Showing 129001 words to 132000 words out of 142410 words

Chapter 44 - MIJIN BUZUWA COMPLETE

Start ads

08 Aug 2025

30

Middle Ads

kuma ?
Yana tsaye bayan ta rungumay da yarsu a kafadan shi tana barci tace dashi cikin zafin rai wanan mara kunyar mana tana ganin ina da raayi abu kuma zata sa wani kazamin hannun ta ta dauka.
Bar mata mana tunda ta riga ta daukan wanan ba sai a kawo maki wani ba tunda baza su rashi ba anan din .
Haba malam yaya zan ce ina son abu sai kace wai in bar mata ita wacece da zan bar mata murmushi nayi nace au shagon dama na gidan ku ne ashe.
Maryam ne ta iso take tambaya ganin shi kuma sai duk ta daburce tana gaida shi tare da gaida nafisa wace ke ta kunduma ashar a bakin ta.
Nace da maryam muje ko ban tsaya kulataba na raba su na wuce maryam ta biyo ni baya duk a tsure take bamu tsaya magana ba muka mika kayan wurin biya suma a lokacin suka iso gurin biyan kudi yace hada kudin da nasu ka cire a katina lokacin nafisa ta iso ta samay shi tace dani.
Karya kike yarinya zanyi magananin ki a garin nan dani kike wasa wallahi nace kafin kiyi magani na ni zan fara yin naki a garin nan na watsa masu harara har mijin nata naja hannun maryam muka tafi.
Bayan mun fito muna saman titi da maryam muna jiran abin hawa sai ga su sun fito daga cikin shagon suma suka shiga wata hadadiyar motar su a gaban mu ta leko glass din motar tana fadin matsiyaciya ko mota ashe baku da.
Tsawa mukaji ya daga mata tare da fadin wai manene haka nafisa ya ja motar da karfi suka bar gurin tsuki naja gami da harara na raka su dashi.
Maryam tace yau naji takacin barin mota na a gida wallahi da dashi muke wanan matar bata isa tayi muna haka ba.
Nace au ke kin damune da maganan ta ita uban wa ya bata motar gidan su badai da namijin nata take barazana ba.
Matar nan lallai bata da hankali khadija jifa yadda take abu kamar wata yar bariki can nace guri ta samu tayi abinta amma ni bata isa ta fada mi in kyale ta ba.
A can kuma cikin motar su fadi Nafisa keyi wai ni ina ma nasan wanan fuskan ne na mance ida nasan wanan yarinyar wallahi ?
Bai mata magana ba sai tukin motan shi yake yi shi kadai yasan abinda yake ji a ranshi a lokacin wai a haka zai hada wa yan nan yan zafin rai guri guda.
Tace wai ashe ba yarinyar nan bace kuwa sai kuma tacce ba ita bace don waccan bata waye haka ba koma waye taci bashi wallahi in dai nice zamu hadu wata rana ai zata raina kan ta.
Tana takama don tana da kyau da diri wa zata nunawa kyau da fari anan kai dake dani a gida tana ganin kyauta zai rude kane take wani far da idanuwan ta haka.
Murmushi ya danyi cikin kunan rai tare da fadin ki san abinda zaki fadawa mutane don baki san ko ita din waye ba a garin nan kizo ki jawo wa kanki matsala wata rana.
Maryam ke ta zuba a mota nace please maryam ki rabani da maganar wanan matar mara mutunci wallahi sai na gwada mata ita karamar yar iska ne daga yau .
Ni fa laifin ki nake gani da kika bata wanan daman take ganin ita wata tsiyace da kin jaye hankalin mijin ta ai da zata gane bata da wayo.
Nace cikin mata wani iri kallo wani mijin kike magana badai wanan mijin da baida ta cewa ba a gaban matar shi kike nufin in sace zuciyar shi in kai ina idan na sace ga mai iko da zuciyar shi kina gani.
Jifa yadda yau ya nuna bai sanmu ba a gaban ta kwata kwata wallahi saboda tsoron mace da yakeyi.
Ta kada kai tana fadin wallahi ba tsoro bane mutunta matar shi ce kawai yayi kuma ko wani namiji ne ma haka zai yi ai a gaban kowa.
Don dai kawai a zauna lafiya amma da gidan shi kike yai haka shine zakice wani abu kyale ta nayi don ina ganin don ba ita akaiwa hakan ba yasa take fadin hakan.
Har muka isa hostel din ba wanda yayi magana da dan uwa wanka nashiga na fito da alwalana na tayar da sallah ina gamawa na kwanta tare da bata baya .
Muryan ta naji tana fadin bazaki ci komai ba ke na kike nufi zaki kwanta yanzu banjin cin komai murmushi tayi tare da fadin .
Ai ba haka ya kamata ki bullo mata ba da fushi da abinci don ita ko shi basu ma san kina yi ba ai yanzu wallahi khadija lokaci yayi da zaki falka daga barcin da kike yi.
Kamar yaya na katse ta tare da juyowa ina fuskantan ta nace may kike son in yi mata tace wallahi ki cusa kanki ga A A shine mafita a gareki.
Kaina girgiza nace haba maryam wanan zubar da ajin kike son inyi komay kuma ni nasha fada maki ban ra, ayin wanan A A din sam.
Tace ko baki son shi ki girgiza buzuwan nan don Allah tasan shayi ma ruwa ne ba ita kadai bace mace a duniya har duniya ta kare akwai mata kyawawa a duniya.
Nasan wallahi kyau ki da zatin ki kadai ya ishe ta ballw uwa uba karatu da kike dashi wanda nasan ko bokon primary ita batayi ba kila acan .
Dama na farko da zaki fara nuna mata kai tsaye shine gorin motar da taimaki kona kwana gudane kice mashi mota kike so anan zamu gane idan yana son ki sai muci gaba da aiwatar da shirin mu akanta sannu a hankali.
Kallon ta nayi wani iri nace mota fa kika ce maryam ina zankai mota tace baki zaiyi kai tsaye akace maki balle ki damu.
Fada mai hakan kawai zakiyi don mu gani kina da tasiri a gurin shi ko baki dashi ajiyan zuciya na sauke tare da fadin zan gwada in gani to.
Har na kwanta kuma na juyo nace mata maryam idan ya bani motar fa ai na kashe kaina a gurin iyayyena wallahi.
Kyautan mota wasa ne khadija ai ba baki zaiyi ba kai tsaye anan kin ga zamu san abin yi kuma nace to shike nan tunda haka kika ce tare da juya mata baya.


