Showing 111001 words to 114000 words out of 142410 words
da mamaki fal a fuskan ta tace khadija kin ga wanan kayan kuwa ?
Nagani maryam nace mata tare da lumshe idanuwana ni kadai nasan abinda nake ji a lokacin.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUJikina yayi sanyi sosai da kayan da naga ya sayo min musu kya dagani kasan ai kashe kudi a wurin sarkan maryam ta daga tana fadin.
Wanan kan kizo kiji kudin shi zai kai a kala dubu dari uku fa saurin kallon ta nayi nace kai haba wanan dai kila mafa fashion ne kawai.
Khadija wallahi gold ne haba baki ganin shi ko agogon nan ban debe tsamanin shi ma fashion bane nace a wani dalili zai sayo min kaya haka masu tsada bayan yasan iyayyena talkawane idan naje gida dasu may zan fada masu akan wanan kayan haka ?
Rigunan ta sake tabawa tana daga su tace wallahi ko kayan nan anan zasu kai dari biyu kila koma sufi zaune nakai ina fadin shi wani irin mutum ne da baijin wuyan kashe kudi haka ?
Maryam dariya tayi tace khadija ke nan baki san ko waye shi ba yasa kike fadin haka bafa karamin mutum bane wallahi kudi na shigo mai ta kowani hanya.
Zasu iya sai da fili daya a wuni su samu milayan dari riba bakomai bane wanan a gare su wallahi kwanaki da mijin yaya na zai sai wani fili AA akace sai ya gani ya sa mashi hannu zai iya samun filin.
To mutum da ke samun kudi haka don ya sayo wanan ai kamar ki jefa allura ne a cikin teku gare shi gashi nan muna ganin shi a banza amma mijin yayana yakai wata uku yana neman ganin shi bai samu ganin shi ba.
Da sauri nace shi din tace wallahi Allah khadija wanan AA din kuwa shine don na tambayi anty na nayi mata kwatancen shi tace shine kuwa wallahi ba karamin kudi yake dashi ba ai.
Banda abinki duk wanda kika ga ya auri buzuwa gidan shi har ta zauna haka ai ya mallaki abinda ya mallakane.
Dubi shadda da tasa ranan da gwalagwala a hannun ta da wuya ke ko shaddan nan da zaki ji kudin shi zaki sha mamaki wallahi.
Ido na lunshe na koma na kwanta ina tunane a raina gaskiya ya zama dole in raba dasu kada suzo su batani haka da itin kayan nan in zo gaba abin ya damay ni na saba da saka mai kyau in sha in kuma ci maikyau.
Ranan da banda mai bani irin wanan yaya zanyi ga iyayyena tallakawa ne lis muna neman abinda zamuci a gidan mu.
Muryan maryam ne ya dawo dani daga tunanen da nakeyi tana fadin khadija zaki iya samun fiye ma da hakan gun samari don kyauki ne ya jawo maki haka .
Don ke din baki da maraba da yan buzaye dole ne na miji ya ganki ya rude haka sai dai shi AA nashi sallon son yazo daban da na sauran maza ne.
Yace dake sona yake yi da kike fadin haka kawai dai mutunci ne a tsakanin mu kune dai dake da Yusuf kuke ganin haka din amma ni ba wani abu makamancin so daya taba hada ni dashi.
Balle yanzu nasan da wuya su kara dawowa inda nake don na fada masu mamud zan aura kuma har na gabatar dashi a garesu sun gaisa dashi dazun.
Kikayi may khadija amma wallahi baki kyauta ma kanki ba wanan wani irin cin fuskane haka kikayi masu lalle kan da wuya su dawo gurin ki kuma sai dai da yake maza ne basu fushi da abinda suke so kai tsaye.
Mun dauki lokaci muna maganan da ita har dai nagaji na kyake ta tanayi ita kadai na bata baya.
Yau da wuri muka dawo dawo daga class bamu dade irin yadda mukan dade acikin makaranta ba maryam ta rigani dawowa har na samu ta gama abinci ko.
Dafa dukan manja yaji atarudu ta hada muna sai naman datayi amfini dashi a ciki danye zaune nake ina cin don ita tace tasha tea da tadawo don maryam bata wasa da cikin ta ko kadan.
Na kusan gama cine wata Ruth Samuel ta shigo dakin tana cewa ina da bako a waje yana jirana maryam ne ta kallo ni bayan Ruth tafita daga dakin tana fadin yanzun haka mamud ne dan kadafin tsiya ya biyo ki.
