Showing 30001 words to 33000 words out of 142410 words
ta yaya ma haka zai faru .
Nan dai ya watsar da maganan ya ci gaba da aikin dake gaban shi sai dai yanayi yana tuna zancen a zuciyar shi.
Kai tsaye da na fito kamar yadda na saba gidan da muke na nufa yau yawan ci basu da lectures sai karan gida ke tashi ko ina a cikin gida.
Yunwa nake ji don ban tsaya nayi karin kwarai ba da safe sallah nayi sana fara hada tea na nasha sai da na dan huta a wurin na mike ina sauya kayan jikina.
Na saka dan guntun rigan da nake zama a daki dashi gyaran dakin nayi na gyaro ko ina na dakin sai na dora girkin dare don shinkafa da miya nake son yi irin na yan makaranta.
Bayan na gama miya na dora shinkafan na koma na zauna a bakin katifa ina tunane zarah ne ta fado min a rai yau in zan lissafa kwananta biyar bata dawo ba.
Zarah tana daya daga cikin "ya"ya dake cin amanan iyayyen su don babu inda suka rageta don koba a fada ba zarah tafi gata don sati biyu bai shigewa iyayyen ta basu turo mata da sako ba.
Amma duk ta watsar da wanan gatan nata tabi ra,ayin kwadan abin hannun samari wanda ya rufe mata ido a yanzu har yakai ga ta watsar da karatun ta.
Ido na lumshe tare da girgiza kaina ina cewa ubangiji katsare mu ka karemu ya Allah kasa mufi karfin zuciyar mu don yanzu rayuwa abin tsorone .
Sai gata washe gari ta dawo dakina ta nufa don karban key din ta koda ta shige ban sake mata fuska ba daga inda nake kwance ta tambayi key din ta na nuna mata da hannu kawai ta nufi wurin ta dauka.
Harara na bita dashi tana ficewa daga dakin andan jima kadan sai gata ta dawo dakin daga ita sai wani dan guntun tawul da ta daura iya cinyan ta tana tambayana wai ban rage abinci ba in bata.
Wani kallo nayi mata nace inda kika fito gantalin ki kwana da kwanaki baki kici abinci bane acan ?
Tace kin san yanzu wata yayi nisa ba wani abin kirki ake samu ba sai maneji nace sai ki je gaba ki nema ni banyi abinci ba yau.
Ta ce khady yaushe kika fara rowa haka ba halinki bane rowa nace ban dafa ba nace maki ashe karyan iskanci kike yi da zaki dawo kwana da kwanaki hannu empty.
Ta dan tsaya jin ganin ban kulataba ina karatuna sai ta fice min daga dakin dagowa nayi nabita da kallon mai kama da harara har tafice daga dakin.
Bayan ya gama saurare abinda malam sani ya gaya mashi jikin shi ne yayi sanyi karshe yayi mai godiya tare da jaddada mashi kan kada ya fada ma Nafisa komai ya dai saka ido ga alamarin ta kawai.
Bayan fitan shi gidan nine na fado mashi a rai wayana ya kira mun gaisa dayake shi mai son wasa ne nan yajani da wasa wanda bai wuce hiran mijin buzuwa.
Yace gobe dai weekend ne ba shiga aji ke nan nace eh sai dai ina son zan fita zuwa wurin wankin kai don ina son gyaran jiki gobe dai.
Yace ashe shi gyaran ma sai anje wani guri yin shi dariya yaban don irin zolayar shi nace ana mace ba gyara ne yace kwarai kuwa har in ta san kanta.
Karfe nawa zaki ya tambaya nace wuraren goma zan tafi nasan zuwa karfe sha biyu ko da rabi na gama yace da safe banda time da nazo na kaiki sai dai ki fada min sallin din da kike zuwa in duba ki idan na rarage abinda nake yi.
Nace No kabarshi kawai ba wani nisa yake dashi da inda muke ba nagode yace aini nace ki fada min ko nace beauty hair drasses na fada mai layin da yake a saman babban titi.
Munyi sallama ina mamikin halin shi da saurin sabo irin nashi na zauna na tsefe kaina a cikin daren nan don kada in makara in samu mutane a wurin.
Washegari da safe na shirya na isa sallon din ba wasu mutane dayawa don haka nabi layi sai da akawanke min akai min drying din shi kafin su fara min kitso.
