Showing 57001 words to 60000 words out of 142410 words

Chapter 20 - MIJIN BUZUWA COMPLETE

Start ads

08 Aug 2025

1020

Middle Ads

na gani nan dai na koro mata bayanin komai don ba zan iya boye mata ba ita.
Tace khadija kina nufin dama Abdulsamad ne ya yi maki wanan alherin ban sani ba khadija baki jin tsoron buzuwa ta san wanan labarin ta yi maki illar nace ya Amina yaya zanyi ni ban roke shi ba shiya bani.
Tace dama khadija kece kika saka yayi wanan alherin da yayiwa iyayyen shi ashe dama duk kece sanadi ni ba komai nake ji wa ba sai buzuwan matar nan tashi wallahi.
Takira daddy tayi mai bayanin komai yace shi zancen buzuwan matar shi bai damay su ba tunda ta sheda ba mugu bane.
Nema ne idan naga zan iya sai in yi dashi wanan ba komai bane Allah yasan abinda ya hada a tsakanin mu ya kawo hakan sai dai mu saka ido a kan yar mu don har yanzu khadija yarinyar ce karama.
Ya Amina tace gaskiya ne daddy zan shigo kafin ta koma dayardan Allah anan suka rufe maganan tare da taya ni addua ga wanan lamari tunda daddy yace abarwa Allah sanin shi a tsakanin mu.
Maryam ta kirani nake mata bayanin abinda ya faru dani maimakon ta tayani jimamay sai naji tana min dariyan shakiyancin da ta saba min tace shike nan ya nuna maki wayon manya ya gabatar da kan shi ke nan gare su.
Nace wai ke maryam don Allah may yasa kike irin haka ne sai a na maganan gaskiya sai ki dauko wani zance daban tace shike nan yanzu mubar zancen a haka dai.
Nace zai fi sauki muka dauko maganan karatu bayan mun gama wayan ne barci ya dauke ni a wurin wanda nasan barcin da ban samu bane a daren jiya.
Nan dai na kwashi barci na sosai a ranan sai wani lokaci na tashi don mama taki sake min fuska yasa ban son fita a tsakar gidan sam.
Wayana yayi kara na dauka Dan Baiwa nagani a rubuce wani haushin shine ya kamani a raina nayi banza da wayan nashi bandaga ba har kiran ya katse.
Ya sake kirana da kyat na iya daga wayan don har yanzu ina fama da ciwon mara dake cina jin murya na da yayi yasa shi saurin fadin.
May ya samay ki baki da lafiya ne may ke damun ki ne khadija haka yadda naga ya rude ne nace banda lafiya ne .
Tun yaushe nace tunda safe daddy na gida naji ya tambaya nace yana waje turo min da layin shi may zakayi da layin shi nace dashi.
Ban number shi nace maki ya fada a dake nace ban san number shi OK zan kira a bani number yar ki in karba a gurin ta yace da sauri nace a a din Allah ni dai kada ka kirata naji sauki.
Dole na bashi layin daddy din don naga yana niyar kashe wayan bayan na bashine ya kashe wayan bai fi minti goma ba sai ga daddy ya shigo gidan yana fadin ina khadijan take ne wai ashe bata da lafiya bamu sani ba.
Sai da wanan yaron ya kirani yanzu yake fada min khadija bata da lafiya a kaita asibiti wai zai turo da kudi kamar shine ya haife ta.
Mama tace ni tunda jiya da ta dawo na ganta kwance ban san may ke damun ta ba, har dakina daddy ya shigo ya samay ni kwance sai dai ba barci nake yi ba.
Zama yayi saman tsohowar kujeran dake falon yana fuskanta na yaga yar raman da nayi yace baby na may ke damun ki ne yanzu wanan mutumin ya kirani wai baki da lafiya.
Sai dai ban san ida ma yasamo lambata ba ya kira nace niyace in bashi na tura mai yanzu amma ban san kiranka zai yi bz ai daddy yace zai turo da kudi wai kije asibiti nace ya barshi bayan kudin da ya turo muna zai kara dawainiya kuma.
Daddy yayi murmushi yace kin san may yace dani na girgiza kai cewa yayi wai dawainiyar ki yanzu akan shi yake.