Nace kada kiga laifin dan bawan Allah a banza don nagane ke son wanda baisan kinayi ba kike yi yasa kike ganin laifin mamud din.
Hijjab dina karami na dauka ina sawa nake maganan na fita waje ban jira may zatace ba kada ta bata min rai.
A zatona mamud din ne yazo amma ina fita sai banga motar shi ba a wurin fitowa Yusuf yayi daga cikin motar da yazo da ita yana min hannu.
Zuwan Yusuf din ya bani mamaki matuka don banyi zaton zasu kara dawowa inda nake ba kuma .
Na iso inda yake tare da sallama yanayin shi kawai ya nuna min bai cikin dadin rai a lokacin yace ya karatu nace Alhamdullahi.
Shirune ya dan biyo baya sai ido daya kura min yace dama nazo ne neman alfarma a gurin ki idan zaki iya yi min .
Da sauri nace in zan iya may zai hana in maka tunda har kataso kazo gare ni a wanan lokacin haka.
Ajiyan zuciya ya sauke yace ina son ki shiga ki shirya yanzu ki fito in kai ki asibiti ki gaida Abdulsamad ne yau kwanan shi biyu kwance bai da lafiya ya dawo da ciwon ciki sosai tunda ya dawo.
Subbahanallahi na fada mace ciwon ciki kuma kodai yaci wani abin ne baku sani ba yace ciki da kai yake fadin yana mai ciwo tun kwana biyu da dawowan shi waje.
Ko ranan da muka zo wurin ki cikin karfin hali nasa shi muka zo ke kuma sai kika bata muna rai da dan banufen ki.
Murmushi nayi nace kuka dai bata ranku ga banza amma ni ban bata maku raiba gaskiya yace kin ko san kishin maza yafi na mata khadija ?
Kishi akan may zaiyi kishi kuma don dan wanan magana kawai yace wallahi ba don nasan Abdul tun farko baida lafiya ba da sai in ce har da maganar dan banufen nan ya sashi ciwo haka.
Sai dai bai karamin magana ba tun wanan lokacin a kan ki yanzu ma ni naga dacewan haka nazo daukan ki muje ki duba shi don Allah.
Nace gaskiya ba zan iya zuwa ba da sauri yace khadija kada muyi haka dake mana na dauka zan iya saki abu kiyi don ni koma badon niba ai yaci kije ki gaida Abdulsamad din tunda akwai mutunci.
Kai na girgiza tare da fadin Allah dai ya bashi lafiya amma ni ba zan tafi ba idan ma naje matar shi ta ganni may kake son in fada mata kuma don komai tamun tana da gaskiyan ta.
Balle ma bazaku hadu ba don ita tana gida bata faye zuwa ba sai sa a mommy ce dai a gurin nashi take jinyan shi.
Ko zan tafi bani kadai zan tafi ba sai inda maryam na fada yace gaskiya ne hakan yana da kyau ai wallahi ni ma kin ga na rude ban ko kawo haka ga raina ba sai yanzu.
Don Allah ki daure kizo muje khadija yin hakan yana da kyau sosai wallahi ciki na koma na fadama maryan zuwan Yusuf din tace muje don Allah ki duba shi gaisuwa ai ladane gare shi so sai.
Mun shirya ba laifi don zakace ba asibiti zamu tafi ba don maryam ne ta saka in shirya haka don kada muje mu hadu da buzuwa a can ta raina muna wayo.
Nace in sha Allahu ma baza mu hadu ba har mu dawo muka fito muka kama hanya ina gaba tare dashi maryam na zaune a baya.
Yusuf ya kawar da shirun da motar yayi a lokacin yace nasan zaiyi mamakin ganin ku yau saidai don Allah ki tuna a wani hali yake yanzu.
Nan dai ma banyi magana ba sai murmushin da na danyi kawai yace maryam khadija ta fada maki abinda tayi muna ranan ko ?
Wallahi ta fada min bata kyauta ba ai nayi mata magana kasan tayi nisa yanzu ga son dan banufen nan bata jin kira sai ta kai.
Da sauri yace ehyehh tayi nisa fa kikace har ya shiga gidane bamu sani ba komay ?
Amma khadija idan kin muna haka baki kyauta muna ba wallahi yaya zaki yi da abokina kuma idan kika fitar da wanan mamud din ?
