Showing 45001 words to 48000 words out of 142410 words

Chapter 16 - MIJIN BUZUWA COMPLETE

Start ads

08 Aug 2025

24

Middle Ads

Yusuf yace mu zabi abinda muke so ni wani jakka da takalma kawai na dauka maryam kuma ta dauki wani dogon riga da jakka.
Munje gun biya muka da ja baya naga ya ciro katin shi na bakin ya basu suka debe kudin su suka miko mai mun shiga motar mun zauna.
Yace kina ganin mun sai komai da zasu buta nace insha Allahu har maman su ma da sauri ya juyo yadan kalle ni kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa yusuf yaja motan muka tafi.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUHutun sati uku kacal muka samu wanan karshen zangon don haka naji dadi sosai da bai kasance dogon hutu bane don zan samu zama a minna tare da iyayyena in yi hutu.
Wanda rabo da in samu kasancewa dasu haka a wadace har na manta yanzun haka na fito daga zana jerabawan karshe na wanan zangon da mukayi da yazo min da rikicin haduwa da Abdulsamad da abokin shi Yusuf.
Ba ranan zan tafi ba sai washe gari don haka maryam ta tsaya jirana don taso muje gidan yayar ta na nuna mata ban son zuwa can din.
Komai na gama shiryawa a dakin sai kayan da zan saka ne da katifa ban samu daga wa sama ba don kwantawa da zanyi na yau kawai da safe in dage shi sama in tafi gida.
Bayan mun rabu dasu yusuf ya kirani yana tanbaya na ya muka isa hostel din mu tare da kara yi min godiya .
Bayan mun kashe wayan gidan Abdulsamad suka nufa sun kusa shiga gidan ne Abdulsamad din yace dashi idan sun tafi kada a sauke kaya da aka sayo a gidan shi abar kayan acikin mota kawai idan sun isa Yusuf yagane manufan shi na fadin haka.
Sai dai bai ma abokin nashi magana ba gamay da abinda ya fahinta na son kada a sauke kayan dayace kada ayi har lokacin gidan ba dadi tsakanin su da Nafisa.
Wanka ya fito yana goge ruwa akanshi ta shigo dakin har lokacin tana nan cikin fushinta da shi zuwa tayi tambayan shi kudin da tayi requesting wana zata yi tafiya zuwa gida.
Tace Samad kwanaki na ta matsowa har yanzu bakai magana kan abinda na bukaci ka bani ba wanda zan je gida dashi indan zan tafi sai in wuce dashi.
Yadda take magana bai sa ya daga kai ya kalle ta ba Samad dakai fa nake magana ya dan wuce ta zuwa bakin gado ya zauna .
Ta juyo gareshi tace magana fa nakeyi maka kana ji kuma ta fadi a hasale sai lokacin ya dago yace kada ki kara yi min maganan nan.
Don bashi ke gaba na ba gobe kaduna zan tafi in daba iyayye da iyali na wani irin gumzi tayi tayo kan shi tana fadin wallahi baka isa ba.
Ba kuma inda zaka kaje na fada ma don baka fada min zancen tafiya ka ba don haka ban shirya ma tafiyan ka yanzu.
Murmushi yayi yace kice ma mai shirya min tafiyan don kece zaki sallamay ke nan ko ?
May kake nufi da wanan maganan haka ban ci na sani bane idan za kai tafiya yanzu koma ko da da kake fada min ni nake sa ka fada min .
Yace shine kuskuren da na aikata a baya yanzun kuma a shirye nake da na gyara komai da ya faru ido ta zuba mai cikin firgici take.
Ganin zata damay shi yasa ya fice ya bar mata dakin don da dakin yaso ya gyara kafin ya kwanta don ya kwana biyu ba samu tsayawa ya gyara ba.
Don yanzu gyaran dakin kwanan nashi ya dawo kan shi saboda indan yan uwan nata sun mashi gyara sai abubuwan da dama suyi ta bacewa a dakin.
Wanan yasa ya daina bari su shiga mai daki suyi mashi gyara sai shi ya ke gyaran dakin nashi da kanshi ya don yafi mai sauki idan bai gyara ba ita bata da lokacin gyaran .
Haka kuma zata shigo ta kwanta a cikin dakin ba kunya ba tsoron Allah haka dai ake rayuwan a dunkule ba wani jin dadin irin na aure tsakanin mata da miji.
