Showing 15001 words to 18000 words out of 142410 words
masu gida an bar mata gida tana yadda take so ita kadai tayi hankali wallahi da iyayyen nan namu.
Shiru yayi yana nazarin maganan abokin nashi baice komai ba san cen yace kasan hajiya don jan magana cewa tayi gobe da wanan yarinyar zamuyi tafiya.
Ina Yusuf ya tambaya da sauri yace wai Abuja zamu tafi a can take tace nowarder idon ta yake a bude haka bata da tsoro da ganin ta ai.
Na karbo dinki na dawo na shirya kaya na bayan na gama komai na zauna ina tunanen yadda tafiyan mu zai kaya a goben.
Ya Amina ta ban abinda zata bani taja min kunne don Allah kada in kula buzuwa har mu isa nace ni ina ruwana da ita su dai kaini su sauke kawai.
Da safe ya Amina ta tana dani da wuri na shirya jiran kawai nake ace in fito mu tafi ya Amina tace in dauki jakkana da sauran kayana inje dasu gidan su mommy nace ai wanan ya zama tonon asiri haka .
Ni madai su wuce idan haka ne dole ta kyaleni don ba yadda zatayi dani na gama komai har da karyawa ya Amina ta sani yi da safe don tafiyan da zamuyi din.
Can sai ga su Binta sun shigo wai in fito da kayana ga su buzuwa nan sun fito suna ciki suna sallaman su mama zasu biyo nan su dauke ni inji mama.
Tashi nayi na fara fito da kaya na waje suna tayani fitarwa kofan gida sai ko ga motan su ya tsaya suna baya dashi da buzuwa gaba zan zauna dani da driver su.
Ina jin ya Amina tana gaida su binta ta bude min na shiga duk da kamshin turen su amma nawa ya karade motar har na shiga na zauna ban yi masu magana ba ina daga wa su ya Amina hannu muka tafi.
Tsayawa sukayi suna bin motar da kallo Binta tace yau akwai tafiya a wurin nan jifa yadda anty Nafisa ke cika tana batsewa kamar ta fashe.
Zainab tace suna daidai da khady ai ta fita iskanci daidai zasuyi a motar niko saida aka fara tafiya na dan juyo nace dasu ina kwanan ku murya can ciki bai fita.
Ina kokarin cire airpies dina na sa a kunnuwa na tare da sake kira, a a wayan na lumshe idanuwa a hankali ban kara bi ta kansu ba kuma.
Tun ina bi sai dan barci ya dauke ni ina yi ina falkawa na gyara zama tare da dan satan kallon su ta karkashin idanuna na naga yadda suka zauna manne da junan su sai dai aiki yake a laptop din shi.
Ita kuma tana gyangyadi daga zaune da yake lafiyayun motoci ne kafin wani lokacin har mun kusa isa Abuja driver yaiwa magana yatambaye ni ina za a sauke ni .
Ya juyo idanuwa suna lumshe ya dan taba sit din na bude ido tare da cire airpies din dake a kunne na yace yallabai yace a ina za a sauke ki ne ?
A hostel nake zaune na bashi amsa ya juya gun ogan nashi yana fadamai abinda nace mai bai kara magana ba har muka shiga gari.
Ban ankara ba sai naga suna shiga jerin gidajen dake asorock a wani gida motar ta danna kai suka shiga katon gida ne mai wani babban get ginin gidan sai mutum yace a turai yake sai lokacin na cire airpies din kunne na naji buzuwa na fadin ita a ina za a sauke ta banji may mijin ya fada mata ba nidai ban fita motar ba su kuma sun shige ko godiya ban masu ba.
Driver ya shiga masu da kaya ciki ni dai sai bin gidan nake da kallo a raina nace shiyasa yake abinda ya ga dama ashe yasan abinda ya taka,
Ga wasu manyan motoci gudu uku a fake wata katuwar jeep ta dauke min hankali har ina satan kallon ta a wurin motar sai sheki take tana daukan ido da gabin ta sabuwace.
Sai dai ga daular duniya matashi dashi amma ya kasa auren yar kasamu suci arziki a tare sai wata bare ce buzaye ne gidan naga suna fitowa daganin su kasan yan uwan buzuwa ce ba sai an fadi ba nace mijin hausa ke nan inwar giginya na nisa ka more ka.
