Showing 63001 words to 66000 words out of 142410 words

Chapter 22 - MIJIN BUZUWA COMPLETE

Start ads

08 Aug 2025

35

Middle Ads

ciki da nafisa a gidan shi.
Da yan uwanta da suka cika maigida da sunan yan aiki ta kwaso yana biyan su a wata ashe ba haka abin yake ba.
Kai inji Yusuf lamarin Nafisa akwai daure kai wallahi Abdul yace nima bashi ba kazantar nan ke damuna Yusuf.
Ka san dai halina da kyakyami wallahi komai na gidan nan yanzu kazantar shi nake ji in ba ruwan gora ba ban iya cin komai a gida na .
Yusuf yaya zanyi da wanan masifa dana dauko ma kaina nasan ina son nafisa sosai why da ba zata gyara halin ta ba may ye ban ma Nafisa a rayuwan ta.
Kamar karta samu cikin nan yanzu abin ya karkare jagule mata mace ba wanka ba saka sutura a jiki idan anyi magana sai tace wai lalurar cikine haka take cikin ta.
Au dama ta taba ciki ke nan naga auren budurwa mukai mata wani kallo ya jefe shi dashi yace Nenan yar waye idan bata taba haihuwa ba nima daga bayan nan na fahinci yar tace ashe.
Yanzun haka zan kare ga yawon restaurant ina cin abinci a garin nan kamar wani mara galihu dani.
Kai innalillahi abin nakune akwai daure kai wallahi saukin abin khadija zata dawo next week zaka dan samu sauki a awurin ta.
Saukin may zan samu a gurin ta ya tambayi Yusuf a yanayin rashin fahintar maganan shi Yusuf yace koba komai tunda ta iya girki naga ai zata dan dinga maka idan tana da time.
No ban san in jefa rayuwan yarinyar ga halaka ko kadan nafi son ayi komai a kaidance yace kana nufin auren ta zakayi.
Shiru yayi ya dafe kanshi bai sake magana ba ya fahinci bai son maganan don haka ya kyale shi tare da canza topic.
Yusuf na fita ya jawo wayan shi ya kira layina muna gida ya Hauwa mai jego ya kira wayana ina wanke kayan miya a kitchen aka kawo min wayan.
Sai da ya kusa katsewa na dauka tare da sallama yace ina kika shiga kika bar waya na ruri haka nace ina kitchen ina girki wa ya hauwa da ta haihu.
Kuna gidan ta ke nan ya tambaya nace eh may kike girka mata nace miyar shuwaka zanyi mata da tuwon shikafa.
Ke wa ya koya maki girki haka ne wai nace girkin ma har sai an koya ma mutum yin shi idai kana mace ai zaka iya girki ko wani iri dole.
Aranshi yace ga macen da ta san kanta ba sai kuma yace ke wace irin yarinyace da baki iya kiran mutane kiji ko sun sauka lafiya ?
Na aiku tafiyan dare ne ko ni na saka ku yin tafiyan da kuyi din yace OK haka zaki ce ma nace haka din ne ma ai.
Sai naji ya kashe wayan dariya nayi nace zaka kaji ai ka daina in yar da magoro in huta da kuda har dare muna gidan sai tara muka dawo gida a gajiye .
Ban kara bi ta kanshi ba har akai bukin suna aka watse lafiya drinks din da suka kawo muna yayi muna rana do shi mukai amfani dashi wurin taron sunan.
Mun fara shiri don tare da yaAmina zamuyi tafiyan kamar yadda na fada mata yace zai turo mota hakan ne ya faru sai ga mota zuwa sha biyun rana ya tsaya a kofan gidan mu.
Nan muka fito mukayi haraman tafiya nasha nashi ha a wurin mama da daddy 6 kafin mu wuce muka dauki hanyar Abuja tare da ita don zata kwana a wurin mu.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU


INA BUKATAN ADDUAN KU YAN UWA ALLAH YASA MU DACEAlhamdullahi mun sauka lafiya inda na samu maryam ta dawo ko saboda kwanakin da na kara ta rigani shigowa na samu har ta gyara min daki ko.
Anan driver ya zube mu ya wuce abinshi ko ba a fada min ba nasan anty ta biyoni ne don taga yanayin zaman da nake a Abuja inda tazo da sunan kwana daya sai gashi ta share biyu kuma muna tare da ita ban je ko ina ba.
Washe gari da safe na rakasu tasha suka shiga motar kaduna suka tafi bayan yan nasihohin da taimin na in kula da kaina in maida hankali ga abinda ya kawo ni.
Muka rakata garage ta shiga motan kaduna wanda ta dauka ita kadai sai yaranta har kaduna mun dawo hotel a gajiye don haka na kwanta barci don nadan ji dama jikina.
Tun da na kwanta ban tashi ba sai bayan sallah la,asar na tashi nayi wanka na tare da gabatar da sallolina ban dade ba maryam ta shigo tana fadin kin tashi ?
Nace wallahi tace ga abinci nan ki cikin kula idan kin tashi ci ni na koshi sauran kayan bukin da ya rage na zauna ina ci nace abinci sai da dare.
Ina zaune kamar daga sama zara ta shigo dakin nace mutumiyar ashe ke ma kin dawo ke nan tace dazu fa na gama tunanen ki.
Zarah tayi dariya tace ai ni na riga ku dawowa tun wancan satin daya wuce na dawo school da sauri nace ai lokacin ba ai resuming ba.
Ta wallahi gajiya nayi da zaman gidan shine nace hutumu ya kare aka shiryani na dawo school kaina jinjina nace Allah ya kyauta da halinki zarah tunda har kin san ki aikata haka.
Dariya ta sake min tana fadin gidan ne babu dadi yanzu da na saba da ruyuwan independent din kaina .
Sai da taci abinci a dakin ta koshi tana bani labarin tafiya sukayi da saurayin ta ta raka shi kano shiyasa ban ganta ba maryam baya ta bamu tana diban takardun da take hadawa har zarah tabar dakin.
Sai lokacin ta juyo take ce min irin wa yan nan bai kamata mutum yana hurda dasu ba ai kada su bata ma mutum suna a banza.
Nace yaya zanyi mun fito gari guda da ita bazan iya kyale ta ba ai kin ji dai ina bata shawara ko zata daina halin nan da tasawa kanta.
Allah ya kyauta tace muka canza hiran kada muci namanta bamu sake fita ba har gari ya waye muka shiga school.

Wanan karon Nafisa bata yar da ba dakanta ta shirya tafiya zuwa kaduna bayan ta dawo Niger don an bata labarin wani sabon malami a Kusfa.
Abdulsamad bai hanata zuwa ba don tace kaduna zata leka don ta kwana biyu da zuwa shiri sosai yayi mata don zuwa kadunan a ganin shi ai gida zata.
Ranan da ta isa kaduna bata samu zuwa ko ina ba sai washegari suka tafi ita da Auta yar take ga su Abdul din sai dai halin kwadai irin nata zata iyayin komai akan kudi.
Haka yasa suka kule sosai da Nafisa har aminci ya shiga tsakanin su tana mata shige shige dama Auta irin yan duniyan matan nan ne tunda ta fito gidan mijin ta bata sake aure ba tana zaman rayuwa kawai a gida.
Su biyu sukai tafiyan sai driver daya kaisu bayan sun gama yi ma malamin bayanin komai ne malamin yayi dariya yace kamar yadda take zargi gaskiyan maganan ke nan ya fada tarkon son wata yarinya a yanzu sai dai abin bai wani yi nisa sosai ba.
Idan kuma bata bi alamarin a hankali ba zafin kishin da take nunawa ne zai sa komai ya iya faruwa da ita.
Hakalin ta ya tashi sosai wanan ne mutum na biyu daya fada mata haka malamin yace alamarin yarinyar yana da karfi sosai.
Don asiri baya kamata kai tsaye da zaran zamcen yakai ga iyayyen shi komai zai iya faruwa a tsakanin su a yadda bata zata ba.
Don haka sai kin natsu aiki zamuyi maki wanda zaki kama mijin ki a hannun ki indan shi ya kamu yadda muke so komai zai iya zo maki da sauki.
Amma koda zakici nasara akan hakan sai kin bi a sannu don yarinyar tafiki komai da kike tunanen kina dashi abune wanda sai an aiwatar dashi a sannu saboda mijin ki yana mata mugun son da bai san yana mata ba.
Nashiga uku tace malam tafini komai fa kace yace kwarai da gaske don gata nan a gaban mu kina gani ta shige maki gaba ko a wurin shi.
Kuka ta fara tana fadin don Allah malam kai min rai ka taimake ni ko nawane zan iya baka indai zaka min aikin da za a raba su hayatan hayatan ya ji bai kaunar ta ko kadan.
Gaba daya yanzu na daina gane kan shi ada komai yana min kai tsaye yanzu sai yaja min rai yake min abu da na dauka ko cikin dake gare ni ne yasa yake min hakan.
Yace magana dai guda ce ga yarinyar nan kina gani taurarin ta na da matukar haske sosai duk abinda ta sama gaba takan cin ma nasara a kan shi lokaci daya.
Yana nuna masu zanen da yayi a kasa wanda su basu fahintar abinda ya zana sai dai bayanin da yake masu wanda ke matukar tayar wa Nafisa da hankali.
Yace saukin abin daya ne yarinyar mijin ki baya gabanta don wani dalili nata amma shi yana kokarin cusa kanshi ko yaushe a wurin ta ne.
Tace da karfi shi samad din malam yace kwarai kuwa muddin muka ce zamuyi aiki na gagawa komai zai iya faruwa na fada maki.
Idan baki yarda ba zaki iya zuwa gurin wani kiji nasan duk wanda zai fada maki tsakani da Allah ba zai fada maki sabanin abinda na fada maki ba.
Tana share hawayen dake zubo mata take fadin malam yanzu may ye abin yi don ko yanzu da dabara na samu nazo nan din.
Wanan ba wani matsala bane aiki zamuyi mashi wanda hankalin shi zai fita a kan wata mace baki daya sai mu cus mashi kaunar ki ke kadai.
Ta gyara zama tana fadin in hakan zai samu malam shi nafi bukatan ai min a kan shi a raba shi da ko wace yar iska ce kison tayi min kutse a gidana.
Ya zayyana masu aikin da zai masu din ta yarda ta amince zata biya makam din abinda ya bukata a wurin ta suka biya shi ba tare da taji komai ba sukai mashi sallama.
Tun a mota take zazaga balai tana zaginshi da iyayyen shi Auta tana kara zugata da fadin wanan wata irin yarinyar ce da za a ce ta fiki komai har kyau ke nan malam yake nufi ko may.
Don banda kyau babu wani abu da Nafisa ke kadagi dashi don ba arabi ba boko haka take dip dinta bakauya kuma.
Koda ta dawo kaduna bata biya gidan su Abdul din ba bata mayi tunanen shiga gurin su ba don daukan su take a makiyan ta dama balle yanzu da sunan su ya fito ga zancen.
Kwanata uku a kaduna bayan Auta ta koma ta koma ta karbo abinda zasuyi amfani dashi idan ta koma sauran sai ya hada yace zai kira Auta ta karban mata don sai ya nemi abin hadi.
Haka ta shirya sai da zata wuce ne ta dan shiga tsatsaye ta gaida su hajiyan shi da sauran mutanen gidan ta juya suka tafi.