Ranan nasha gyara sosai na jiki daidai zan fito sai ga wayan Yusuf shigo yana tambayana ina wurin ko wuce nace an kusa gamawa nan da minti talatin zanbar wurin .
Nakashe wayan akaci gaba da min gyara sai yaba yawan gashina da tsayi suke yi nidai murmushi kawai nake masu ban wani dogon magana da kowa a wurin.
Sun fito daga kubuwa duban fili da sukaje gani a hanyansu na komawa gida yaga Yusuf ya dauki hanya bai iya magana ba yana aiki a system din shi kan shi a duke yake.
Sai dai yasan ba hanyan gida Yusuf ya nufa dasu ba aikin da yakeyi ya dauke mashi hankali a lokacin ganin ya tsaya a bakin wani gyaran jiki na mata yasa shi dago kai yana tambayan shi ina ne nan kuma ?
Kafin ya bashi amsa yaji yana fadi a wayan shi fito gamu a kofa idan an gama maki nace gani tafe na fito tun fitowa na ya hango nice tafe kallon mamaki yake wa Yusuf din.
Har na karaso bakin motar nasu sai a lokacin nasan tare suke dashi fadi yusuf ke yi da na karaso wai wanan haduwa haka fa kanwata .
Kaike kara zuzuta yayi maganar kamar bashi ya fada ba yace ba dole ba in zuzuta kanwata yar gidan mama wanan ai kyasa ayi karo a hanya nidai murmushi kawai nayi mashi.
Na fara gaida su yace shigo mu sauke ki mana ba hostel zaki koma ba nace a a nagode yayana ku tafi abinku kawai dakai dayane zan shiga amma dai ku tafi kawai.
Yace au don wanan miin buzuwan da kika gani ai bashi ke jan motar ba ko shiga muje don ki kawai muka biyo nan fa.
Jin haka yasa na bude motar na shiga batare da na sake wani magana ba shiko sai aikin shi yake yi kawai ana tafiya mun kai wurin wani babban shago yace don Allah ku bani minti biyu in dawo.
Ya faka motar yafita sai mu biyu a cikin motar kowa da abinda yake yi a lokacin sai can naji yaja tsuki yana kallon shagon na dauka dani yake yi nace dakata malam bafa kai ka dauko ni ba da zaka ja min tsuki haka.
Da mamaki ya dago kai yana kallo yace ke dani kike nace da wani nake haka kawai zaka kama jamin tsuki a mota da mamaki yake kallo na yace ke wata irin yarinya ce da bata da tarbiya.
Kadai gyara maganan ka malam tarbiya ai ko makaho yasan akwaishi nan sai dai a lalaba a gani ai ba bace marasa tarbiya suke ba.
Bai kai karshen magana ba cikin zafin nama da kunar zuciya ya juyo inda nake yace wa kike nufi baida tarbiya cikin muryan nan nashi mai dadin saurare da yake rowan ta.
Tsoro naji ganin irin kallon da yake bina dashi mai kama da harara ko tsana sai nayi kasa da kaina na kasa furta komai don kwarjin da yai min a idona
Ya nuno yatsan shi daidai saitin fuska na tare da tsure ni da idanuwan shi lumsarsu yana fadin ke in badan Yusuf da bai san ciwon kan shi ba har kucaka irin ki ta isa ta shiga min mota na a tare dani.
Yace kallani nan ko a hanya nagan ki baki isheni kallo ba a cikin mata don banga abin gani a wurin irin ki ba cikin dakiya da dauriya nake kallan shi ina jin kalamin shi har cikin raina sai dai ina tara abinda zan mayar mashi ne a zuciya ta duk da naji tsoran yanayin shi.
Yaci gaba da fadin idan baki hankali da ni ba watarana sai na balbala ki wallahi don ni mace bata kawo min raini nace dashi.
Don Allah malam matsamin bakumayi mamaki jin haka don ba abin mamaki bane don ka fadi hakan tunda dama kai irin maza nan ne dake raina jinsin su sai kai ido ga mata ketere saboda zalama irin na rashin sanin ciwon kai.