ZAINAB IDRIS MAKAWAWanan magana ya tsaya min a rai sai dai gaskiya ban aminta da maganar maryam ba don ba zan iya bude baki na in roki namiji koda kwandala ba balle har mota.
Ina zan kai mota idan ya bani a gida ince dasu ina nasamo mota kana wa yaban motan akan wani dalili zai min kyautar mota haka inma har zai bani din.
Gaskiya maganar ta bai karbu ba a wuri na sam zandai gwada mata nima ba kyale bace zan mata abinda sai tarena kanta da kanta anan na aje maganan azuciyata.
Sai dai ban fada ma maryam abinda na yanke a zuciyana ba nabar abin a raina don ita maryam ba abinda ya damay ta wanan nake ganin a gurin su ba komai bane hakan sai abin alfahari.
Washe gari na mike kamar komai ba faru dani ba ajiya ganin yadda na sake yasa maryam dauka ko na dauki shawaranta ne.
Ban damu da fita ba don yanzu karatuna shine a gabana ranan mun dawo maryam ke tambaya na wai har yanzu taji shiru mana ko ban buga ma AA waya bane akan batun motar.
Banza nayi da ita kamar badani take magana ba sai da ta sake tambayana nace mata don Allah maryam ki bar wanan zancen .
Don bashine a gabana ba yanzu abinda nazo yi nake fuskanta ban son abinda zai raba min hankali ko kadan.
Amma dai khadija kin kwabsa wallahi don kawai kin tambayi AA abu shine kike ganin rage ajine a gurin ki wanan ai ba komai bane wallahi.
Yan mata nawa samari ke sayawa mota kuma a zauna lafiya so maye bai sakawa a yi wanan ai kara ma kanki daraja ne ba wani abuba.
Wani kallo nayi mata nace rokon shine karin daraja ga mace rokon ma irin na rashin hankali haka wai ma idan har ya bani motar ina kike son in kai mota yanzu.
May yasa kike magana kamar wata bagidajiya ne khadija samu yafi iyawa aida samu din ai yadda zakiyi dashi ba abu bane mai wahala.
To bazan roka din ba period sai kuma may a take ta bata ranta a wuri banza nayi da ita na mike ina dauko kayana da zan goge itama batayi min magana ba.

