Showing 72001 words to 75000 words out of 142410 words
da takan nuna nata ne.
Ita mommy Allah bai bata haihuwa da yawa a gidan ba daga Sadiq danta na fari sai salma kuma ba wasu manya bane sosai yanzu ma suke a secondary.
Yace mommy in sha Allahu za a gyara kwanan nan ma zaki tafi abuja wurin mu don Nafisa ta kusa haihuwa ke nake son kije tare da iya na zaria ku zauna a gidan.
Ba mommy ba har hajiya sai da tayi mamakin jin wai yau Abdul ne da kansa ke fadin wani nasa yaje gidan shi ya zauna don matar shi da zata haihu.
Kirikiri a baya tace bai yarda kowa nasa yaje gidan shi ba don suna zuwa suna tayar kashi da hankali a gidan shi haka Nafisa ta fada mai a baya.
Hajiyan su ce tace yar ikon naka tasan da haka kuwa yace haba hajiya sai ta san da hakan mahaifana da yan uwana zasu zo gidana.
Idan na gama shiri zan aiko a dauke su yanzu idan na shiga gurin Abba zan sanar dashi bukatan hakan don ba zan so ta haihu babu wani dan uwana a kusa ba.
Allah ya kaimu mommy tace da murnan ta fita daga dakin cikin farin cikin canjin da suka gani gareshi.
Wayan shine yayi kara ya mike yana amsawa ya bar Yusuf a gurin hajiyan Yusuf yace hajiya muna bukatar adduan ki kamar kulun yanzu haka akwai yarinyar da Abdul ya fara so ina ganin zata iya zama da Nafisa.
Duk wanan shiri nane don ba mace matsoraciya bane zata iya gwabzawa da halin nafisa ba don haka a tayamu da addua akan zancen in lokaci yayi nasan zakifi kowa farin ciki da zancen.
Hajiya tace ashe ba batun mayar da Fati kuke yi ba ku wani tashin hankalin kuke shiri daukowa yace hajiya wanan shi kadai ne nake ganin mafita ga alamarin.
Tace to shike nan addua dama kulun munayi Allah yasa hakan shine saukin abin amma dai wanan yarinyar ta cuta muna da yawa a rayuwan mu.
Babu komai hajiya komai ya kusa zuwa karshe insha Allahu Allah yasa tace ya mike tana mashi godiya ya fita ya samu Abdul din a waje suka wuce wurin alhajin shi.
Da sallama suka shiga dakin na Abba yana zaune saman kujera yana duba wayan shi ya dago kai yana amsa sallama tare da kallon su ta cikin farin glass din shi idon na medical.
Kasa suka zube suna mika gaisuwa ga Abban girma da kuma ciwo ya ramar da Abban don mutum ne mai jiki a da yanzu ko girma da ciwo yasa duk ya zube.
Sun gaisa sosai sabanin da da in yazo gaida Abban yake amsa mai a dadafe ba wani saki a fuskan shi.
Ya aje wayan tare da mayar da hankalin shi gare su magana yake irin na dattako yana tambayan su yaya aiki da iyali suka amsa da lafiya kalau Abba Alhamdullahi.
Kallon da yake masu ne yasa suka san da magana a bakin Abba din jikin Abdul yayi sanyi yana tunane a ran shi may kuma yayiwa Abba din yake mashi kallon tuhuma a yanzu.
Yasan dai ba wuce maganar yar aminin shi ba da yake ganin yayi mata ba daidai ba shi dai Fati taja mashi kiyayya a gun mahaifan shi yanzu komai yake masu baya fari a gare su.
Gyara zama yayi yana kallon Abba din don jin abinda zai fada masu Abba yace Yusuf zan iya cewa yanzu Alhamdullahi a yadda naga abokin ka yana waiwayan mu akai akai.
Ko ba a fada ba alama ya nuna cewa yanzu ya fara samun kwanciyar hankali a tare dashi shidai Abdulsamad ya zuba ido yaji karasan magana shi.
Abba yace ya na dade ina jiran wanan ranan tun ban mutu ba ranan da zaka gano gaskiya ka dawo a cikin hankalin ka irin haka.
Wanda nasan ba yin kan ka bane don ba haka muka tarbiyarta da kai ba da farko don haka nake son ka kara natsu ka tsayar da ibadan ka duk wani abinda zakayi kada ka manta da yawan addua a tare da kai don shine jagoran rayuwa ko ba haka ba ya tambaye su.
