Showing 36001 words to 39000 words out of 142410 words

Chapter 13 - MIJIN BUZUWA COMPLETE

Start ads

08 Aug 2025

32

Middle Ads

nace mukai sallama dashi bayan ya gama kwatar min da hankali na.
Maryam ido ta tsura min ina aje wayan tace dani ina son nima inga ina haka da iyayyena wallahi sai dai hakan bai samu ba a gare ni don na taso ne ba tare da iyayyena a wuri daya ba.
Mahaifiyar mu sun rabu da babban tun muna kanana sai dai idan naje inkai masu ziyara dukkan su tunda riko na yadawo hannun yayata.
Nace Allah sarki lalai dole kiji sha, awan hakan gaskiya don iri haka babu daddy ni kinga iyayyena sun fi son suga nayi aure ko yaushe maganan su ke nan a kaina.
Sai dai ko yaushe auren nawa zai zo ban sani ba tunda ko sauriyi tsayayye ban kai ga tsayarwa ba a yanzu haka.
Tace to ina ga dai yazo din ne tunda ga wanan yanzu da ya fito ya fara nuna maki son shi dariya nayi nace maryam ke nan baki ganewa ne ke.
Bandai fada mata komai ba mukaci gaba da hiran mu sai goma ta koma dakin ta nima na gama abinda nakeyi na kwata.
Har na kawanta naji wayana na verviration a gefena nasa hannu na dauko wayar nace salamu alaikum.
Yar mama kina lafiya yaya ruwa , ?
Na sauke lafiyayyen murmushi nace lafiya kalau yaya Yusuf yace kina kara fasa min kai fa da yayan nan da kike kirana dashi nace kai ka saya a kira ka da sunan.
Nace yaya kuka isa gida kuma yace lafiya kalau sai yanzu na kai mutumin ki gida yanzu haka ina hanyan gidana ne na kiraki mu gaisa.
Yace bayan mun rabu dazu mun dade muna maganan ki da mutumi na nasan zai kiraki yau din na shiya na kira ki in fada maki don naga ya yarda sosai da shawarana.
Nace anya kuwa zan iya cika maka alkawarin da na dauka don mutumin naka akwai zuciya sosai wallahi ni kuma ban iya daukan haka don nice zan taimake shi ba shi zai taimake ni ba.
Dariya yayi yace a yadds kuke yi din nan shakuwa zaizo ya shiga tsakanin ku sosai zakice na fada maki watarana bagashi yanzu ya fara saukowa ba.
Idan ba ta haka na fito mashi ba da wuya yayarda mu aiwatar da komai yadda muke so amma ki daure don Allah mubi abin sannu ni dai buri na shine ki san yadda kikayi kika kara ma wanan buzuwar kadarin ta a gurin jamma,a.
Abin ne da kamar wuya yaya na sai dai zan yi kokari inga nayi yadda kuke so din yace good girl Allah ya taimaka ya bada sa,a nace amin.
Shine kuma ka yi min dawainiya haka mai yawa don Allah nan gaba kada ka kara min irin haka don hakan zai yi maida ni cikin wani yanayi daba shi nazo yi a gatin ba.
Dariya yayi yace Khadija kin san dai sutura shine mutum yanzu don haka farawa akayi don ina son ki goge sosai ki fito a cikin classes ladies ta yadda zamuji dadin aiwatar da komai a cikin sauki nace to na gode sai dai a rage don Allah.
Kada kiji komai mana lokacin kine yayi kawai ki kwantar da hankaki kici arzikin ki a saukake wanan ba komai ba kada ki damu da hakan don har motan shiga ba dadewan nan ba zaki samu in komai ya tafi daidai.
Zanyi magana ya katse ni da cewa na iso gida zan shi sai dai indan mun kara waya don yanzu zamu rage haduwa sosai kada a zargi wani abu a gare ni.
Mun gama wayan ina mamakin su kudi kamar na sata haka nikan ban cika amincewa da irin haka ba azo ba a daidaita ba shirin mu ya watse abarni cikin wahala daga baya.

