Showing 126001 words to 129000 words out of 142410 words
mamud din bari ki ji ki sani ba don ki ke kadai akayi shi ba daga yau ki gyara kalamin ki inzaki magana akan shi ki dinga cewa mijin mu.
Ina fadin haka ban tsaya jin haukanta ba na kashe wayan ina dariya nace banza mahaukaciya ni mijin ki bai a gaba na yanzu da kin ga tsiya wallahi.
Bai kirani ba nima ban kirashi ba sai bayan kwana biyu sai gashi ya aiko kirana wai ace mamud ne mace ace ban samun fitowa aiki nake yi.
Mamace ta samin baki dole na fita naci karo da dan aiken ya dawo wai yace don Allah inyi hakkuri minti biyu kawai zanyi.
Tare muka koma da dan sakon na samay shi zaune a cikin motar shi yana duban wayan shi karasowa na ya fito yana washe baki.
Fuska na a daure na gaida shi magana yake na kyale shi sai ko umm ko ummumm nake bashi amsa dashi kaina a kasa ina dakilan wayana.
Muryan shi naji yana fadin yau gimbiya may ya faru ne naga an fito min haka a daure nace wani abu ka gani halan ?
Yadan motsa kafan shi kadan yana murmushi tare da harde hannayen shi guri daya yace ko gimbiyar tawa mulki take jine haka ?
Sai da nayi mashi wani irin kallo shekeke nace mulki ai mulki yana gidan ka don ko wayan ka sai an baka izinin dauka kake dauka ko zuwa gurina yanzu waya sani ko santan hanya kayi kada matan ka su gani.
A cikin rashin kuzariya dago kai yana kallona yace wanan wani irin magana ne haka khadija kikeyi kai tsaye ba tare da tunane ba.
Nace irin wamda matar ka tayi min jiya daga kiran wayan ka ta dauka tana zagina a wayan ta daukar min waya fa kikace nace ka duba nan ga kirana a wayana kana gani katuna ina kaje jiya a daidai wanan lokacin ?
Look mamud na fada ma soyayya dakai a yanzu akwai matsala ka nace akan sai munyi gashi tin ba a je ko ina ba an fara kirana ana zagina daga gidan ka har da yimin iyaka dakai.
Ya kai duban shi gare ni tare da sake dan murmushi yace mai shi tayi nasara gare ki ke nan tunda gashi har kin karaya zaki bar mata ni.
Haka muka kasance dashi muna musayan maganan karshe dai yaban hakkuri nace ya wuce amma ya daina zuwa wurina.
Yace ba da sanin shi ba amaryan shi ce ta dauka daya shiga wanka kuma da ya fito bata nuna mashi akwai wani matsala ba.
Nace wanan kai ta shafa ni dai na gama magana kuma.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
SEENABUHutun mu yana karewa na fara shirin komawa makaranta bayan na kara sati daya a sama agida ina tare da iyayyena da yan uwa na.
Duk da ba so daukan kaya nake yi ba hakan bai hana mama ta dan tanadar min irin abubuwan da uwayen mu mata suke tanadarwa yaro idan zai koma karanta.
Inda mahaifina ya bani kudin da zanyi sayayya na raba kudi biyu na mayar mai da rabi nace ina da kayan abinci da ban ci ba a daki na.
Bayan na shirya ina shirin zuwa Abdulsalam garage da kayana inda zan shiga motar zuwa abuja na fito a cikin shiri na yan uwana suna a bayana zasuyi min rakiya bakin titi.
Gaban daddy da mama nazo na durkusa har kasa ina fadin daddy zan tafi ya dago kai ya kalle ni tare da fadin khadija kin fito ke nan.
Yace do Allah khadija ki kula da kanki kamar yadda kika saba a baya ki maida hankali ga karatun ki kinga lokaci na tafiya yanzu.
Kaina na kasa nace in sha Allahu daddy na gode mama tace banda kai kai inda Allah bai kaika ba kawar da kanki ga komai sai kiga komai yazo maki a cikin sauki nace na gode mama na mike tsaye jiki a sanyaye.
Ban dade ba na samu mota naba kanne na kudi su raba daga cikin wanda daddy ya bani in rika din muka tafi tare da kanina dake bin min.