Yana zaune a falon shi kiran Fati ya shigo mai a waya bayan sun gaisa dashi dan shiru ne ya biyo baya sai can ta kau da nata miskilancin tace naga dubu dari biyar ga account dina dazun.
Shima cikin magana kamar yana gune dayin maganan ya bata amsa da cewa eh kudin da kika bukatane nace a tura maki har wanda zaki wanin abin.
Angode tace mashi zata kashe wayan yace ke baki taba kiran mutum sai idan wani lalurar kudi ko wani abin ya taso maki zaki kira.
Bazaki kira kiji halin da mutum yake ciki ba anan tace yanzun kiran nawa inyi godiya ya zama laifi ne kuma ?
Tsuki yaja tare da kashe wayan ya lumshe idon shi yana jin takaicin wanan baki halin na fati a kulun ita bata taba wayewa tana nan a yadda ya san ta a baya.
Karan takalma daji ne yasa shi bude idanuwan shi ya sauke a gare ta ba laifi idan zata fita tana kwalliya na kure a daka.
Sai dai a gidane baka taba samun ta a cikin shiri yadda ya kamata gashi shi mutum ne mai son yaga mace ko yaushe a cikin kwalliya hakan nayi mashi dadi sosai.
Karasowa tayi gare shi tana fadin zan fita don kasan yau saura yan kwanaki kadan bukin namu zan leka inga may ake shiryawa a gidan kareemay din.
Yanzu wa kike fadawa da zaki fita kin nemi izzinina kan zaki fita din kallon shi tayi tana dariya tace wata sabuwa ke nan ?
Yanzu fitan ma da zanyi nan cikin gari sai na nemi izinin ka ko may bafa gari zan bari ba wanan wani magana kake nema kuma ?
No ba sai kin nemi izzini ba tunda haka kika daukar wa kanki amma ki sani komai daren dadewa watarana wace zata nemi izzini na a gidan nan tana tafe.
Da sauri ta gimtse fuskan tace bako a gidan nan ba idan ma mafalki kake ka falka ba wata shegiyar mace da zata sake shiga rayuwan ka kuma muddin ina raye kai koma ban raye na fada maka haka.
Kina zancen ki dai yanzu don kin ga ban tashi ba cikin daure fuska tace don Allah mu bar wanan zancen zan fita lafiya kana son bata min rai na.
Ta juya ta fita ba tare da tayi mai sallama ba don ranta ya gama baci sosai dashi a lokacin nan ta fita ta barshi zaune a falon .
Zaman falon yaji ya ishe shi daga inda yake zaune yake jin kukan yar shi na zuwa mashi haka yasa ya mike yabi inda kukan nata yake zuwa.
A dakin Yanyala ne kukan ke fitowa ya tsaya daga kofa yana kwakwasawa ba a karba ba yasa kai dakin ya samu yarinyar ta tashi daga barci tana zaune tana kuka ita kadai a dakin.
Dauko ta yayi zuwa sama yayi mata wanka ya bata abinci har ya shirya ta ya fito gidan ba wanda ya nemay ta cikin gari ya fita da ita yawo.
Gidan Yusuf ya nufa ya samu zai fito sai suka fita tare da yusuf din Yusuf ne ya kalle shi yace ina mukayi yanzu ga yarinya ka dauko kuma ?
Yace dashi kaini gun khadija please batare da ya kalle shi ba murmushi Yusuf din yayi yace yau ranka a bace yake halan ?
May kagani kace haka yace naji kace in kai gun khadija abinda na dade banji ba a gare ka shiyasa nasan an bata maka rai ke nan.
Ya furzo iska daga bakin shi tare da kara rungumay yarinyar a jikin shi yace ban san irin rayuwan Nafisa ba Yusuf yau da yake ranan hutu ga kowa daya kamata in zauna gida in huta da iyalina.
Sai gashi ta kirkiro fita wanin unguwar da baida dalilin komai wai kawar kawarta ne zata buki shine suka fita gin shirye shiryen bukin.
Aka bar wanan yarinyar tana kuka ita kadai a dakin da sauri Yusuf yace subbahanallahi ina masu kula da yarinyar suka tafi kuma ?
Yaja tsaki yace itama ta iya fita tabarta don may zasu tsaya kula mata da ya suma sun tafi nasu mana.
Kai Allah ya sauwaka da halin bariki wallahi ba don nasan ka tun farko ba Abdulsamad da sai ince auren bariki kukayi da nafisa.