Driver ne ya fito tare da wani dan saurayi buzu a baya shi yana dauke da tire da drinks yace gashi mai gida yace a kawo maki No na gode na fada tare da juyawa da kaina gefe a can cikin gida kuwa fitina na tsakanin buzuwa da mijin ta.
Wai sai dai in shiga motar haya akaini hostel bata yarda ya wuce su sauke ni ba dole yasa driver yakai ni sai ya dawo ya kai shi office daga baya.
Mun kama hanya driver ke cewa kai matar oga akwai kishi yanzun haka ta rike shine ciki wai bata yarda ya fito atafi kai ki dashi ba.
Murmushi nayi nace mahaukaciyar banza kawai itake nata haukan ni ko a jikina yace nayi mamakin yadda ta yarda aka dauki ai nasan shi take ma fushi har muka zo ba shiri a tsakanin su.
Surutun nashi ya isheni don haka nakawar da kaina gefe kamar ina kallon titi don abokin gulma yake nema da alama ganin na kyale shi shima yaja bakin kishi yai shiru har muka isa gidan da nake ba a cikin hostel sai dai gidane na haya da yan makaranta ke kamawa.
Driver shi ya taimaka min da kayana har zuwa bakin gidan namu ya shiga min dasu sai dai bai shiga ciki ba kudi ya miko min yace gashi oga yace idan na sauke ki in baki.
Dan jimm nayi kamar bazan karba ba sai dai nasa hannu na karba tare da fadin kace nagode sai dai ban faye karban irin kyautar nan ba kallo na yayi ganin na fara jan trolley dina yasa shi wuce yana mamaki na a ran shi.
Dakina na bude wanda mijin ya Amina ne ya kama min hanyan shi dakine ciki da falo da bandaki a cikin sa sai inda mutum zai danyi girki daga waje haka dakunan suka a jere har dari da wani abu.
Dakin yayi kura dan sati biyar din da nayi ban ciki daga kofa na aje kayan da na dawo dashi na fara gyara dakin tukun sai da na sharo ko ina na dakin.
Na mayar da komai yadda nake son shi na fito ba zan iya fita ba haka yasa na kwanta don in sauke gajiyan dake jiki na a lokacin.
Ba wanda yasan na dawo do haka na rufe kofa na kwanta abina sai barci mai nauyi ya dauke ni a cikin barci sai gashi wai muyi mumunan fada da buzuwa mijin kuma na tsaye yana kallon mu baiyi magana ba.
Falkawa nayi don kiran wayana da akeyi na lalubu wayan da kyat saboda barci da yaci idona ya Amina takirani.
Ina dauka naji muryanta tana cewa ina kika shiga ne haka waya nata kara baki dauka ba cikin muryan mai barci nace wallahi barci nakeyi anty.
Tace yaya kuka sauka shine koki kirani hankalina ya kwanta nace wallahi lafiya kalau muka sauka tace badai wani matsala ko ke da buzuwan ki ?
Naja guntun tsaki nace suna can gidan su muka sauke su driver su ya kawo ni hostel ni komai bai hada mu ba a motan bayan gaisuwa.
Tace to barin barki ki huta an jima zan kira son naga yanzu barci yaci karfin ki nace ai na tashi yunwa ma nake ji yanzu tace to ki samu abinda kikaci kin san kina da ulcer nace yanzu zan tashi.
Baki sayo komai ba ma ke nan nace yau na gaji ne anty ba zan iya zuwa ko ina ba sai dai gobe idan na fito lecture.
Allah yakai mu tace muka kashe waya ina jin dadin yar uwa ta sosai saboda kulawan da take bani na musanman shiyasa nima nake mata komai kamar ita ta haife ni.
Mafalkin da nayi ne ya fado min a raina lokaci guda yake dawo min dan dariya nayi nace ikon Allah wanan buzuwar kamar manya ta tsaya min a rai haka ?
Sai a lokacin kudin da driver nan ya bani ya fado min a rai na jawo jakka na daga kwance na kirga kudin ido na zaro ganin har dubu hamsi ya bani nace wanan yasan zafin kudi kuwa ?
ZAINAB IDRIS MAKWA
SEENABUBai yi mamaki shigowa ya samu abinda ya gani ba a gidan don ba yau bane farkon yin haka gare ta don a duk lokacin da ta ganshi ya rabi wata mace ba aita ba ko kannen sa da suke uwa daya ko uba daya ba hakan take mashi wannan haukan a gida.