Lokaci guda suke kada ma Abban kai tare da fafin hakane Abba , murmushi Abban yayi masu yace to yanzu saura maganan iyalin ka zan so inga ka hada kan iyalin ka a wuri daya.
Kamar yadda ka taso ka gani a gidan nan kasan hakan shine cikar kamalan ko wani magidanci aga yana ba ko wace mace hakkin ta daidai gwargwado.
Suka ce hakane Abba, Abban ya dan tsura masu ido yayin da kanun su yake a kasa suna sauraren shi Abban yace kai kuma Yusuf na dawo gare ka mai kake jira har yanzu baka maye gurin matar ka da ta rasu ba shikenan kana nufin ba zaka sake aure ba a rayuwan ka ko may.
Yusuf din ya dago da sauri yana fafin ba haka bane Abba zan sake insha Allahu da zaran an gama na Abdulsamad dake tafe.
Au Abdul din aure zai karane kuma Abba ya tambaya sai Yusuf yayi kasa da kai yana fadin insha Allahu Abba basu gama daidaitawa bane da yarinyar shi yasa bamu gabatar maku ba tukun.
To madalla ka nuna ka gado gida ke nan to yaya maganan Fati kuma fa may ake ciki game da alamarin ta ?
Abba insha Allah zata koma daki ta ba da dadewan nan ba akwai abinda muke tsarawa a kai ne yanzu to Allah ya bada sa a sukace amin ya kara da fadin a kula da hakkin akai dai.
Insha Allahu suka fadi suna mikewa ta ciro kudin da ya ware na Abba ya nufe shi yana aje mai a gefen kujeran da yake zaune a sama.
Suna fita dakin Abba suka sallami mutanen gidan suka fice a gidan Abdul yace Yusuf yaya zakai min haka kace wa Abba wai aure zan kara kwanan nan ?
Idan ba haka na fada mai ba kana ganin iya abinda zai fada muna ke nan a yadda yake kallon mu din nan shine kawai mafita ai kai kasan ba auren zaka kara yanzu.
Bai yi magana ba ya bi bayan shi yana murmushi don yasan ya kulu dashi sosai da yamma motar kaya ya tsaya a kofan gidan Yusuf yasa akai ta shiga da kayan cikin gida.
Kowa na gidan sai farin ciki duk da zaman kishi dole na ciki na ciki a ransu ganin sauyin da yayi hakan bai hana a kebe gefe ai gulma ba tsakanin ummi da anty Amarya.
Nafisa da madam murnan tafiyan shi kaduna a satin sukayi don dama kafan zuwa ondo take nema don Abdulsamad ya hanata tafiya yanzu ko ina.
Tafiya sukayi sosai tun suna na dadin rai har ta fara galabaita ga tafiya don dan karan nisan da garin ke da tsakanin shi da Abuja.
Bata dauka nisan shi yakai haka ba sai da suka fara hanya duk wanan bakar wahalan bai sa ta janye kudirinta na zuwa wurin wanan bokan dataji ana yabon aikin sa ba.
Ko da suka isa ondo da safe wani motar suka kara bi zuwa kauyen da bokan bayaeraben yake zaune sun isa a wahalce don har amai da zazzabi sai da tayi a hanya.
Sun isa dajin mai kama da gari da baifi yan gidaje a kirga ba sai da suka huta kafin su samu ganin bokan don ranan suke son su koma Akure su shiga motan dare su koma abuja.
Bayan ta gama fadin abinda take son yai mata nan boka ya fara surukule shi ya dago yana kallon ta na dan lokaci.
Sai duk suka tsargu da irin kallon da yake masu wanda ke nuna akwai magana kai ya girgiza sanan yace aikin ta akwai dan wahala a cikin sa.
Don yanzu haka mijin ta yana tare da wata yarinya sai dai bai hango soyayya tsakanin su ba amma akwai aure har da haihuwa a ciki.
Kirjin ta ta doka tana fadin ta shiga uku ita samad zaiwa kishiya wacece zai aura har su haihu ?
Sam ta mace da Fati ma mallakin mijin ta ne har da diya shi boka Allah bai bashi ikon tsafin shi ya hasko ni ba nan tasa ai mata aikin da za a raba tsakanin shi da ko wacece .