Laptop din shi ya dauko ya na dubawa sai dai tunane ya hana shi yin wani aiki a ciki bakomai yake tunane ba sai irin maganan da nake fada mai, mai kama da shagube yana jin haushi na ashe gaskiya nake fada mashi.
Yaushe rabon shi da yaran shi suzo kusa dashi su zauna a matsayin shi na mahaifin su suji dadi babu.
Ya tanbatar da ya tafka babban kuskure da Allah zai iya kama shi da laifin da ba zai iya amsawa ba gobe kiyama.
Khadija khadija ya furta a hankali kin taimake kin ceci rayuwana ta yadda ban taba zato ba wanan wace irin yarinya ce mai hikimà da basira.
Ya dade a wurin zaune har ya kai kwance sai da wayan shi yayi ringing ya daga wani yaron shi na wurin aiki ke gaya mai an samu wasu filaye ns gwaunati a gwagwalada da wasu mutane ke son ci.
Yace da yaron nashi ya bari sai next week za a duba case din idan Allah ya kaimu sun gama waya kiran Yusuf ya sake shigo mai inda yake fada mai gashi a kofan gidan shi sin dawo da motaci an gama duba su .
Yace gaya nan fito mikewa yayi ya zura santala santalan kafan shi cikin wasu budaddun takalma ya sauko zuwa kasa inda ya samu falon cike da yan uwan Nafisa kamar suna shawara.
Ganin yadda ya fito yasa ta dago kai tana kallon shi ya fito ya samu Yusuf din zaune a saman dan wani dakali yana jiran fitowan shi.
Ya fito ya fara mai baiyanin komai basuyi aune ba sai ganin Nafisa sukayi a gaban su tana huci ba bata lokaci ta shiga dura ma Yusuf din zagi tana ai banta shi.
Bai tanka ta ba sai faman kururuwa take masu a kai tana kiran da munafuki dan bakin ciki ko bai so sai ya gansu da Samad agidan shi.
Dama tasan duk wani munafuncin da ga wurin shi yake fitowa daga shi har samad din sai ta dauki mataki a kansu.
Amma dai karki manta bakece Allah ba ko don haka babu wani abin da zaki iya muna sai Allah don in da sabo ya saba da wanan halin na Nafisa.
Sau da yawa idan sun kwaso rikici da mijin ta a kanshi take saukewa don tana ganin shine mai zuga shi sai taga ta kamo shi da kyau dan lokaci kadan kuma sai abin ya juye mata.
Wanda take ganin Yusuf din ne ke mata zagon kasa a hakan sai dai bai nasaran rabata da Yusuf din da yake son yi ko yaushe.
Da kyat yan uwanta suka samu takoma ciki bayan sun kare masu kallon banza suka shige da ita cikin gida tana ta haure hauren rashin mutunci.
Washe gari tun da safe ya shirya Yusuf yazo zasu tafi kamar yadda ya saba motoci uku zasuyi tafiyan da shi sai dai wanan karon tafiyan ya canza masu sallo.
Na farko su kadai ne ba tare da buzuwa ba na biyu kuma tare da a abin arzikin da bai saba tafiya dashi ba zasu dunfari gidan.
Ana kara gyara kaya kamar daga sama sai ganin ta sukayi a wurin motacin tana ganin kayan ta shiga tonawa har ta gano abinda ke cikin buhuhunan da akayi siling din su din.
Ranan sun ga masifa haka sukaja mota suka tafi ransu bace da halin da Nafisa ta nuna masu din sun isa a cikin lokaci gari bai je gidan ba sai da ya karasa gidan shi ya huta don sun iso kan shi yana mashi ciwo sosai saboda hayaniyar da baiso.
Tunda Yusuf ya sauke shi yanufo gidan nasu da abinda suka zo inda sai gani motane keyi anata shiga da kaya a cikin gidan ana jibgeasu a kofan hajiya mama kamar yadda ya umurce shi da yi.
Sun kasa boye mamakin su anty amarya ce ta fara tambaya anya wanan abin da Nafisa ko aka zo wanan karon dariya Yusuf yayi yace bada ita bace anty muka dai muka zo.
Mommu tace abin kan da mamaki gaskiya Allah yasa babangida ya canza daga wanan karon dariya Yusuf yayi yace insha Allahu mommy kudai taya mu da addua.
Ya shiga dakin hajiya mama don ya gai da ita ya samay ta da yan matan ta suna mamakin wanan sayyayan da suka gani haka wai daga gun Abdulsamad ya fito haka ?