Don sani yadda suka rabu da ita kafin yaje office akan kawai mahaifiyar shi ta bashi umurni ya bi na su rage min hanya zuwa abuja kuma a motar shigan su.
A hankali ya kusa kai cikin falon su na sama ga tarin gajiya a jikin shi daya kwaso yau ga na tafiyan da sukayi ga ya zo ya samu aiki a office.
Hankalinshi yayi matukar tashi saboda ganin yadda tayi kaca kaca da falon komai ta har gitse ta fasa na fasawa ta watsar dana watsarwa a kasa.
Hatta tv bango ta tarwatsashi ga crystal glass da aka aje don decoration din falon a folon a kasa ta tarwatsa duk komai na falon a har gitse kamar ta haukace.
Tsayawa yayi a daga kofa yana bin ko ina da kallon mamaki a ranshi kuma yana mamakin irin zafin kishin Nafisa.
Wanan wani irin kishine haka shi bai da dama ya sake da wata mace a rayuwan shi sai ita duk da tasan neman mata ba halin shi bane.
Wanan wani irin rashin hankali ne ko kishi haukane kinshi Nafisa ba ba bai san yadda zai fasarashi ba don abin baiyi kama dana mai hankali ba.
Shi dai tun farko bai fada mata da ita kade zai zauna ba a rayuwan shi kuma tasan yana da mata tayi ta nacin sai da ya yarda ya aure ta.
Amma kuma shigowan ta ta hana shi zaman lafiya da iyalin shi da mahaifan shi gaba daya halin Nafisa idan ya motsa sai yaji nadaman auren ta dayayi.
Amma kuma idan komai ya wuce sai ta koma kamar ba ita ba shi dai wanan abin yana matukar damun shi wallahi.
Dakin barcin su ya nufa inda ya hangota takure a wuri daya tayi kuka tagaji ta ba kanta hakkuri jin an shigo dakin yasa ta dago kai cikin fushi don taga ko waye ya shigo mata daki.
Daga kofa ya tsaya ya kare mata kallo da kyat ya bude bakin shi yace wanan wani irin rashin hankali ne ko kishi haukani a garin ku ko kwakwalwan ki ya tabo ne da zaki min hassara irin haka don bake ke saye ba ko ?
Ya ka maganan cikin fushi yana hararanta a harzuke ta dago tana huci tana fadin eh hauka nake kuma a kan ka wallahi kadan ka gani duk kace zaka hadani da wata mace a duniyan nan abinda zan ma sai yafi wanan.
Yace oh ashe kina da aiki kuwa don dai ni namiji ne mijin macd hudu so zan iya aure a duk sanda nayi raayin hakan.
Cikin wani murya tace wallahi karya kake baka isa kace zaka hadani da wata kishiya can ba ni ni kadai ne matar ka, ka sani.
Oh dama tunanen ki ke nan amma kafin ki shigo kin samay ni da wata matar ko amma sabods zafin kishi irin naki ki hana mu zauna lafiya da ita.
Kaima kasan abinda ba zai yuyu ba ke nan ka hadani da wata mace may na rage ka dashi a duniyan nan wani irin kulawane baka samu a gare ni da sai ka hango wata a waje.
Cikin mamaki yace wana na hango a yanzu din kuma wa kika gana kula haukan ki dai ke nuna maki hakan mahaukaciyar banza kawai.
Indan kai ba baka hango ba ai mahaifiyar ka ta hango maka ita in bashi ba may ye nace wa sai wata ta biyomu a motar mo inba son hada fitina ba.
Yace Nafisa rashin hankalin naki har yakai ga mahaifiyata haka tanan kika biyo kuma Nafisa kan mahaifana tace in ba haka ba ne may take nufi yasa ta hado mu da ita ?
Yace cikin daka tsawa karki kuskura ki kara fadin wani maganan banza akan haka rakin zai baci sosai a gidan nan daga haka ya juya zaj bar dakin sai kuma ya juyo yace.
Ki tabbatar da kin gyara dakin nan da kan ki kuma ki mai da komai da kika fasa in ba haka ba wallahi zaki ga bacin rai na a yau din nan.