A hankali ya shigo gidan babban falon su ya samu su hidaya da sauran yan su zaune suna shan bakin shayin su na buzaye.
Gaisuwa sukayi bai tsaya ta kansu ba ya shige ciki bai jin dadin yadda suke cika mashi gida a ko wani lokaci haka.
Duk da wani lokaci abin yana taba mashi zuciya ganin yanzu babu wani nashi da yake zuwa wurin shi kamar lokacin da suke zaune kano da fati .
Yan uwan shi na yawan ziyarar su maza da mata amma tunda abin ya juye haka sai dai kulun idan ya dawo gidan ace mai akwai bakin da suka zo daga kauyen maradi.
Dakin ya nufa ya tura kofa a hankali dakin na nan a yarda ya barshi da safe ba a gyara shi ba in zai iya tunawa yau kwana uku ke nan bai samu lokacin da zai tsaya ya gyara dakin ba.
Don cikin yan kwana kin nan suna zirga zirgan filin da suke son saya a kubuwa ga kuma wanan shirin da Yusuf yake son yi a kan shi.
Rigar shi ta sama ya jefar a saman gado ya kara bin dakin da kallo ya ja tsuki ya nufi yanyar bathroom din shi wani zarni ne ya daki hancin shi da sauri ya fito ya nufi hanya wajen dakin.
Dakin Nafisa ya shiga don yana kyautata zoton tana ciki tunda bai ganta falo ba kuma bai ganta a nan dakin shi ba.
Yana shiga nan ma wani tsami ya tare shi mai kama da karni karni yabi dakin da kallo ga kaya a ko ina watse a dakin tana kwance saman godon dake tule da kayan da bai san ko na maynene ba.
Nafisa na ganin shi tace ka dawo ashe yanzu nake tunanen ka fa a raina nace ko ina ka shiga tunda ka fita da safe baku dawo ba.
Haushine ya kamashi yadda take kwance ta mike kafa sai kadasu take yi tana magana kamar wata basaraka da ita.
Kallon da yake mata ne yasa ta tsargu yace Nafisa wai ke dadin may kike ji ga kazantar nan naki ne haka don Allah dubi dakin da mutun ke rayuwa wai a cikin sa.
Kina mace kice ba zaki iya gyaran muhalin ki ba sai wasu sunyi maki wai ma ina masu aikin da kikace kin dauka ban ga wani abinda suke a yi a gidan nan ba.
Tace Samad yan uwana ne fa ko kuma yanzu kana bakin ciki da zaman su ne a gidan ko suyi aiki ko kada suyi zasu dai zauna anan tare dani ne ko ?
Nasan wanan munufakin kila yaka su hadiye a falo ya zuga kwanan nan sai nayi maganin shi wallahi ni banga dalili da zai sa yayi ta shigo min gida ba haka ba gaira ba dalili yana sa muna ido.
Ke na fada maki duk abinda zakiyi idon ki ya fita ga Yusuf don idan kikace zakiyi kokarin raba ni dashi kan ki zakiyi wa kin dai san halina and kuma ki tashi kije ki pulloshing din rubish din da kikayi min a bandaki tunda ba dakin ki bane.
May nayi kuma kewayawa fa kawai nayi a ciki na fito yace zaki tashi ko sai na bata maki rai yanzu ya fadi yana dan zare mata idon shi.
Mikewa tayi da kyar tazo ta wuce shi zuwa dakin ya bita da harara ya mara mata baya yana sa kai warin bayin ya ji har cikin dakin da sauri yafita zuwa dakin hutun shi tare da rufo kofan da key don bai son damuwa.
Anan ya cire kayan shi ya yi wanka ya fito sallah ya gabatar ya dade zaune a wurin yana tunanen halin Nafisa ga gida da ta cika mai da yan uwanta babu halin ya zauna a tsararen falon shi ya sha iska a ciki.
Tsuki yaja ya mike don ya kwanta nan yaga wayan shi da ya jefar saman gadon daya shigo dakin kafin ya kewaya dauko wayan yayi yana duba lokacin maganan Yusuf ya fado mashi a rai.
Da yake ce mashi kabi yarinyar nan a sanun har mu cin ma manufar mu a kan hajiya ba wai nace kaso ta bane dole a a wanan wani dama ne da muka samu zamuyi amfani dashi.
Nomba na ya bida a wayan da ya rubuta ma tsoturburn girl ya danna kira sai ko kiran ya shiga tunanen ya fara yi idan na dauka may zai ce min sai yaji na dauki wayan da sallama a bakina.
Queen yar matsala yaya kika shiga gida yaya kuma ruwa i hope bai taba ki ba dai ?