Nace Allah kadai yasan wa zan aura yanzu da kuke wanan magana niko mamud din ina shakku a gare shi ne don ban faye son mutum mai mata ba a rayuwana .
Murmusgi Yusuf yayi yana kada kanshi yace yanzu dai kikai magana dama nayi zaton don ki musguna na munane kikai hakan.
Nace a a wallahi ni gaskiya na na fada maku har cikin raina bandai son mai mata ne a rayuwana yasa nike shakkan shi.
Tsaya yayi ya sayo kayan dubiya asibiti ya dawo ya shiga motar muka tafi dan jefi jefi yake dan jan mu da magana har muka kai inda zamu.
Motar ta shiga cikin Turkeys hospital ya samu wuri ya faka muka fito zuwa cikin dakin da aka kwantar dashi wurin tsit yake baka cewa akwai mutane saboda natsuwan da wurin ke dashi.
Da sallama muka shiga dakin yana gaba muna bayan shi biye har zuwa cikin dakin yana kwance rai,rai ya doran hannun shi daya saman goshin mommy tana zaune gefe saman kujera tana duban wayan hannun ta.
Sallaman mu yasa ta dago kan ta tana amsa muna tare da zuba muna idanu don bata sheda ko suwaye tafe don maryam ce ke bin Yusuf din.
Sannun ku da zuwa tace muka amsa da sannu mommy muna gaida ita sai can tace khadija kune tafe kun san baida lafiya ne ashe , ?
Yusuf ya karba da fadin wallahi sunji mommy yanzu na gansu shigowa nan din na karaso dasu ya mai jiki nace da mommy .
Mai jiki gashi nan yaji sauki yau ai mun ga hankalin shi jiya kan da muka zo abin ai ba dama wallahi.
Maida hannkali na nayi inda yake kwance yana saye da wandon three quarter fari sai yar riga irin na shan iskan maza din nan mara hannu amma rigar na da kauri blue colour.
Ya jikin nace a cikin wani irin murya mai taushi da sanyin jiki tare da dan kura mai manyan idanuwa na a hankali ya sauke hannun shi saman kan shi yace da sauki.
Shirune ya biyo dakin na dan wani lokaci Yusuf ne ya karaso zuwa bakin gadon suna magana dashi wanda ba lalai ne mu jisu ba.
Ledan da muka shigo dashi ya mika wa mommy yana fadin mu muka zo dashi tace kai khadija ina laifin zuwan da kukayi ke da ke makaranta kikaje yin wani dawainiya kuma haka ?
Tana nuna mashi daga inda yake kwance tare da fadin kako gane ta yarinyar nan ne kawar su Binta da suka kwana wurin ta kawar matan officer na layin mu.
Murmushi yayi mata kawai ba tare da yace komai ba muna nan tsaye jin yace yace Deedar akwai ayaba ki bare min in ci kai na gyada mai ba tare da nasan ko akwaishi ba.
Na bude ledan ina ciro ayaba daga ciki na fara barewa na miko mai tashi yayi zaine ya dan jingina jikin shi da filo ina mika mai a hankali yana karba dakin yayi tsit a lokacin.
Kofan aka turo wasu mata ne suka shigo dakin hamshakai dasu idon su caraf a kaina a yadda nake tsaye wurin kan shi ina bare mai ayaban ina bashi yana ci ko mommy ido ta zuba muna tana kallon mu sai take gani kamar da can musan junane ko kuma namu daine yazo daya bata sani ba.
Shigowan matan ya dauke mata hankali ga barin kallon mu ta maida hankalin ta gare su suna gaisawa dasu.
Kun fara jerabawa ne ko da saura ya tambaye ni mutum ba zai iya fahintar abinda yake fadi ba saini dake kusa nake jin shi nima a hankali na mayar mashi da amsa da cewa next week zamu fara insha Allah.
A yadda muke magana zaka dauka wani magana mai ma,ana mukeyi idon matan nan da suka shigo su uku ya dawo a kan mu suna kallon mu gashi jikina na kusa da nashi kamar dai mata da miji.
Mommy ke fadin yaji sauki sosai yau gashi ma yana cin ayaba har mun ga idon shi ai jiya abin ba dama wallahi.
Basu tsaya ba suka yi ma mommy sallama tare da fatan Allah ya kawo sauki suka fita muma bamu dade ba mukace zamu tafi Yusuf ya taso yana fadin barin je in sauke ku ko ?