Yanzun dai ni kaga ina jin kunyan Khadija wallahi na dade ban kirata ba kuma ban nemay ta ba tasan kuma muna garin .
Ranan yakai three weeks mun hadu da ita da Nafisa a shago nakaita taiwa Bannan sayayya sai gasu ita da maryam har dan rikincin kayan shafa yaso hada su a gurin.
Kasan halin nafisa da rashin hakkuri nan dai suka rikece ya bashi labarin komai da ya faru a wurin a tsakanin mu.
Dariya Yusuf yayi sosai yace dakyau khadija baki daukan ta kwana ko kadan AA yace shine matsala ta da ita wallahi.
A bakin hostels din mu suka tsaya aikawa sukayi a kirani bayan an tabbatar masu da ina ciki wata Annah ce tazo ta fada min ina da baki a waje.
Ban tsaya wani gyara ba nasa kai na fita ganin kowaye yake nemana din tun daga nesa na hangoshi yana ma yarinyar wasa a mota.
Har na iso inda suke fuska daure bai dago kai ba hannkalin shi naga yarinyar muryana yaji ina gaida Yusuf.
Ya dago ya dan kalle ni bance dashi komai ba lafiya dai na gan ku a wanan lokacin na tambayi Yusuf din cikin daure fuskana.
Haba kaunata kin daure fuska haka kamar ba gobe ai kya gaida dayan yayan naki ko tunda kin gan mu tare dashi nace ai ba wuri na yazo ba.
Ka taba ganin mai arziki mijin hamshakiya yazo wurin diyar matsiyata wace bata kai matsayin a tsaya da ita ba ?
Haba khadija ina wanan maganan ya fito haka kuma nace gashi nan ai ka tambaye shi idan nakai matsayin yazo inda nake sai ya fada ma .
Murmushi AA din yayi yace da zaki shigo daga ciki zaifi don wanan zafin ranan zai iya maki illa anan har lokacin bai daina wasa da yarinyar ba.
Ido na waro waje nace mota ai sai ku da matan ku yar matsiyata da bata gaji shiga mota ba ina zan taba motar ku in sha maku talauci a ciki.
Motan ku na gama shigar ta tun ranan na dogara ga yadda Allah yayi mu ni da mahaifa bamu kai kan mu inda Allah bai kai mu ba.
Ido ya runtse yana jin maganan da nake fadi har cikin ranshi Yusuf yace dakata kauna na nasan abinda yasa kike wanan maganan yanzu ma shi yace muzo mu duba ki don tun ranan bai samu lokacin zuwa nan ba.
Ga kuma yar ki nan ya kawo maki ita ki ganta mun san Nafisa bata kyauta a yadda kukayi din nan ina ganin shine dalilin ramshin zuwan shi gurin ki don yasan dama a jirace kike dashi gashi kuma ashe har yanzu baki huce ba ke ?
Akan may zanyi fushi da abinda ta fada ai gaskiya ta fada ba karya ba ni yar tallakace bamu da ko keke a gidan mu ita kuma da ya mayar yar masu arziki ba rawa taiwa Allah ba ya bata shi.
Sai dai ta sani daren baiyi ko balle gari ya waye tajira taga zuwan daren tukun kafin ta wullakanta mutum.
Yarinyar ne tasa rikici don haka hankalin mu ya koma gare ta yana dan jijiganta ta kallon inda nake tsaye a side din Yusuf tana mika hannun ta.
Yusuf yace kin ga Banan tana ba mamanta hakkuri on behave of her father murmushi nayi ina kallon yarinyar nace fine girl wanan bai shafe ki ba ko ?
Daga inda nake na mika hannu sai yarinyar ta zillo zuwa gurina banyi gigin karban ta a wurin shi ba sai cewa nayi ku kaita gida mana.
Taga kuna kama da uwar ta ne take dauka ko ita ne nace Allah dai ya tsare min kama da wanan matar yarinyar bata bar kukan ba haka yasa naji har cikin raina na mika hannu ya miko min ita in dauke ta.
Da sauri ko tazo wurina karban yarinyar nayi ina dan jijiga ta a hankali tare da shafa mata bayan ta sai tai shiru tana ajiyan zuciya a jikina.
Ikon Allah banan kin san ta ne Yusuf ke fadan haka yana dariya AA yace daga inda yake zaune dauka ta ko maman ta ne don ta ganta

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login