Murmushi nayi sai da yaji shi cikin zuciyar shi nace au mijin buzuwa ne a layi lallai kana son aikin nan da zan maka ke nan ?
Yace to yaya na iya tunda Yusuf yace ke ce maganin matsalata yanzu indai har zaki min hakan ai ya zama dole in koyi zama dake da halin ki .
Nace ashe shiyasa na samu queen din yan matsala yace idan akwai abinda yafi queen din su kinci a baki wanan muka min.
Murmushi na sake yi nace nace nako gode da wanan sunan da aka rada min sai dai ina ganin bada ni sunan ya dace ba yanzu ai.
Da sauri yace dawa ya dace nace kaida buzuwar matarka mana fara yar dagwas mai gashi har baya sai dai kassh kuma gashin sai naga kamar bai samun gyaran da ya dace dashi balle har kaji dadin shakan shi dakyau.
Ke kada fa kiga na kiraki ki nemi tozarta min matata don kin san tafi komai da kike takama don wanan banzan dalilin na Yusuf da yakawo bashi ne zai sa ki samu daman fada min maganan banza ba.
Wanan kuma fadi kayi mijin buzuwa don yanzun haka ma nasan tunanen yar asaline ya hana ka shakat sai da ka kirani kaji yaya nake sai dai kana tsoron buzuwar ka nasan ma yanzu haka wani wuri ka samu ka labe kake wanan waya dani.
Idiout stupied girl kawai ya fada ya ja tsuki ya kashe wayan yana huci wai may yarinyar nan take takama dashi ne wai zuciyar shi tace kyau ilimi tsabta da fadin gaskiya.
Idon shi ya lumshe yana tunane sai kuma ya sake guntun murmshi a yadda yake rigingine a kwace taba kofan da Nafisa keyi yasa shi bude idon yana jin ta har ta soma bugun kofan bai tashi ya bude mata ba sai gyara kwanciyar shi yayi dakyau ya fara adduan barci haka har barcin ya dauke shi yana tunane.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUZaman da maryam yana min dadi sosai don itama bata da wasa da karatun ta gashi musan mutuncin junar mu kamar mun dade da haduwa da ita.
Ita ta tilasta min fara amfani da kayan da Yusuf ya saya min tace may ye amfanin ajesu da nakeyi gara dai a fara gani a jikina zai fi.
Ban sake bi takan su Yusuf din ba na mayar da hankalina ga abinda ya kawo ni garin sosai sai dai muna waya da kowanin su har yanzu wanda wayana da Samad duk ya kira fada ne da zolayan junan mu har ai fada a kai ga kashe wayan.
Munyi jerabawan karshen zango na farko inda muna gap da gamawa Yusuf ya kirani nake ce mai sati mai zuwa zan tafi minna don ba zan leka kaduna ba wanan hutun saboda hutun ba mai yawa bane .
Nan yake ce min suna tafe gurina kafin in wuce gida don suma zasu shiga kaduna don Samad ya dade bai je gida yana kokari yaga ya shawo kan shi su tafi.
Nace ka barni dashi in gwada in gani idan zamuyi sa, a da nawa dabaran yace ya gode muka kashe wayan suna zaune tare aiki suke a wani file.
Yusuf yayi mamakin jin ya tambaye shi khadija yace tana nan lafiya kasan jerabawa suke yi kwanan nan wayan shi ne yai kara baiyi saurin dubawa sai da ya gama abinda yake ya dago wayan.
Kallon Yusuf yayi da mamaki tare da fadin Yusuf yarinyar nan ko mutum ce jifa itace ke kirana yanzu muna maganan ta.
Yusuf ya kalle shi yace mutum ce mana kamar kowa kaima kana ranta kamar yadda take a ranka ke nan .
Ya dauka ciki daure fuska kafin in magana ya fara fadin lafiyan kirana ina aikina nace lafiyan ya kawo haka ai .
Ya sake kiran suna na a zuce da karfi yace matsala na amsa mai da cewa may ye ne haka zaka fasa min kunne da kira haka kamar makaho.
Kai na tsani wanan yarinya ya fada a hasale na amsa mai da nima haka wallahi cikin yanayin na bashi amsa.
Nace dama abinda yasa na kiraka don in fada ma ya kamata kaje gida ka duba tsofin ka don gudun su da kakeyi ba shine mafita ba gare ka.
Yace what da karfi don bai yi tsammanin jin wanan magana haka ba a baki na