Na isa Abuja da wuri inda na samu maryam ta rigani dawowa lokacin ranan mun jima tare muna hira ko barci bamuyi da wuri ba dan shaukin juna da mukeyi duk da muna waya kusan kullun da ita.
Dayake muna da abinci ga kuma wanda maryanm ta karo don haka ban damu da nashiga gari in sayo komai ba don akwai shi a dakin.
Mun samu sabbi fuska a gidan namu don an dauki sabbin dalibai yanzu wasu sun tafi kuma koda zan dawo ban bari mamud ya sani ba .
Idan ya tambayeni yaushe zaki koma nakan ce dashi ba yanzu ba idan na tashi zan sanar da kai lokacin da ya samu labarin na koma school ranshi ya baci sosai dani.
Kirana yayi ga waya yana fada wai ya fahinci gaba daya yanzu ban damu dashi ba don may zan koma school ban sanar dashi ba saida yazo gidan mu ya samu labarin na tafi.
Nace dashi na fada maka tun farko kada ka wahal da kanka gare ni don ba auren ka zanyi ba na riga na rufe babin nan ko a raina.
Satina biyu da dawowa sai ga mamud din ya kawo min ziyara gaskiya banji dadin zuwan shi ba don na gane yana son da karfi da yaji ya shiga raina again.
Yadan jima a guri na muna hira dashi wanda hiran duk a kan zaman mu dashi ne anan maryam da wata Aisha da yanzu muke tare da ita suka samay mu.
Da zasu tafi ya basu alheri sukayi mai godiya yace ma maryam ta taya shi kanfen a guri na dariya tayi tace ban maka wanan alkawarin ba don abaya ka gujemu ba wani dalilin komai.
Haba maryam banyi zaton jin haka a gare ki ba yace tace gaskiya na fada don yanzu tace karatun tane a gaban ta doon kaga muna gab da gamawa ba wasa a gare mu.
Kaya masu yawa yazo min dashi irin na bukatan yan makaranta na nuna mashi hakan da yake yi ba daidai bane yace yace bai son irin kalamin nan da nake mashi.
Bayan tafiyan shi ne muka bude kayan da yazo min dasu muna kallo Aisha tace amma ni kan sai naga kun dace dashi very handsome dashi wallahi.
Nace Aisha ba handsome bane abin damuwa abinda ke cikin gidan mamud din ne ai maryam tace da ita ai khadija haka take samun handsome guys don baki ga AA bane har kike ganin mamud a matsayin handsome a gare ta.
Nafitar da zancen wani mamud da AA a raina karatuna kawai nake fuskanta a yanzu da ya dau zafi gare mu banda lokacin kowa a tare dani ban kuma shiga gari ko yaushe ina cikin makaranta ko hostel din mu.
Zaune yake a office din shi yana aiki a wani file aka turo kofan office din nashi aka shigo baidago ya kalli wanda ya shigo din ba don yasan daga Yusuf ne sai ko masinjan office din nashi.
Muryan da yaji yana mashi sallama ne yasa ya dago a lokacin wani hamshakin Alhaji ne ya shigo office din tare da wata mata a bayan shi.
Yana ganin su ya kara daure fuskan shi tare da amsa masu sallaman su wuri suka samu suka zauna tare da fara gaida shi hakan yasa ya aje aikin da yake a lokacin yana fuskatar su.
Bayan sun gama gaisawa ne mutumin ya fara magana da cewa yau ma gamu mun dawo gare ka bayan wahalan da mukasha kafin mu iso gare ka.
Cikin daga hannu ya dakatar da mutumin ga maganan da ya fara yace Alhaji na fada ma wanan business din ba zai yuyu ba tun farko.
Ba haka muke sake fili ga mutanen da basu san darahan shi ba suna gina abinda suka ga dama a cikin gari.
Mutumin yace ba zancen gina wancen company a yanzu gare mu ni buri na kawai a yanzu shi ne in mallaki filin nan isan yana a matsayin nawa ne.
Zan baka ko nawa kake bukata muddin zaka yarda ka saka min hannu in malaki daga milayan daya har zuwa hamsin zan baka idan kana so don wallahi ina , , , , ,
Table di gaban shi ya buga tare da mikewa tsaye yace na fada maka tun farko ba haka nake aikina ba kada kayi tsamanin da cin hanci ire iren ku na dogara.
