ta tafi b'angaran Meerah.
Bayan wata d'aya, Rahma yaranta tsotsa yanzuma tserewa tai b'angaran Abie2 ta barosu wajan Jaddatu.
Iskowa tai Meerah ba lafiya zazzab'i sun dawo daga asibitin ciki wata biyu.
Rahma tai ihu ta b'ire kan Abie2 tana fad'in.
Abie2 nah Ashe bayan kai zan sake ganin dangin Mamyna.?â€
Abie2 yay murmushi ya ce.
“Rahma bakya girma ai mu kam tinda munada Abie da Ummi sun ishemu sune komai namu ga kuma Meerah zata fara bamu sabuwar zuri'ah.â€
Meerah ta ce.
“Ni kun wareni kenan?â€
Rahma ta Saki Abie2 ta rungume Meerah ta ce“Ai kam kallon Abie nake miki har abadan mamyna.â€
Dariya sukayi nan sukaci gaba da hirasu sai da Abie2 ya kori Rahma dan batada niyar tafiya.
Kwance tashi ba wuya har Allah ya sauki Rayyana lafiya ta samu 'ya mace mai kyau wace ta d'auko baqin mahaifinta amman sosai tana Kama da Rayyana. An samu Asma'ulhusna, sosai take samun kulawa wajan mijinta yarinyarta kuwa ita kanta tasna tanada gata wajan yayunta.
Auntien saro ma ta samu wani dattijo na gari tayi aure suna zaune lafiya bata rufe wata shidda ba itama ciki ya b'ullo.
Aishatu Gabon itama tanada ciki haihuwa yau ko gobe sai muce Allah ya raba lafiya. Ma'aruf yanzu kam.kud'i Hamdan ba laifi sunfi qarfin abincinsu motar hawa sutura ga shi da bayar da sadaka Farook anyi wayo sosai masha Allah.
Meerah ma ciki ya tsufa taso zuwa gida haihuwa Rahma ta roqeta ta bari bayan haihuwarta zasuje tare itama tana son zuwa ganinsu Abby Morocco.
Ibtisam da Ja'afar anata zuba love suna renon Rafael sai wayo yake masha Allah yana tafiyarsa ko ina kamaninsa da Ja'afar na qara fitowa.
Masha Allah Ja'afar harakan kasuwancinsu na company na k'ara hab'aka, addu'a ba dare ba Rana duk wani me nemansu da sharri Allah ya tsaresu.
Harisu anyi bikinsa da Maimuna k'anwar Ja'afar, Taslim ta samu wani yaro mai shegen kud'i ga hankali bikinsu watan gobe su Ibtisam sai shirye² tafiya akeyi.
Inna yanzu masha Allah an FASA tuyar waina Ja'afar ya hana tin kafin auren Maimuna ya kashe gidansu an yimusu gini mai kyau na zamani abun sai Wanda yagani Mal Adamu ma ya hanasa siyar da ruwan duk da yaqi yana zuwa abinsa, ya ce baya son zaman gida hakan bai saba.
Mahmoud ma a samu aikinsa ba laifi shima bayan sallar azumi bikinsa da wata yarin nan bayan layinsu.
Jaddatu Alhmllah zamu sabida tana qoqarin kulawa da Rahma da Abien, jikin tsufa yau da lafiya gobe jiki ya tab'u haka lamarin yake amman masha allahu har yanzu da k'warinta.
Sosai Ibtisam da Rahma suke zumunci masha Allahu, Abie ya d'auki Ja'afar kamar d'an uwansa.
Rahma tsaye ta fito da wanka.
Idanu ta zaro ganin Dady da Mamy tsaye suna janyo kayan kwaliyarta suna watsarwa, sunyi baja-baja da kayan dressing mirror.
“Wayyo ni Rahama na shiga uku Yara wata goma Sha uku amman sun iya shegiyar b'arna haka sabida Allah, wlh sai na zaneku.â€
Ta k'arashe mganr tana nufar wajansu aguje suna ihu suka fita suka nufi falo ta biyosu.
Jikin Abie suka fad'a suna sakin kuka.
Turis ta tsaya tana hararensu.
Abie ya ce.
“Don Allah Baby kije Allah ya baki hkr zan biyaki abinda suka lalata kinji amman bar raza min su.â€
Baki ta zumb'uro ta ce.
“Ai wallahi daman nasan ni yanzu tawa ta qare baka sona sai Dady da Mamy.â€
Ta k'arashe mgnar tana juyawa bedroom.
Dariya Abie yay yana rungume yaran ya ce.
“Ku kam Allah ya shiryamin Ku kuna d'aukomin mgna wajan Manmmy yanzu dai cikin wata biyun nan ramuwa nawa kuka sakani wajanta?â€
Dariya kawai sukeyi dan basu Iya magana ba sam.
Miqewa yay dasu ajikinsa ya fice ya kawai Jaddatu su ya dawo yay rarrashi.
Zama yay a falon har ta fito.
Tsaf ta shirya cikin doguwar riga maroon colour tasha adon stones falo ta isko Abie yana waya.
Saman cinyarsa ta zauna ta zagaye hannayenta bayansa ta kwantar da kanta a 'kirjinsa, ta ce.
“Ba ni ba dai Sweet darling. â€
Abie ya matseta ya ce.
“Yes my baby love bakeba ya lafiyar babyna hope baya baki wahala?â€
Rahma tai saurin kame bakin Abie ta shiga masa wani irin kissing Wanda ta kusa haukatashi yaje maida martani ta zame ta zuba aguje tana fad'in haka kawai Abie sai ka k'ullamin sharrin ciki bayan rasss nake yaran da ko nono basu gama shaba zakace inada ciki bayan banyi kwana 20 da gama period ba.â€
Ta k'arashe mganr ashagwab'e ta hararesa, sai kuma ta dawo wajansa ta