Showing 66001 words to 69000 words out of 142410 words

Chapter 23 - MIJIN BUZUWA COMPLETE

Start ads

08 Aug 2025

26

Middle Ads

ta dawo ta dubani.
Sai ganin shi tayi yana shirin juyawa da sauri ta karsa wurin shi tana gaidashi tare da fadin wallahi tana ciki bata da lafiya ne tun jiya nima yanzu na dawo in dubatane.
Yace shi yakawo ni yazu asibiti nake son zuwa da ita a ranta tace boye min khadija ke nan rayi ashe suna waya dashi shine take boye min.
Taji yace nakira wayan ta taki ta ga bayan yanzu Yusuf ya gama waya da ita ta fada mai bata da lafiya tace barin shiga in fito maka da ita nasan fushi take daku.
Fushi ya tambaya da mamaki dariya tayi tace ina zuwa don Allah ta wuce ya bita da kallo har tabace yana mamakin kalamin ta wai fushi take da ku fushi akan may ?
Tana shiga dakina ta nufa ta samay ni a kwance zama tayi a gefe na tana min sannu tare da fadin ga mutumin ki nan a bakin get yana jiran ki wai kuje asibiti yanzu.
Wani kallo mai kama da harara na watsa mata nace rabu da mayaudari nine zai kai asibiti akan may zai zo min a yanzu da bana son ganin shi.
Haba khadija kin san uzurin da ya tsayar dasu basu nemay ki ba tunda har yanzu ya iya zuwa da jin baki da lafiya ai ya kamata ki saurare shi.
Haba maryam abinda kika sani ne nafi jin dadin zaman da nake yanzu babu takuran kowa a kaina akan may kuma kike son in kara fadawa tarkon mayaudari irin wanan mutumin da matar shi tafi karfin shi kuma.
Kada kice haka khadija ko ba komai ya nuna kulawan shi a kan ki yanzu ina laifin wanda ya nuna maka haka a lokacin da kake cikin halin ciwo.
Don Allah ki tashi ki daure badon ni ba sai don Allah ki tafi ki ganshi ko ba komai zakiji abinda ya tsayar dasu kwanaki mai tsawo haka baki ji su ba.
Allah da kika hadani dashi ne zai sa in tafi badon wani abu ba can nasa, don ina son inyi nisa da shuumancin su yanzu tace daure kiwa Allah da kika ce zato kike yanzu kila ma ba matar shi bace ta hana ya kulaki.
Kalaman ta yayi tasiri sosai a raina koba komai ina son jin abinda ya hana injisu kwana biyu don ban sin jawa kaina wulakanci ko kadan.
Ita ta taimaka min na shirya atamfa na daura don yanayin da nake ciki tare muka fito zuwa ida yake zaune a motar shi.
Yana yi yana kallon agogon hannunshi can ya ga fitowan mu tare da maryam ina tafiya da kyat yanayin ina jin jikin nawa sosai.
Har muka karaso bai dauke idon shi a kan mu ba yi hakkuri mun barka kana jira wallahi barci na samu tanayi yanzu na tayar da ita.
Bai yi magana ba sai kallona yayi yana fadin shiga mota mu tafi nace basai naje asibiti ba na sha magani naji sauki ina magana da kyat cikin daure fuska.
Shiga muje nace maki da sauri maryam ta riko min hannu ta nufi gefen mai zaman banza tana bude min motar tare da fadin sai kun dawo Allah ya sauwaka.
Sai da na zauna da kyau ya tayar da motan muka hau dogon titin da zai kaimu cikin gari sai da mukai nisa kaina da duke na dafe goshina da hannu na daya naji yace.
May damun ki ne haka ban bashi amsa ba sai gyara zama da nayi ina cije baki don dan motsawan da nayi maran yana min ciwo yanzu.
May damun ki ya sake maimaitawa shiru nayi can nadan sauke nufashi nace da kyar banda lafiya ne kawai tare da dan dafe mara na.
Au ko abin ne yazo maki na manta yanzu kike cikin time din period din ki ko hararan shi nayi tare da kawar da kai ina cewa a raina kaji min mutum da bin didigi haka ?
Kwana nawa yakeyi halan sake dago kai nayi na kalle shi kamar bashi yake maganan ba nayi saurin kawar da kaina daga kallon shi.