Sannan wani magana guda kada ki kuskura ki kira wani dan aiki yazo ya kwashe wanan barnan da kikayi ke da kan ki nake son ki kwashe shi daga haka ya fice ya shige wani daki a gidan.
Bin shi tayi da kallo don tasan ya hau sosai ga abinda tayi din sai yanzu nadama yazo mata a rai ga abinda ta aikata don tasan gaskiya ya fada mata kuma zuciyar tane kawai ya bata hakan ta hau ta zauna akai.
Gashi ta jawa kanta aiki don abinda ya fada har cikin ranshi ya fada duk dan aikin da takira ya gyara mata tasan abakin aikin maishi yake.
Gashi duk yan uwanta ne na jini babu wanda zata so a kora a cikin su haka yasa ta mike dole a cikin daren nan ta fara gyaran duk inda ta bata din.
Dakin yake yayi wanka ya sauya kayan shi zama yayi tare da dauko laptop din shi ya duba sai dai ya kasa aikin da yake son yi a lokacin tunane halin Nafisa yake yi.
May take nufi dashine ya tun haduwan su na farko da ita a bakin ma aikatasu yazo shigewa ta miko mai hannu tana fadin baba bani kuddi.
Kallon mamaki ya tsaya yana mata tare da waigawa baya ko da wani take magana bashi ba sai yaga babu kowa a wurin sai shi kadai tsakanin shi da mutane akwai nisa ta sake mika hannu tana fadin baba bani kuddi.
Yace kudin may zan baki tayi mashi alama da hannu abinci zataci alhalin su ke sai da abincin dayake shi mai tausayi ne kamar yadda mama ta koyar dasu na taimaka ma nakasa dasu sai ya ciro dari biyar ya mika mata da sauri ta karba har kasa tana mai godiya.
Ta nufi rufan sai da abincin nasu ta mika kudi yana kallo aka bata abinci ta koma gede tana ci a haukace kamar mai yunwa.
Tun wanan ranan idan yazo zai shige zata taso tana fadin baba bani kuddi sai ya mika mata dari biyar taje ta karya dashi.
Har shakuwa ya shiga tsakanin su mai karfi ko bai ganta ba zai aje mata dari biyar din nan kudin karyawanta yakawo mata yace ga kudin abinci nan.
Tsaki yaja ya rufe laptop din tare da kai kafadan shi saman gado ya kwanta rigingine yana ci gaba da tunane shi mutum na farko da ya fara warning din shi akanta shine Yusuf.
Yace kasan fa irin mutanen nan kudi suka fito nema ido rufe da maza ya kamata ka daina bata kudin nan kar mutane suyi zargin ka akanta.
Shiko tausayi take bashi baiga zai iya kin taimaka mata ba don taba bukatan taimako aa lokacin har yakai sun fara kyaabewa da ita.
Alokacin kallon yarinya yake mata don bai dauka ta haihu ba ma sai da yaje da zancen ta gida wurin su mama nason ya taimaka mata.
Mama ta kafe ba zai dauko mata fitina cikin zuri,anta ba anyi anyi da mama tace ba zata yarda ya dauko buzuwa ba yadda take ganin a na kwashewa dasu a gidaje da suke.
Ga fati bata rage shi da komai ba tana mishi biyayya don auren gata akai masu shida ita tun yana karami sosai saboda an ga taso yazo daya da ita aka dauka soyayya suke yi dashi aka hadasu aure tare.
Ido ya runtse a haka barci ya dauke shi cikin barcin ne yaji ta a jikin shi don bata zuciya dashi duk yadda ya iya fushi da ita bata yarda fushin nasu yai nisa.
Tea na tashi na hada don yunwa ke damu na na debo danbun da mama ta bani ina hadawa dashi ina jin kida na tashi a gidan alaman adawo da yawa ke nan hakan bai sa na fito ba don har na rufe kofana a lokacin.
Na gama nayi shirin kwanciya na don kada in makara da safe ina son shiga school tunda safe in gama komai don zan tafi shopping da yamma.
Washe gari bakwai na gama komai na fito don zuwa cikin makaranta ina rufe daki ne makwaciya na ta gani tace ashe kin dawo dama naga haske jiya a dakin ki sai kuma ba sake gani ba nayi zaton idona ne ke gizo kawai.
Nace eh nadawo jiya nan dai na tsaya muka gaisa sama sama da ita don ina sauri a lokacin na samu napep da zai karasa dani