Akuma fitar da ranshi ga ko wace mace a rayuwan shi sai ita kadai ya kara yin saddabarun shi na bokayen da suka gwane da tsafi yace ya ga wata mace sai dai baiga gaban ta sai bayan ta kamar tana son shiga rayuwar mijin ta amma dai bari ya mata aiki akan wace ta baiyana in yaso daga baya aikin da zaiyi zai gusar da waccan matar da yaga bayanta din.
Tace tana son koda kashewa ne a kashe mata wace aka gani ko a haukatata gaba daya kowa ya huta.
Yace an gama sai dai aikin ta na da tsada sosai tace kada yaji komai indai aikin zaiyi kyau nan ya shiga hada mata irin nashi surukulle da bayanun yadda zatai amfani dashi ba tare da kuskure ba.
Yace ba mijin ta ba wata mace da zai duba a duniya muddin tayi abinda ya fada mata daidai suka kama hanya komawa gida bayan ta cika shi da kudi.
Sam bata san Abdul kwana biyu zaiyi a kaduna ba lokacin da Abdul ya iso gida ya neme ta sai cewa sukayi ta tafi unguwane.
Har ya shiga ya huta ya dan kwanta bata dawo ba ran shi ne ya baci sosai da ita yaji yana son fita don haka ya shirya ya fito dan yasan kafin ya dawo ta dawo gida a lokacin.
Sai dai abinda ke bashi mamaki baifi ganin motocin shi duka dayayi ba a gidan yana tambayan kan shi da wace mota nafisa ta fita ?
Yana fita batare da sanin inda zai tafi ba har ya yanke shawaran zuwa wurin Yusuf sai ya fasa don ya san yanzu shima hutawa yake a gidan shi kada yaje ya damay shi.
Sai kawai ya yanke shawaran ya leka khadija don ya kwana biyu da ganin ta hanyar hostel din mu ya dauka sai da ya iso ya kira waya gashi abakin hostel.
Nace da yamman nan yace na koma ne nace gani fitowa yaja iska ya kashe wayan na fito ina tako dadaya wanda ni ban san inayi ba ma.
Na karaso wurin motar cikin yar murya na nace dashi sannu da zuwa baki maraba da zuwa na bane ko may ?
Murmushi nayi tare da fadin naga baka fita a wanan lokacin ne kawai har ina da lokacin fitane na daban da ban sani ba yace shigo mota mana.
Ina shiga sai kawai ya tayar da motar nace da sauri sata na zakayi ko may ?
Bai bani amsa ba yaci gaba da kallon titi may zan sata anan, nace mutum, dariya yayi yace kan nan naki kuwa zaiyi kudi sosai nace ai kafin ka sai da nawa ka fara sayar da na buzuwar ka ita bakuwar haure,
Kuff naji yake ma bakina dan bugu da sauri na dafe bakin nace saboda buzuwa ka dukar min baki ?
Yace ban san hadinki da wanan buzuwar ba nace halinta halinta bai mun bane don tana da ji da kai da son wullakanta mutane.
Ita abi kyama ba a kyamace ta ba sai itace zata kyamace mutane matar tawa ce abin kyama khadija ?
Ba ita duk buzaye abin kyama ne gare mu yan Nigeria sai iri kune dake mai dasu mutane kawai baku kyaman su don su din ba abin yarda bane mazan su da matan su.
Sai mutum ya yarda dasu daga baya su zo su yaudare shi yaudara a wurin su ba abin kunya bane don su din basu da kunya ko kadan.
Shiru yayi yana tunane a ran shi bai bani amsan magana na ba nace kuma gasu da son raba mutum da yan uwan shi su cika gida da nasu yan uwan.
Ga kazatar tsiya da son mamaye komai ya koma nasu su kadai koda kuwa sun samu wasu mata ne a gidan shiru nayi don na dauka bai saurare na a lokacin.
Sai naji yace uhmm go on yaya kikai shiru ba labari kike bani ba nace au na dauka baka sauraro na ai gasu da dan banzan bin malamai da bokaye basu yarda da kowa ba sai kan su suna iya yiwa yan uwan su yankar baya su zauna da mijin yar uwar su.
Zasu iya ketarowa da auren su suzo su auri wani anan alhalin duna da mazan da suka baro a gida sai lokaci lokaci suke lekasu.