Don wanan matar taka abin kyama ga jamma a da kai ka mayar mutum har kake ganin tafi ko wace macen kasan nan dadin abin dai kaima macen kasan nan ta haife , , , ,
Fat naji yakai min bugu a baki don zafi sai da na dafe baki na ina dubawa ko jini yake min ban san lokacin da idona ya fara fitar da hawaye ba na yun kura zan fita daga motar yasa hannu ya danna lock mutar ta rufe kit yace kuma ki saurare ni.
Duk kika sake ganina a mota kikayi gigin shigan shi sai ya jefar dake a waje mota ya take ki kin mutum in kashe ki in kashe bazan .
Nace ni wallahi ba banzan bace sai dai in kaine yace bakin naki bai mutu bako yana kokarin kai hannun shi ya kamo baki na na noke kaina a kafana sai bai samu kama bakin nawa ba.
A daidai lokacin Yusuf ya iso wurin da manyan ledoji a hannun shi yana bude motan zai sa ganin mu haka yasa shi ya sake murmushi.
Ina jin shi nayi saurin dago kai nace mugu kawai azzalumi yace kai yaya haka may kai mata don Allah take kuka kuma ya waigo zai kara jamin baki na noke ina son fita a motan Yusuf ya tare ni yana fadin haba dai yaya zakaci zalun ta kuma haka ?
May tayi maka haka wai kasa ta kuka ya juya yana cewa bakin nan mai rashin kunya na daka ido ya zaro yana cewa ka dake ta Abdul ?
Kadan ma ke nan nayi mata ai fita nake son yi ba hanya don Yusuf dake wurin yayi rufe kofan ya zagaya ya shigo motar sai da muka fara tafiya yace ka bata hakkuri Abdul.
Ina baya ina kuka naji ya fada mai hakan yace nace ka bata hakkuri yace wani zanba wanan yariyar hakuri ko wa yace bakai ka zalunce ta don may bazaka bata hakkuri ba ko kafin ka tafi da hakkin ta ne a kanka ?
Baiyi magana ba sai aikin shi dayaci gaba dayi yace wai may ya hada kune haka da sauri nace zagina yayi na rama.
Motar ya tsaya a kofa gidajen mu na fita da sauri ya biyo ni yana kirana ban tsaya ba wata yar gidan yaba kayan ta shigo min dasu suka tafi ban san yadda suka karata ba.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIna isa na fara bude kofana na lokacin yarinyar ta iso da kayan da Yusuf ya bata tana mika min kallon kayan nayi sai na karba ta karasa min da sauran a cikin daki na.
Godiya nayi mata tace babu komai ai ana tare bayan na aje kayan na fada saman katifa na wasu hawaye masu zafi ne suke silalo min a fuska na.
Idan na tunana da maganganun da ya fada min masu zafi duk da nima din nayi karfin halin ramawa a lokacin sai nake ganin ya kwaraini da yawa.
Na dade a wurin ina neman hanyan da zan rama abinda yayi mun din don yaji zafin da naji ban kai ga samun mafita ba wayana yayi kara a lokacin.
Yusuf ne ya kirani sai da ta kusa tsukewa na dauka na kara a kunne na ina sauraron shi yace har yanzu kina fushi ne yar mama.
Daurewa nayi nace ai ban fushi dakai don bakai min komai ba yaya na yace dakyau ina son ki saurare ni dakyau magana nake so muyi dake yanzu.
Ina jinka nace mai.
Khadija don Allah ina son ki bani hankalin ki ki fahinci abinda zan fada maki yanzu naji na kara furtawa.
Don Allah ina son in rokeki wata alfarma wani aiki zaki nake son ki min a kan aboki na amma aikin yana da wahala sosai sai dai indan kin daure ba wani wahala a cikin sa.
To ina jinka Allah yasa zan iya kuma Allah yasa dai aikin bai fi karfina ba, murmushi yayi yana fadin bai fi karfin ki ba ma insha Allahu don zaki iya.
Nace fada min inji aikin idan ba zai shafe karatuna ba da rayuwa na zan iya insha Allahu yace good girl dama na dade ina neman mace irin ki mai gaskiya da zan saka.
Ba wani abu zan saki ba sai taimako rayuwan abakina Samad nake son in danka a hannun ki don kice a yanzu kadai nake da ita da zatayi min wanan kokari.
Nace ni kuma yayana yace kwarai kuwa ke khadija don ko zaki iya idan munyi laakari da irin halin ki na san zaki iya shiyasa na zabo ki.