Ina da abinda zanyi a wuni daya million dari ya shigo min a accout dina ba tare da nasha wani wahala ba nafison in ci halan dina da na tsaya amsan cin hancin ire iren mutane irin ku.
Matar ne ra katse shi da cewa ba wai cin hanci muka kawo maka ba kanina ka sani gogi bai ki kari ba balle mutum mai lalura da jama, a irin ki ko yaushe.
Ina son ki sani wani gogin ne ke son kari wani ko an zuba mai wani ruwan aman shi yake yi don ba wurin zaman shi yazo ba.
Don haka na roke ki ku fita min office yanzu ina da abubuwan yi a gabana da yawa da zanyi kada ku bata min lokaci.
Matar zatai magana don ranta ya gama baci a lokacin mutumin ya daga mata hannu yace barshi mu tafi Allah ya bashi hakkuri bata mai rai da muka.
Ya mike yana fadin mun barka lafiya sai dai ka sanin haka ba zai sani fushi dakai ba don abinda nake so nake nema a gare ka.
Kuma ka sani ni ma ba irin mutanen ne da kake zargin suna sayen filin gwanati su gina abinda bai dace ba dashi nima kamar yadda zuciyar ka yake fari a kan kasan ka haka nawa zuciyar yake fes ga komai.
Do haka mun barka lafiya matar tace bai kamata kana saurin yanke hukunci haka ba akan abinda bakai bincike akan shi ba.
Binsu yayi da kallo har suka fice a office din nashi wani iri tsuki yaja tare da dafe kan shi da hannu shi daya yana fadin wai may mutane yanzu suke daukan kan su ne ?
Yana jan tsuki tare da bude file din gaban shi yana gyara zaman shi da kyau Yusuf ne ya turo kofan ya shigo da sallama ciki.
Tun daga nesa yake kallon yanayi abokin nashi yace may kuma akayi naga yanzu yanzu ka sauya gaba daya mana ?
Bai yi magana ba sai duban files din yaci gaba dayi wuri Yusuf din ya samu ya zauna yana fuskanta abokin nashi tare da kara maimaita tambayan shi gare shi.
Yace wanan mutumin mai bakin nacin tsiya akan sai ta mallaki filin da yake so mu bashi ne ya sake zuwa yanzu tare da wata mace dake son karanto min hauka.
Wai har ni zasuce zasu iya ba daga million daya zuwa dari don dun mai dani mubukaci ban san ciwon kaina ba ko may ?
No ba haka bane wasu ne ke bata wasu ga alumma shiyasa suke daukan haka ga kowa idan da sun san ko kai waye da ba zai tunkare ka da wanan zancen ba.
Kai din ne ka faye boyon kurwa ga jamma, a kaki fitar da kan ka fili mutane sunan kokai waye may zai hana irin mutanen bazasu dinga tunkaran ka da suna baka ci hanci ba ko yaushe.
Murmushi ya sake a fuskan shi yace dole ne sai na fito na nuna ma duniya ko ni waye san nan zasu sani kana ganin ko a gidana da matsalar Nafisa kawai bai isheni ba yanzu.
Ni ba wanan ba ma gida nake son ka sama mun mai dakuna da yawa inda zan sai wa yan uwata su koma nagaji da zaman da suke min a gida na wallahi.
Mutum da gidan shi baida halin ya huta yaji dadin gidan nashi sai a hana shi shaka wanan abin yana damun raina sosai wallahi.
Ya zakayi abinne sai hakkuri tunda yan uwar matakar ce kaga ko don yar uwasu zasu zo gidan da son ka ko ba da son ka ba.
Iska ya furzo daga bakin shi tare da ci gaba da aikin shi yayin da Yusuf yake dan tunane a zaune a gaban shi.
Can ya dago kai yace ina ganin fa hutun su khadija ya kare don haka nake ganin tana garin nan duk yadda akayi yanzu ta dawo school din.
Ummm nima abinda nake tunane ke nan do hutun su ya kare ai ita ba zata iya neman mutane a ida take ba tana jira a nemay ta ko ?
A, a kaiko yaya zata nemay ka kafa san halin mata da jan ajin su ko yaushe aji kawai take ja muna ita ma a matsayin ta na mace.