Nace daddy kada ka yarda da maganan shi wallahi ni ba komai a tsakanin mu yace naji sai dai yadda yake ya nuna min da fuskan gaskiya yazo maki don bai bar abin a tsakanin ku ba ku biyu ya sakomu mu iyayyen ki a ciki bai boye muna ba.
Yanzun dai yace a tura mashi da account number da zai turo kudi kije asibiti nace daddy nifa ba komai a tsakanin sai mutunci kawai yace yaji.
Sai ga daddy ya shigo zuwa sha biyu yana fadin ya turo dubu hamsin in tafi asibiti nace nasha magani naji sauki daddy dama ciwon mara ne kawai ke damu na.
Yanzu yaya kike son ayi da kudin da ya turo maki kasa kasa da murya nace kayi amfani dashi kawai daddy.
Sai yamma ya kira yana tambaya ko naje asibitin nace eh yace sun baki magani nace eh nasha har naji sauki sosai yace ashe period kike yi kike wanan raki haka ?
Shiru nayi banyi magana ba yace duk wata haka yake maki nace ban sani ba yace kan ki ga Yusuf ku gaisa.
Kunya naji sosai jin har da Yusuf yasan ina period yanzu muka gaisa yayi min yaya jiki nace da sauki yace ki sha magani kin ji sauki ko nace eh yayana .
Sai shiru ya biyo nace Yusuf batare da fadin yayan da na saba kiran shi dashi ba yayi makin jin hakan daga bakina sai ya dake yace yaya akayi yar mama ?
Nace kayiwa mutumin nan fada mijin buzuwa akan abinda yayi min bai kyauta min ba don may yake son saka iyayyena su zarge ni.
Yace zargi kuma khadija akan may nace yanzu haka tunda na dawo mama sai fushi take yi dani akan abin da ya saka a motar da naje gida dashi.
Saboda shi take fushi dake nace wallahi ni na rasa may zanyi akai suna ganin kamar ban kama kaina bane a Abuja ina hurda da mazan banza ne a can.
Sai daddy ne kawai daya fahinci komai da taimakon ya Amina na samu ya dan sausauta min bai fishi dani muryan shi naji yana fadin why mama zata yi fushi dake akan dan abinda na tura masu.
Mama bata yarda da tarbiyan da sukai maki bane ko may in haka ne kuwa zan shigo da kaina in mata magana da zata fahince ni ita ma.
Ban saka ba haka ka hadani dasu dazun daga na fada ma banda lafiya ka fadawa daddy yazo yana yi min fada balle maman mu da ta hau dani.
Ba matsalan ki bane nasan abinda zance da ita idan nazo nayi saurin fadin bansaka ba dai ka barni da ita zamu shirya wataran.
Bayan na kashe wayan na mike na shiga wanka na fito na canza kaya jikina zuwa dogon riga nayi kyau sosai a cikin rigar lokacin yamma yayi sosai nace zan je gidan su hafsat kawata da tai aure ta haihu bani gari.
Kallon da mamaki min ne yasani tsarguwa sai daga baya na fahinci rigar da na saka ajikina ne yasa take min wani kallo da bashi ba.
Sai na dawo tace min batare da ta kalle ni ba na fita jiki a sanyayye zuwa gidan hafsa din dake bayan minna minicipla coucil.
Hafsa kawa ta ce tare muka taso da ita kasancewar unguwar mu ba nisa da karatuna ya dawo minna na hadu da ita muna zuwa girl day dake a bayan old airport tare kusa da tsohon makarantar wtc na mata.
Bayan mun gama ta samu wani guy ta aura dan kabilar Nufe dake tashen kudi a lokacin .
Na fito gida a hankali nake takawa iskan marance yana kadawa inda nake ganin fuskokin wa yan da na sani muna gaisawa jefi jefi dasu a hanyan.
Har na isa gidan na samay ta tana girkin abincin dare tana gani na ta tare ni da murna muka gaisa ta nufi falon su dani ina biye a bayan ta.
Sai bayan na zauna ne ta dauko min baby ta har yaron ya fara wayo sosai ta miko min shi sai bina take da kallo wai na sauya gaba daya na zama wata big girl dake nace kai haba dai hafsat har dake cikin fadin haka.
Tace wallahi gaba daya kin sauya ma sani na ne khadija nace yanayi ne kawai wallahi yazo a haka ba wani abu may ye sunan yaron na tambaye shi.