Sallama mukai masu muka baro asibitin Yusuf ya fito ya sauke mu tare da yi muna godiya nace ba komai ai Allah dai ya bashi lafiya.
Fitan matan kenan daga daki suna shiga motar su dayan tace nikan yau naga abu wallahi wai waye wanan yarinyar danagani tare da mijin Nafisa.
Dayan tace aini yau imani ya kashe ni anan anya Nafisa batai sakaci ba kuwa ta yaya zata zaune gida ta bada damar wata na mata jinyar mijin ta don tsaban son jiki da sakaci irin nata.
Wanan may ta sani banda karyan arziki da nuna son miji a baki kawai waya ta daga ta kiranta tana labarta mata abinda suka gani.
Bata jira ta gama bayani ba ta kashe wayan tare da fitowa waje a sukwane tana zunduma ashar tare da fadin su Yanyala su biyu ta.
A hanya take fada masu abinda ke faruwa a asibiti da mijin ta da wata sai dai kafin su zo mommy tasha ita da Yusuf da mijun nata uwa uba yarinyar da bata san ko wacece ba .
A fusace ta turo kofan mummy dake zaune tana lazimi ta dago kai tana kallon ta da shigowan ta tace ina yar iskan yarinyar da tazo tana bare ma Ayaba ina karuwan yarinyar ta tafi ?
Wacece ita wa ya bata dama tazo kusa da miji na haka tana magana tana zaran ido ta kalli mummy ta kalli Abdul di dake kwance yana kamllon ta.
Nafisa you're very stupid zaki shigo ma mutane daki ba sallama kizo kina fadin rubish haka wakika ba ajiyan yarinyar da kike tambaya ?
Mommy tace wace yarinya wai take magana ne wani kallon wullakanci tayi ma mommy din tace ko wace yarinya ce ai kun sani ni za a munafunta kuma ?
Dama na sani ai abinda ake kulla min ke nan ba yau ba wallahi anyi kadan aga baya na a gidan nan balle aje a dauko wata karuwa tazo tana bare ma ayaba tana baka a baki.
Subbahanallahi wani munafuki ya fada maki haka mommy barta an bare min ayaban an bani a baki may zakiyi ?
Au ashe ma kasan karuwan ka tazo har ta baka ke nan karuwa kema kin san nafi karfin karuwa don yar kwarai ce ba irin ki ba da tashigo duniya tabar iyayyen ta.
Babangida kubar maganan nan don Allah tunda kai kasan gaskiya tace dole kice haka mommy tunda dake ake hada bakin yin haka.
Samad akan karuwa kake zagi na har kake min gori na baro iyayyena gida nazo nan ni kadai.
Ba karuwa bane yadda na aure ki haka itama zan aure ta in kawo gida ta zauna dani tafiki komai da kike tunanen kina dashi.
Ido ta waro waje kafin tai magana security din asibitin suka shigo suna kokarin jan ta waje suna fadin ba ai masu hayaniya anan kuma ba lokacin zuwa duban marasa lafiya bane yanzu.
Samad aure kake fada min da bakin ka zakayi aure fa kace suka tura ta waje tana masifa tana zagi mommy mamaki ne ya cika ta da jin kalamin da ya furta.
Bayan fitar ta tace Babangida dama kuna tare da khadija ne ko dai ka fada mata hakane don ka bata mata rai.
Mommy bar yar iskan matar nan da bata da hankali zanyi maganin ta nan bada dadewa ba.
Lamarin Nafisa ne sai hakkuri kabar biye mata kuna sai da hali haka haka ba tarbiyan ka bane wallahi.
Bai iya mata magana ba don ranshi a bace yake da abinda nafisa tazo tayi masu yanzu sai mommy tace wai ma a ina taji wanan abin ?
Har take aibanta yarinyar mutane haka khadija ne take kira da karuwa wanan bata da tarbiya wallahi.
Har ta kare bai mata magana ba tace Allah ya kyauta taja bakin ta tayi shiru zuciyar tab da sake sake a cikin shi.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUTunda muka muka bar asibitin shiru nayi ban iya magana ba sai su ke dan hira jefi jefi a motan ajiyan zuciya na sauke ina fadin yanzu baku ganin kamar yawan ciwon kan nan wani abune ?
Da sauri Yusuf ya juyo yana fadin wani abu kamar yaya sai nayi shiru kuma yace tambayan ki nake yi mana kin yi shiru kuma.
Nace akwai ciyon kai irin wanan da yake na