Yace bakiji bane kwana nawa kike dauka kina period din nace ya fada tare da dan kallo na nace ban sani ba kada ka wuce hurumin da ba naka ba mana na fada ina kwantar da kaina.
Murmushi yayi yace haka kike ce ko nace na fada din ni banga dalilin tambayana haka ba kai ba likita ba wani sai nayi shiru.
Yace go ahead you say your words out, shiru nayi tare da kawar da kaina gareshi gaba daya ya sake fadin you free to say komai zaki iya fada don ance fushi kike damu.
Da sauri na jiyo ina kallon shi nace fushi fa akan may zanyi fushi daku in ba ina son sama kaina nauyin da bai hauni ba ?
Murmushi yayi da sai ka saurara zakaji shi yace kwana biyu bamu kasan ne daga ni har Yusuf na fita da madam dina ne mun tafi check up ciki ke bata matsala.
Don Allah malam ni ban tambaye ka ba in zaku iya ma ku tare a can ba damuwa na bane wanan ciki kuma Allah ya bata lafiya ya sauketa lafiya amma mi ya hadani da tafiyan ku kuma.
Kwana yasha muka shiga wani clinic inda yasa na fito muka shiga guri ya sama min na zauna ya nufi gurin tankan kati ba mu dade ba duk da mun samu mutane a gurin yace in taso mushiga gurin likita.
Mun shi likitan yare ne don turanci suke dashi sun gaisa naji likita na cewa kayi sabin aure ne ashe yace mashi eh yace madam ta kwana biyu bata shigo ciki ya zaunu ko yace eh a gadarance yake ma mashi magana yace ina son ka duba min ita tana fama da mesturalpain ne.
Yace ayya sorry madam yakamata ace ya rage maki ciwo yanzu da kiyi aure ya kamata ace kin rage jinshi haka indan zakiyi period don agana kawai matsalan hakan.
Nauyi kunya ya rufe ni a wurin na kasa daga kaina shima wayan shi yake dakila baibi ta kan likitan ba sai da likitan ya fara tambayana ina mashi bayanin ya dago yana kallo na.
Tashi nayi zuwa inda likitan yace in kwanta ya dan dadana cikin nawa na dan sake kara daidai kasan mara na daya tausa da dan karfi yace in tashi ya dawo ya zauna yana rubutu a wani farin takarda ya mika mai lokacin na dawo na zauna dakyat dafe da marana dake min tsananin ciwo sosai.
Bayan ya mika mai yayi mai bayanin anemi wanan maganin in sha zasuyi min allura kuma zan samu sauki da yardan Allah ya mika mai hannu tare da fada mai inda zamu kai takardan a duba ni.
Sai da muka gama komai muka fito yana min sannu muka dauki hanya wani shago ya tsaya yace min yana zuwa ya shiga ciki yadan jima sai gashi ya fito yaron shagon na binshi a baya dauke da wasu manyan ledoji biyu a hannun shi.
Ya saka bayan motar ya shiga muka tafi bayan ya mikawa yaron kudi yana mashi godiya kaina na duke yace sannu likita yace zaki samu sauki dan anjima kadan amma zaki barci sosai ki ci wani abu don kince baki karya ba.
Bana jin shi do murdan da mara na keyi ina dan cije baki ina jijiga kafa na da matse hannaye na duk yadda na so in daure na kasa sai da na yi ya gani a bakin down hostel din mu ya tsaya da motar shi.
Zaki kara kawar ki ta taimaka maki ne ko in taimaka maki ki fita duk da ciwon da nake ji sai dana harare shi na bude motan na fita ko godiya ban mashi ba.
Ina fita yace turo min kawar ki ta daukan maki magani kai na iya dagawa na shige ciki na samu maryam na girki a dakina din bata da kiuyar girki ita tana gani na tace har kun dawo kaina gyada mata na fada saman katifa nace yana kiranki a waje.
A saka hijab da sauri ta fita daga dakin zuwa wurin shi bata jima ba ta dawo dauke da ledojin nan da ya sayo tace yana maki sannu wai sai kunyi waya yace kici wani abu kafin ki kwanta.
Itace ta zauna ta bude ledan kayan ciyeciye ne a cikin dana sha tarkace dai gasu nan sai dayan ledan dake dauke da pad din mata always kamar mai bude shago dashi ban san ranan da zai kare ba.