Ashe ko zata tsunke idan nine ya fadi ba tare da ya dago kanshi ba ya kalli Yusuf din dariya Yusuf yayi yace idan bata tsunke ba kai ai zaka tsuke din.
Nayi mamaki da tunda muka dawo ka daina maganan khadijan amma acan kusan kullun kana min zancen ta har ina jin dadin ta shiga ranka yanzu ashe abin ba haka yake ba a gurin ka ban sani ba ?
Au so kake banda aikin yi sai na ta yanzu kai ni fa tunda yanzu muna lafiya da Nafisa wani batun karama kaina wahala ya kawu min a zuciya.
Ban gane may kake nufi ba yace Yusuf amma dai kaga aiki nakeyi ko yana mikewa yake fadin nagani barin baka wuri ka taba aikin ka.
Har ya mike yake fadin ina son ka turawa Fati kudin da ta bukata na bukin da suke dashi don jiya take fada min bukin ya gabato.
Kallon shi Yusuf yayi yace baka fada min nawa zan tura mata ba and kuma ina ganin ya dace ka tura ma da wanda zasuyi suturan fita bukin dashi.
Katura mata biyar dakomai da komai don saboda laluran yara idan zai ishesu dariya Yusuf yayi yace indai fati ne ko bai isa ba baka jin korafin ta akai shiya nake ganin zubin su daya da khadija wallahi a wani gu.
Baiyi magana ba sai murmushin da yayi a baiyane tare da fadin yar matsala wai ita a dole fushi take ba a kulata ba.
Mata idan suka samu guri sai so wuce limit din su akai ni dake da mata biyu wata mace zata tsaya jawa rai a waje yanzu ?
Fita Yusuf yayi yana mashi dariya tare da fadin ni dai nasan yanzu akwai nadi a lauje muje zuwa dai a hakan .
Kwance nake a dakina ina so in huta don yau a gajiye nake ga test ga pratical da muka fita da rana maryam ce ta shigo dakin tana fadin malama tashi zakiyi fa mu fita.
Don har kayan miya nake son mu sayo kin ce kuma kina son kayan make-up ke ma da sauran abubuwan bukatan ki.
Wani kallo nayi mata nace cabdi jam a yanzu yadda nake din nan don Allah ki tafi ki dawo yau na gaji wallahi sosai maryam.
Ke ma kin san dole zaki tashi mu tafi don yau kadai kike free kara kwantawa nayi na fita batun ta tana ta shirin ta har na fara barci sai naji takai min doka a baya.
A zabure na mike tana fadin don Allah tashi muje khadija kada ki bata muna lokaci mana nace maryam ba zaki barni in huta ba don Allah wallahi na gaji ne yau.
Matsa min tayi dole na mike na fara shiri ba don naso ba dogon riga na saka kaman kullun don sune kayana ko atamfa zan dinka nafi inyi dogon riga dashi yanzu nafi sakewa a cikin shi.
Mun fito maikon mu tsaye kusa sai da ta jamu zuwa ciki gari a shagon da take ganin zamu samu kaya da sauki a gurin.
Raina na bata ina fadin ni ban iya wahalan ki wallahi shiyasa nace kizo ke daya don ban iya wanan wahala saboda son banza zaki jawo mu zuwa nan.
Dariya take min tace kin dai riga da kin fito yanzu sai yadda nayi dake kuma ai shagon babbane so sai kaya iri iri ne a cikin sa .
Binta nake a baya kamar dole banko iya magana don gajiyan da nake ji din ta sai wanan ta dauki wancan.
Wani set din kaya make-up na gani mai kyau na mika hannu zan dauka naga hannun wata mace ta mika itama zata dauka.
Duk tare da ita muka dauka a lokaci guda na juyo ina kallon ta Nafisa ce a baya na ta ke daukan set din ita ma nace cikin wani irin murya sake don na rigaki dauka.
Nawa gare ki da zaki biya wanan make up din halan ta na shirin bangajeni ta dauka na riga ta rike kit diin nace don Allah ban wuri malama.
Baki isa ba mara kunyar banza nace marasa kunya din ke wacece da zan dauki abu kice wai na bar maki kamshin turaren shine naji a hancina yana fadin may ke faruwa ne Nafisa ke da waye