Duk wani da mai neman albarkan iyayyen shi yana tare da su a kullun suna saka mai albarka da fatan gamawa da duniya lafiya don samun haske a gare shi.
Kai kana ganin kudi da girman kai da suke rudin ka zasu iya sama ma farin ciki haka ne a gare su, sunyi ciwo sun yi rashi amma bakai tunanen zuwa ka duba su ba har yau.
Who dear you are da zaki fada min abinda zanyi akan iyayyena, nace ni bakowa bace sai mai neman albarka iyayyena don haka kai ma na tunar da kai akan hakan.
Kuma kada ka manta da su Affan don sun fi kowa bukatan ka a wanan lokacin don nasan zaka iya zuwa masu hannu sake kai ba abin kunya bane a wurin ka.
Don haka oga aje a duba su kada a shagala da yawa wataran sune masu duba mu you are stupid kece zaki tunatar dani komai kike nufi wai ke wacece wai waya baki wanan right din da zaki min wanan magana haka.
Nace gani kamar kowa na tsoron fada maka gaskiya don suna ganin kana da kudi niko kudin ka ba damuna sukayi ba wallahi gaskiya komai dacin ta dole ne in fada ma mutum shi.
Amma gani nayi buzuwan ka kamar kanta kawai ta sani sai yan uwanta ai don haka nima dan uwa na na sani a yanzu.
Kit na kashe wayan ina dariyan keta shima Yusuf dake zaune yana jin yadda mukayi dashi sai murmushi yake yi yana huci yabi wayan da kallo.
You see abinda nake fada maka kenan gashi yarinyar nan har ta hango tunda kaji ta fadi haka akwai abinda taji ya faru a gida may be.
May yarinyar nan ta dauki kanta ne wai zanyi fa maganin ta a garin nan Yusuf da sauri Yusuf din yace kunfi kusa ai ni dan kallo ne a tsakanin ku sai dai ya kamata ka bincika idan ba wani taji bai da lafiya a gidan ba.
Tsaki yaja yana rufe file din da suke aiki akai alaman rashi ya baci sosai ya dafe kai da hannun shi daya tunane ya shiga yi yaya akayi yayi sake rainin da bai taba shiga tsakanin shi da kowa ba har shiga tsakanin mu haka wai abinda nake mai zakace ko mu din cousin ne.
Kan shi yana dafe da hannu shi daya Yusuf yace muci gaba mana yace kana iya tafiya yanzu makarasa next yanzu matsala ya shiga .
Dariya yayi yana mikewa yace matsalan khadija ke nan ko hararan shi yayi da idanuwan shi da sukai mashi ja shidai ya fice bai yi magana ba.
Ya dade zaune a gurin a karshe ya jawo wayan shi yana neman layin mommy don ita kadai ce zai tsaya yayi magana na fahinta da ita ya gane komay ke guda.
Kira biyu ta dauki wayan da sallama a bakin ta ya amsa mata tare da fadin mommy kowa na lafiya ko kwana biyu ban kira waya ba.
Tace lafiya kalau muke sai dai Alhaji ne jikin nasa ba dadi wallahi wanan matsalar tashi dai ta kwanaki ke damu shi kuma sai kuma Affan da suka kwanta asibiti amma dai yaji sauki sosai yanzu.
Wanan yarinyar takai shu,uma wallahi mommu tace wace yarinyar ke nan kuma yace da sauri No magana mukeyi a nan bayan ya gama waya da mommy sai ya kira hajiya mama.
Sun gaisa ta fara mai korafin rashin kula da kyautatawan da bai yi take mai fadan ga mahaifin shi nan ba lafiya yan uwan shi na kai da komo akan sa amma ace shi yayi biris dasu badon suraj da yazo ya kai shi asibiti ba may yake son mutane su fada a kan shi.
Hakkuri ya fara bata yana fadin in Allah ya yarda jumma,an nan mai zuwa zai shigo ya tabayi jikin Affan sai bata bashi amsa ba.
Bayan sun gama waya ya dade zaune a wurin kafin ya mike ya nufi hanyar fita office din ya rasa abinda ke yawan shagaltar dashi yanzu gamay da iyayyen shi haka.
Zuciyar shi ne tayi mashi zafi don haka ya nufi gidan shi dan ya dan sarara batare da ya sanar da kowa ba ya fice a ma,aikatar nasu sai gida.
Tun a kofa yake jin suruntun yana shiga Nafisa tana zaune a tsakiyan falon tana shan bakin shayi a dan karamin

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login