Kai bazaye muggan mutane ne sosai wallahi duk wayon ka zasu san yadda suka juya ka indai na miji ne ji nayi ya tsayar da motar da karfi yace bari inyi sallah please sai kici gaba da bani labarin ki.
Fita yayi a motar ya nufi wani gu sai yanzu na duba naga ashe massalaci ne a wurin shiga yayi a ciki na mayar da kaina akan sit din motar ina kallon mutanen da ke gurin.
Ya dan jima a ciki ya fito ya shiga motar ya kama hanya mun dan taba tafiya ba tare da nasan ida zamu nufa ba.
Yace bissimila cigaba da labarin ki nace labarin yai ma dadi ke nan kwarai kuwa ina jin dadin labarin sosai nace toba zan kara fada ba.
Don may ko don kar naji halin buzaye nace ba wanda baka sani ba a cikin wanan kai da ke da ita a gida may ya rage da baka sani ba.
Ina ga saura bani kuddi baba ko a yaye ka kafa ka wayi gari ka samu ta ketara kasan su da dukiyar ka.
Yace da taci rabon ta ashe idan ta iya ketara kasa da dukiyana duka eh tunda a banza kake samun kudin yace haka kike zato ashe ?
Ni ba ragon namiji bane ko da yaushe ina tsaye da kafana wurin neman na kaina zaune a office din nace mai.
Au haka kike dauka na ni ko a gidana nake ina neman na kai na nace gun buzuwa ke nan kai ya girgiza min.
Koda yake dama abinda kuke nema a wurin su na daban ne da sauri ya juyo yace may muke nema a gun su nayi shiru tare da kawar da kai gefe.
Fada min may muke name muka aure su nace su mana tunda irin su ne ku din jara, , , , shiru nayi karasa mana ina jin ki.
Hannu yakai yana kamo min baki nayi saurin rike hannun nashi a karo na farko dana taba taba jikin shi da sauri na sake hannun nashi.
Na kawar da kai na gefe hannun nashi ya duba a hankali sai naga ya sauke murmushi a fuskan shi yace how lucky you're ?
Ke ce mace ta uku da na taba hada jiki da ita a duniya nace nima ina regreting din hakan da nayi wallahi.
Shiru mukayi yaci gaba da tuki wani guri ya shiga da motar mai yawan ginene gine da sasa da yawa yace kin san wanan gurin tsoro ne ya kama ni dana kalli gurin sai na dauka ko hotel ne.
Kai na girgiza alaman tsoro ya kamani sai naji yace nan ne ma,aikatar mu wanda daga MD din mu sai ni a gurin.
Da sauri na kalle shi yace ko kina bukatan shiga kiga gurin da sauri na girgiza kaina nace a,a don Allah ka mayar dani hostel inda ka dauko ni.
Ai bamu gama ba don baki ban amsata ba da sauri nace tamay yace irin mu da kika fara fadi baki karasa ba nace maganar yawuce ai.
Yace a gunki ya wuce ni a wurina bai wuce ba sai naji karasan maganan ki ko mu kwana a nan da sauri na dago ina kallon shi don Allah dai kayi hakkuri ka mayar dani inda ka dauko.
Maimakon yayi abinda na nace sai naga ya gyara set din motar ya kwantar dashi tare da sa hannayen shi yayi matashi dashi yakai kwance.
Muna wurin shiru ba wanda yai magana a cikin mu sai tsukin da nake ja can yace a kasalance kada ki kara jamin tsuki a mota yanzu na fitar dake na wuce.
Kayi hakkuri don Allah ka maidani hostel ina da exam next tomorrow ban son in fadi wani mutum ne ya dun faro inda muke yana haska toci a hannun shi.
Ni dake zaune nake iya ganin mitumin dake tafe nace ga wani nan yana zuwa gurin nan fa bai damu da abinda nace ba yana kwance abinshi yadda yake.
Har mutumin ya karaso ko ya sheda motar shine sai naga ya dan tsaya daga nesa damu yana fadin barka da dare yallabai an wuni lafiya cikin harshen turanci.
Ya dago yana amsa mashi da lafiya kawai sai mutumin ya juya ya koma ciki ban san na firgice ba sai bayan wucewan mutumin yace lafiya kika shige min a jiki haka ?
Ko kina son jin abinda buzuwa ke ji ne ajikina ta leke min da sauri nayi kokarin jaye jikina dana dan manna da nashi sai naji ya riko ni.
Ta yadda har