Tun ranan da muka shiga dakin hajiya mama na fara ganin ki da kuma abinda yafaru dake da Nafisa matar shi kika tsaya min a rai.
Ban kuma gaskanta hakan ba sai da naga kin iya biyu su a motar su zuwa nan Abuja kuma komai bai faru ba yasa na kara yarda da abinda nake shirin yi din .
Sai gashi kuma yanzu abubuwa suna wakana a yadda nake son su tafi a tsakanin ku cikin hukuncin Allah komai yana tafiya daidai.
Khadija ko kin san ba macen da ta isa ta tsaya kusa da Samad tun lokacin da ya auri Nafisa buzuwar matar shi kuwa.
Nasan kin san matar shi Fati da akai masu auren gida har suka haifi yaya biyu shigowan buzuwa gidan ya sa suka rabu da ita badon basu son junan su ba.
Khadija kin san abinda ya daure min kai nace a a yace yadda Yusuf ya aminta dake a lokaci daya duk da nasan ba abu bane mai wuya a wurin Allah idan ya tashi yin ikon sa akan abu.
Don haka nake son ki taimaka muna ki sake jiki da shi tayadda zai aminta dake idan haka ya samu gare mu na tabbatar da sheri buzuwa yana gap da karyewa.
Da sauri nace ba zan iya ba gaskiya ku nemi wata wanan miskilin mara mutunci ai buzuwar ne daidai dashi yace khadija zaki iya zaki iya komai.
Kyau dai Allah ya baki shi ilimin addini da na boko duk kina dasu a wadace to may zai saki ce bazaki iya ba ai ko ba don niba ko don hajiya mama da fati da yaran ta zaki iya.
Nace yanzu may kaka son in yi wai yace shina ke son in fada maki da farko dai idan ki bi labari na zaki gane Samad bai iya ssoyayya ba shine matsalaan farko da aka samu gare shi.
Murmushi nayi nace bai iya soyayya ba ta yaya ya auri matan shi har suka zauna Fati har ta haihu dashi biyu shima din murmushi naji ya dan yi yace.
Bamu tare ke nan kin manta na fada maki ita fadi hadin iyayyene auren su ita kuma buzuwa abu biyu muke zaton shine silar auren su na farko dai ta rude shi da kyaun ta na biyu kuma ta hanyar sihiri da sauri nace sihiri kuma bada ni ba gaskiya.
Yace da zata iya maki komai da tayi tuntuni ai shine ya bani daman sakaki wanan aiki a yanzu.
Nace a takaice dai kana son in bata lokaci na a kan shi abinda ya kawo ni in barshi inje taimakon wani wanin ma wanda bai san darajan mutane ba.
Aikin da zaki muna ke nan dama ki koya mashi zama da mutane da sauran abubuwan da ya watsar a baya ki dawo muna dashi Abdulsamad din shi na baya.
Babban magana ke nan yayana yace ba wani babba bane a matsayin ki na mace zaki amfani da daman ki taimaka muna ki tai maki hajiya dake cikin halin bakin ciki a kashi.
Shiru nayi ina tunane ko badon Yusuf ba ko don hajiya da yaran Fati zan iya kasadan yin wanan gwajin da suke sona dashi yanzu.
Nace to shike nan naji zan yi matukar hakan ba zai shafi mutunci na ba dai yayi saurin cewa idan nasan zai zubar maki da kiman ki ba zan saka ki ba ai.
Nace amma fa in ya nemi keta min mutunci ba zan kyale shi ba zan dauki mataki da kaina yace wanan ba halin shi bane don nasan halin shi tare muka taso tun muna yara dashi.
Nace Allah bamu sa,a yace amin na godd da kika fahince ni yanzu zan samu lokaci in shigo inji mai kike bukata don kin san dole sai kin koma ke ma babban yarinya sosai.
Kada ka damu zanyi amfani da wanda nake dashi yace kin wuce wanan yanzu khadija zaki zama budurwan mayan garin abuja ne fa.
Yace ina son ki fara daga yau nace yau din nan ina zanganshi yace zai bugo maki waya ba yana da layin ki ba nace eh zaki kaga ya kiraki kan abinda yayi maki.
Amma sai dai please ki bishi a hankali yana da izza da saurin fushi da zuciya bai son yawan magana idan ba