Ya shiga dakin sai da ya zube kasa ya fara gaida ita sai faman murmushi take yi har lokacin ta kasa boye mamakin ta bayan sun gama gaisawa dakin take tambayan shi wanan sauyin yanan Abdul din data gani.
Yace hajiya adai taya mu da addua kusan kece sillar canzawan nan nashi lokacin fada maki komai baiyi ba amma nan gaba insha Allahu zan sanar dake komai so nake komai ya tafi haka yadda muke so dashi .
Don yanzu insha Allahu akwai canji sosai wallahi nan dai suka dan taba hira yace Abdulsamad na tafe zamuyi bayananin komai idan ya shigo.
Duk da zaman lafiyan da akeyi gidan bai hana a kebe gefe ba ana gulman wanan sabon yanayin da aka hango a gare shi.
Sai dai kowa ya matsu yaga abinda ke cikin buhuhunan wanda ba wanda ya iya gane komau ye a cikin su su indan gaiyan aikin nasu ya shigo.
Saida suka sauko sallah jumma a ya shiga gidan iyayyen nashi a falon Alhajin su ya fara shiga ya gaida shi da mashi yaya jiki ranan yaga sauyi sosai na sakin fuska a wurin mahaifin nashi wanda ya dade bai gani ba.
Bayan sun gama da mahaifin nashi ne ya shiga ciki ya fara gaida ummi sai mommy sai anty amarya ya wuce dakin hajiya mama wanda dama kullun itace karshen shiga da yafito kuma sai ya bar gidan.
Sun gaisa da ita acikin sakin fuska ya dubi Affan dake zaune gefenta yana cin abinci ya kira yaron saboda rashin sabon da basuyi ba dashi ya dago ya kalle shi kawai ya gaida shi.
Sai baiji dadin yadda yaron yayi mashi ba shiru ya dan biyo dakin take tambayan shi iyali ya amsa da duk sina lafiya hajiya tace dole ita da yan uwanta zamu tambaye ka don sune yanzu iyalin naka.
Babangida yanzu kana ganin abinda kakeyi kana aikata daidai a rayuwanka mutum ya watsar da iyalin shi ya rugumi wasu bare can.
Shiru yayi ya dukar da kanshi tace kaima kanka fada kada ka mutu a cikin wanan halin kasan Allah na zai barka ba Yusuf ne yace ayi hakkuri hajiya komai zai zo daidai in Allah ya yarda adai tayamu da addua.
Nan ya fara mata bayanin kayan da suka zo dashi inda ta fahinci komai yace saura kayan abinci muyi magana ko za a kawo zuwa yamma sai a raba yadda ya kamata.
Yayi mamakin yadda yaji mahaifiyar tashi tana kwararo mashi addua yau da saka mashi albarka wanda ya dade baiji ba daga gare ta duk zuwan da yake yi da fada sukan kare ya fita rai a bace.
Yau sai gashi sanadin yarinyar da yake gani mai matsala a gare shi yaja mai samun addua irin haka a gurin mahaifan shi bai fita gidan ba sai da yayi masu alheri yakuma mata alkawari zai je zaria yayi masu taaziyan rashin da akayi can.
Taji dadin jin hakan sosai na ya fito ya barsu a cikin farin ciki ya koma gidan shi don yana bukatan hutu a lokacin bayan fitar shine hajiya ta kira su mommy tana masu bayani aka shiga bude kayan da ta nuna masu din.
Kowa yayi mamakin ganin hakan don basu zaci haka ba yanzu a gare shi sai addua suke mashi da fatan gamawa lafiya kowa aka cire mai nasa cikin farin ciki da jin dadi.
Tunda ya koma wake kwance a dakin shi na gidan ba abinda yake tunane sai irin yadda na fada mai magana mai amfani acikin gatse kuma yayi mai tasiri.
Yani yace a ranshi lalai ya zama dole in san yadda zan gyara alamarina da yarinyar nan don ita din ba abin yar wa bace .
Cikin dan lokacin kadan tayi min sanadin dawo min da farin ciki tsakani na da iyayyen har da yan uwa wanda wanan tunanen bai taba zuwa min ba ko wani ya tsayar dani ya fada min gaskiya yadda take fada min kai tsaye.
Tayi namijin kokari wurin ganin ta tsaya ta fada min maganna irin haka kai tsaye bataji shakka ko nauyin fada min yadda kowa ke shayi na ba.
Wayan shi aka kira ya daga Faiza ce take mai godiyan abinda aka kawo masu yace babu komai ta kashe kuma Lawisa yar wurin ummi ma ta kirashi tana mashi godiya haka suka dinga kiran shi sai da yagaji ya kashe wayan shi ranan.