Abinci ta debo min na dan ci kadan na kwanta sai barci mai nauyi ya dauke ni a gurin ban kara sanin inda nake ba kuma.
Yana fita ya daga wayan shi six miscall ya gani na Nafisa da sauri ya danna wayan ya kirata yana fadin sorry ina wani abune yasa banga kiran ki ba.
Tace Samad ina kaje wacece akace mi an ganku tare a asibitin doctor Bisi yanzu waka kai asibiti wata macs ce aka gan ku tare tare ta fada cikin tashin hankali.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Bai iya bata amsa ba sai kokatin wuceta da yake yi ya karasa cikin dakin rigar shi ta riko ta baya da mamaki ya juyo yana kallon ta.
Shi da magana take mai wuya ina shi ina tsayawa fada irin haka da mace sau da yawa nafisa takan tunkare shi da irin wanan fita tana kokarin kama mai kaya ko ta sha mai kwala sai dai bai biye mata sai dai ya shige ya kyale ta tayi ta masifanta har ta gaji.
Inda ita kuma a nata ban garen take ganin tafi karfin shi ne, dan bai da yadda zaiyi da ita dole ya zauna da ita take gani yau da ta cakuma rigar shi ta baya tana kokarin kaimai duka ya juyo da sauri yana fadin Nafisa ki na da hankali kuwa ?
Cikin shi tayi tana banda hankali sai ka fada min wacce aka ganka da ita a asibiti dazun hannu yasa ya banbare hannun ta da karfi ya jefar da ita gefen kujera.
Zafin kishi sosai ya rufe mata ido nan ta fara ja mai Allah ya isa ya ci amanan ta ya cuce ta sai taga bayan ko wacece ke son mata katsalandan a rayuwan ta.
Yan uwanta suna tsaye cirko cirko suna kallon ikon Allah sai yare ne ke tashi suna magana rai a bace suna nuna goyon bayan yar uwan su.
Harara ya watsa masu sai suka fara sulalewa daga falon kowa yana barin gurin don yanayin kallon da yayi masu din .
Sama ya hau a hankali inda yake tafiya yana jin sautin kukan Nafisa yana isa inda yake.
Tsaye yake yana balle bottom din rigar shi a hankali sai dai zuciyar shi cike yake da mamakin waya gan shi ya fada ma Nafisa cewa ya ganshi tare da wata mace a asibitin doctor Bisi.Doctor Bisi ne ya fada a ranshi sai kuma yace No it can't be doctor bisi is a man he can do such full to me.
Beside, ma nine na hadasu da doctor bisi din anan don bata san kowa ba a Abuja sai zuwan da yayi da ita ne tasan kan garin.
Bayan wucewan mijin nata ciki ne ta watsa ma yan matan uku da suga rage a falon harara tace a cikin yaren su na buzaye.
Simi simi suka mike suka bar gurin itama mikewa tayi ta bishi ciki su karasa a can sai dai ta samay shi har ya shiga wanka ko.
Zama tayi a bakin gadon cike da masifa tana jiran fitowan shi daga wanka su aza a inda suka tsaya.
Zancen malaman ta ne ya fado mata a rai da kyat ta yaki zuciyar ta ta dan sasauta zafin da take ji nashi koda ya fito anan ya samay ta zaune cikin masifa bai kula ta ba ya fara gyaran jikin shi kamar yadda ya saba yi idan ya fito daga wanka.
Kallo daya yayi mata fuska a daure ya kawar da kan shi gare ta ta mike ta tako gare shi tace samad ka daina ganin laifina.
Ni kadai ce macen da ta dace kai a duniya da ina da iko ko macen kudi ba zan bari ta sauka a akan ka ba balle macen mutum.
Ta hade wani miyaun fitina da yazo mata a makoshi tare da fadin nasha alwashin duk macen da tayi gigin shiga gonar ka sai naga bayan ta a duniyan nan.
Kallonta yake da mamakin abinda ta fada yaga kuma gaskiyar maganan nata har cikin kwayan idon ta da gaskiya take maganan.
Kuma ko wacece wanan macen sai na tono ta a garin nan na nuna mata ruwa ba sa, an kwando bane.
Juyawa tayi ta fita daga dakin a fusace bayan taja wani uban tsuki tare da rufo kofan da karfi, binta yayi da kallo bayan ta fita ya girgiza kan shi ya tabe bakin shi gami da daga kafadan shi yace mahaukaciyar banza kawai.