Muna hira tana duba girkin da takeyi har ta karasa takawo min nace wallahi hafsat a koshe nazo gidan nan watarana zanci.
Mikewa nayi saboda magariba daya kawo jiki sosai na bata asai ma yaro takalma ina shirin fitane mijin ta ya shigo gidan.
Allah ya gani jini na bai hadu da mijin ta ba tun farko asali ma nice ya fara cewa yana so sanin shi da nayi dan duniya mai wayan yan mata da kyale kyali yasa ban bashi fuska ba.
Naje hutu kaduna kafin in dawo na samu sun dinke da hafsa har sukai aure yanzun ma da ya shigo gidan ya samay ni sai da ya daga min gira ba tare da sanin hafsa ba.
Harara na watsa mai na fice gidan tare da yi mata sallama nadan yi nisa naji muryan shi a baya na yana fadin khadija ji mana.
Juyowa nayi fuska a daure ina kallon shi nace lafiya dai ko ya washe baki yace don Allah sorry to distub you kin boye fa da yawa ban san kin zo garin ba ai dana kawo maki gaisuwa.
Dan murmushi nayi nace ba komai ai gashi mun gaisa yanzu dama boye nazo gani na ganshi har yayi wayo.
Yace in ba laifi ki bani layin ki akwai maganan da zamuyi kin san dai yanzu ba da bane zaki iya fahinta na har yanzu ba kin fita raina bane.
Auren hafsa Allah ya nufa sai munyi da ita amma ni ke ce choice dina tun farko hafsa dai ta shishige min har na aure ta.
Dakata Adam kada ka kara taro na da irin wanan maganan ko da hafsat bata gidan ka kai ba choice dina bane ka sani ban hurda da maza irin ku da kafan su bai tsayo a guri daya ba.
Ke kizo kici arziki kibar arziki kawai don yanzu arzikin bana yaci uban na da zan iya daukan lalurar ki da komai naki wallahi.
Wani kallo na watsa mai na up and down nace a haka din kake tunanen zan iya cin amanar kawata aminiya ta nace Allah ya tsare ni da masu irin halinka.
Na wuce na barshi tsaye a gurin yana bina da kallon zalama irin ta yan iskan maza yana sosa kan shi baida mu da mutanen dake wuce ba a saman titin.
Na shigo gida ana kiran sallah magariba dakina na nufa sai da mama ta gama alwala ta kwada min kira na fito inyi sallah lokacin sallah yayi.
Nace mama kin manta bana sallah ne ta ce oho ta shige dakin ta sai bayan sallah isha,i daddy ya dawo gidan suka zauna a dan falon mu har kanne na ciki suna kallon NTA dake labaran marance.
Daddy ya duba bai ga na shigo ba yake tambayan ina nake mama tace ina dakina kafin yace wani abu wayan shi ne yayi kara ya dauka bayan sun gaisa ne yayi mai magana yana son magana da mama ne daddy yasa handfree din wayan yadda zai ji abinda yake fadi.
Sun gaisa yace mama don Allah a dan sasauta ma khadija da takurawa tace na saka kuna zargin ta da aikata ba daidai ba ni kuma nasan idan har kun yarda da tarbiyan da kukai mata ba abinda zaisa ta canza daga baya kuma.
Mama kiyi hakkuri khadija na nan a yadda kika santa alheri kuma yanzu na fara maku kuda ita muddin ina raye sai abinda yafi karfina ne bazan maku ba.
Alherin yar ku gare ni ne ya jawo maku hakan ba ina nufin Khadija da wata manufa bane sai alheri don ta cancanci haka a gare ni so kuyi hakkuri a sake mata fuska babu komai sai alheri ga haduwana da khadija.
Bayan sun gama waya da mama ya gama daure ni a gaban su da ban gane manufar maganan shi ba daddy ya kwala min kira daga falon.
Da sauri na shigo dakin har lokacin shigan da na fita gidan hafsat ne a jikina ban cire ba na samay su a zaune falon.
Gaidasu na fara yi tare da samun wuri na zauna mama tace khadija yaushe ne kika canza haka wai ?
Nace cikin dago kai da mata kallon mamaki nace mama wanin abin nayi kuma again tace yanzu bamu da shakat a gidan nan dan abu kadan sai ki kai karan mu ga saurayin ki.