Wani irin farin ciki yake jin kanshi ciki mara misaltuwa da wanan kiran da yan uwan shi suke mai a lokacin don ba zai ce ga ranan da suka kirashi karshe ba.
Ya zama dole gare shi ya san yadda ya gyara mu,amulan shi da duk wani dan uwa nashi da ya watsar da farko.
Sai yaji yana sha, awan ya kira layin khadija a lokacin yayi mata godiya haka yasa ya jawo wayan shi ya kira layin ta.
Ina fitowa cikin makaranta na samu guri na zauna ina jiran maryam tafito mu wuce cikin gidajen mu don an kara muna kwana daya yanzu.
Kiran shine ya shigo min wanda tun bayan rabuwar mu ranan ban kara ji daga gare ba sai yanzun da ya kirani din na tuna dashi.
A hasale na dauki wayan ba tare da nayi magana ba don na gane shine jin shiru ya danyi yawa banyan na dauki wayan sai nace
A hasale nake fadin lafiya ka kirani ko ka kirane ka fada min ka tsane ni din da kake fada min ko yaushe ?.
Murmushi naji yayi kasa kasa sai ya sake kiran suna full yace khadija a zuciye nace ina jinka ai yace ba wanan kiran nayi maki ba yanzu.
Nace may ye ka kira malam ni kada ka bata min lokaci haushi ne ya ishe shi a lokacin yana rayawa a ranshi yaya zai yi dani ne wai ?
Cikin sanyi murya yace min thanks khadija na gode kwarai da taimakon ki gare ni sai dai don Allah, , , ,
Dama abinda yasa ka kirani ke nan don ka samu wani sabon yaudara ka zageni kuma dashi na fahince ka don haka banda lokacin ka ni yanzu.
Na fadi a cikin tsigar tsokana tare da saurin kashe wayan sai dai a zahiri jikina yayi sanyi da yadda naju yana maganan cikin wani yanayi.
Shiko ina kashe wayan yabi wayan da kallo kamar nice wayar ya sauke wani irin ajiyan zuciya yana fadi a fili shi kadai a daki.
Wanan yarinyar ni yaya zanyi da ita ne wai ta fahince ni yanzu ya girgiza kai yace kina da matsala khadija yarinya haka bata da kwaciyar hankalin fahinta.
Why why khadija baki so na da kwanciyan hankali a tare dani yanzu ne mikewa yayi daga kwancen da yake ya nufi fridge ya dauko goran ruwa mai sanyi a ciki ya kwankwada tare da wurgi da goran ya fito falon shi.
Mutane ya samu sunzo gaida shi inda ya bisu da alheri sai yamma lis ya samu suka rage nan ya nufi bathroom din shi don ya dan watsa ma jikin shi ruwa ko zai ji sanyi.
Dan ruwan dumi ya hada saboda yanayin garin na kaduna ya shige jacuzzi ya dan dauki lokaci yana tunane kafin ya fito ya sa kaya a jikin shi ranan a maslcin uguwan su yayi sallah magariba tare da jamma, an unguwa da mahaifin shi aciki.
Ba abinda yake tunane sai yadda zai samu mu shirya a tsakanin mu gashi dan lokaci kadan yarinyar ta shiga zuciyana ta samu wuri a ciki.
Tunanin yadda zai shawo kaina amma ya kasa samun mafita har wanan lokacin shigowan suraj soja wurin shi yasa ya matan halin da yake ciki don sun dauki lokaci dashi suna fira kafin Yusuf ya shigo mai da abincin da mommy ta girka masu.
A tare da Suraj da Yusuf din sukaci abincin suna hira a tsakanin su bayan fitan Suraj ne suka samu kebewa da Yusuf wanda tun bayan zuwan su basu samu zama a tare ba.
Nan yake kara mai godiyan kokarin da yake mashi inda yake sanar dashi ya kira ni don yai min godiya amma naki fahintar shi Yusuf din yace ya sake kirana zan fahince a hankali.
Ba laifi yace dashi sun dan dauki lokaci sukayi sallama akan da safe zai shigo su tafi zaria idan sun dawo yana son kuma ya dan je wurare masu muhinmanci a kaduna daya dade bai tafi ba.
Yusuf na fita ya kira waya maryam ta dauka ta miko min bayan ta dana recieve na dauka da sallama na kara a kunne na.
Bayan mun gaisa ne yake rokona da in karba wayan abokin shi inji may zai fada min dariya nayi tare da

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login