Karasa shirin shi yayi ya fara gyara gadon shi don yana bukatan ya huta don ya gaji yau sosai ga maganan Nafisa da ke ci mashi rai kishi kamar wace bata da hankali.
Gadon ya hau ya kwanta bayan ya gama gyara yana sauke ajiyan zuciya a hankali may Nafisa take nufi da kalamin ta na sai taga bayan khadija.
Yasan zata iya abinda ta fada mashi a yanzu karfa ya ja ma yarinyar mutane matsala a rayuwan ta don bai san abinda Nafisa zata aikata mata ba.
Tunane yayi kada ya sare Nafisa ta samu daman da zats yi mai abinda taga dama a rayuwan shi don haka zuciyar shi ta bashi shawaran gwada Sa,an shi akan khadija ko zai yi nasara akai.
Bai koma ta kanta ba yadda ya saba binta yana bata hakkuri har sai yaga ta hakkura yake samun saida a ranshi wanan karon sai yaji ba zai iya tunkaranta ya bata hakuri ba akan kuskuren da take tuhumar shi da aikawa ba.
Kamar yadda Nafisa itama a dakin ta take zaune abin duniya duk ya damay ta ji take tankar tayi hauka don bacin rai wai yau samad din tane yakai wata mace asibiti ba ita ba.
Wai wacece wanan da samad har ya iya tunkara da sunan so may take dashi may take tunkaho dashi a duniya wanda ake cewa tafi ta komai.
Zubur ta mike ta fara zagaya dakin duk da dan cikin ta dake mata motsi a lokacin bai sa ta damu ta tuna da yadda take kaunar cikin nan ba.
Kishi ne zalla a rayuwan ta kawai so take tasan wacece wanan yarinyar don tasan ta inda zata iya fito mata da shirin ta.
Tana yi nata kallon lokaci don tasan dole yazo gare ta idan ta yi mai irin wanan boren nata sai dai a yan watanin nan tana ganin abubuwa suna son sauya mata sallo ga aikin ta.
Shiko Abdul a dakin shi yana kwance barci yaki zuwa mai a lokacin tunane kala kala yayi shi a wurin Yusuf ya kirashi yana tambayan shi ko yaji yaya jikin nawa don ya kira wayana yana a kashe.
Yace ban kirata ba don likita yace zatayi barci sosai a idan maganin ya fara mata aiki a jiki wata kila ta samu barci ne ta kashe wayan.
Nan yake labarta mashi yadda suka kwashe da Nafisa da ya dawo gida hankalin Yusuf ya tashi yace sai nake zaton doctor ne ya fada mata tunda kace baku hadu da kowa ba a gurin.
Yace idan shine ya fada mata kuwa yayi kuskure don cikin shi tayi don zan can za wani likita ke nan yanzu.
Yusuf yace baka tunanen kada Nafisa ta gano a inda khadija take tayi mata wani abin yace haka ma ba zai faru ba zanyi tunane mafita akan hakan.
Sukai sallama bayan sun gama tataunawa ga maganan ya kashe wayan yana gyara kwanciyar shi a hankali.
Bai dade da gama wayan ba yaji an turo kofan an shigo dakin yasan ita ce don ita kadai ce mai shigo mashi daki.
Ta karo gaban gadon ciki da mamakin ganin shi a kwance da tayi cikin rashin damuwa da ita har ta iso a gadon ta zauna tana fadin nasan ba barci kakeyi ba.
Ya dago ido ya dan kalle ta yace banyi barci ba kuma hutu nake so a yanzu ta gyara zama tana kallon shi tace samad cikin sanyayar murya.
Wai may na rage ka dashi a duniya may ye wanda ban maka har kake kokarin hadani da wata mace a duniya bayan kasan irin son da nake maka ba na wasa bane.
Ta kamo hannun shi tana fadin gaba daya ka canza min a yan watannin nan ko dan ka gani da ciki ne ka dauko yimin hakan.
Ka hana mu kwanciyar hankali gaba daya a gidan nan sai faman takura min kake yi ko yaushe.
Sai ga hawayen da yaki zubu mata a daki yazubo mata a lokacin tace ko wacece sai na kashe ta a garin nan idan na gane ta.
Cike da jin haushinta yace ashe ko ke ma za a kashe ki ke nan kinga matsalar ki ko meyasa ne har kullun

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login