Da sauri nace mama wane saurayina kuma danakai karan ku gare shi tace wanda kika jajibo a Abuja mana wanda ya fimu sanin zafin ki a yanzu.
Mama ni ba saurayina bane wallahi ba wani abinda ya taba shiga tsakanin mu na soyayya har yau tace in babu yaya kika kai karana wurin shi wai na saki gaba a gidan nan tunda kika dawo.
Kai kai innalillahi haka yace maku mama fada nayi mai fa akan abinda yayi min nace kina zargina ga abinda kika gani ya bari ban so.
Daddy sai dariya yake muna ni da mama don yasan duk iya binciken shi bai gano wani abu da nake aikatawa a bayan su.
Tun daga wanan ranan mama bata kara daure min fuska ba muka koma daidai a gidan kamar yadda muke a baya.
Wayana gaba daya na kashe sai zan kira nake kunna wa don ban son wani abinda zai haifar min da matsala kuma tsakani na da iyayyena a gida.
Ya rage saura kwana biyar mu koma makaranta sai ga kamal mai bi mun ya shigo da kaya wai ya Amina ta shigo gari.
Da gudu na kwasa nayi waje ina masu sannu da zuwa tana sallaman driver da ya kawo ta gida na rungumay ta na sake ta naja hannun yaran na rungume su a jikina.
Ciki muka shiga gaba dayan mu bayan ya Amina ta huta taci abinci tana zaune a falo na shigo da karamin dan ta a hannu na tace dada hutu ya kusa karewa dai nace wallahi ya Amina.
Nakai zaune kusa da ita tace dama ina son in zo gida in samay ki kafin ki koma ne nace tau wani abin nayi ya Amina ?
May ye ma baki yi ba khadija ina ke ina Abdulsamad mijin buzuwa fati da mijin ta ta barshi dole don wanan buzuwa ke yanzu kike kokarin jefe kan ki ciki.
Kai ya Amina kuna bani mamaki wallahi wai ya fada maku muna soyayya dashi ne halan na san dai shi ba zai fada ba.
In kuma don wanan abinda yayi ne kuke zaton muna tare ne da bakin shi ya fada ma daddy gaskiya ba sona yake ba.
Haka kike tsamani ke ko azaton ki duk wanan alaman da yake gwada maki ba so bane hakan wani namiji zai samay ki yace bai so ki.
Kin fi buzuwa durin na ya mace sai dai fari da gashi zata gwada maki ko farin ma ba wani can ba don ke ma ba baya ba.
Sai yanzu nake gane maganan baban boy da yake cewa ke din matar manya ce watarana ina ganin kamar fadi dai yake yi.
Abin mamaki ne yadda har Abdulsamad ya fada tarkon ki abinda ba wanda ya taba tsammani zai iya sai gashi lokaci guda har kin fara canza shi da naki sallon soyayyan.
Mama da ta shigo dakin dauke da kwanon da ta tuka muna tawaska ta aje tana cewa ke ma dai kya fada idan anyi magana tace an matsa mata ba soyayya suke da shi ba ko takai karan guri shi.
Shi ko ba kunya gare shi ba ya kira mutane yana rokon su akan a daina matsa mata don Allah ni daddy ku har mamaki yake bani yarda ya yarda da mutumin nan a lokaci daya.
Da ban san halin shi ba sai ince ko don kudin shine yake son shi ya Amina tayi sauri cewa a a mama ba halin daddy bane haka da yana bin kudi da ba zan auri Abban su boy ba.
Mama tace nasani ai shine abin ke ban mamaki yanzu ai tace yarda ne kawai wallahi in badon buzuwar matar shi ba ai Abdulsamad mijin aure ne ga ko wace mace ta samay shi.
Nan ya Amina ta fara ba mama labarin shi da rayuwan su har karshe nace wai ku may yasa kuka damu da wata buzuwa can ne.
Kowa tashi tafishe shi amma ni bata cikin tsarina ni dai kawai bai min bane ina zan jefa kaina ga family man mai iyali da yawa haka.
Wanan duk ba matsala bane tunda yana da abin kula da koda mata nawa yayi niyar yi abin damuwa shine kishi da wanan buzuwan da bata da imani ko kadan.
Balle idan taji ba barin shi zatayi ya aure ki ba kuna tana iya yima rayuwan ki illar yada taiwa fati ko sunan ta baya son ji yanzu.
Allah

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login