Almarina kuwa tunda na dawo sau daya muka hadu dashi koshi a tsatsaye don ina sauri zan tafi class karatu don muna da test din da zamuyi washe gari.
Yazo min da provition mai yawa kamar ba gobe har sai danace kayan suyi min yawa yace naci da kawayena.
Sun tafi abisa alkawrin zamuyi waya amma har wani lokaci bai kirani ba Yusuf ma haka bai kira ba nikan haka yafi min nono fari.
Don dama neman mafita nake dashi kuma na samu yanzu sun sarara min ranan muna hira da maryam take tambaya na su.
Nace banji komai daga gare su ba na nuna mata ni basu gabana yanzu abinda ya kawo ni nakeyi.
Tace kai amna abin mamaki ne khadija ace sun share ki haka ba labarin komai daga wurin su ko yusuf ai ya kamata ace ya kira musan halin da suke ciki.
Ke kuma baki neme su ba halarci baice haka ba fa khadija shiru nayi mata don mu kawar da zancen su da ta dauko min ina zaune kalau.
Sai bayan da na kwanta sai kuma maganan ya damay ni a rai gaskiya maryam ta fada min ya kamata ka kula mai kula ka koba komai zai san ka damu dashi ai.
Ranan da kyat na samu nayi barci da tunanen su a raina sai dai ni ba zan iya kiran shi ba sai dai dan dama dama Yusuf din.
Washe gari haka na tashi da jin bakin rai a zuciyata sai dai kawai na danne abin a raina don na kudurta a raina ba zan taba kiranshi ba indai nice zakira inji ko lafiya suke.
Tunda dama ba wani soyayya ko wani abu ke tsakanin mu haka ba mai karfi kawai dai ya gaji danine shima ya hutar da kan shi.
Na share kawai kada maryam ta fahince ni na shirya muka nufi cikin school don daukan lectures na watsar da maganan su a raina kada in sa wa kaina damuwa a banza.
Alamarin gidan shi kuwa yanzu tun dawowan Nafisa daga kaduna sallon zaman su ya sauya don yana dan samun kulan daya kamata daga gareta duk da ba wani dadin yake ji ga hakan ba don baya samun sakewa har yanzu a gidan shi yadda yake so.
Shima Abdulsamad din ina a ranshi yakan so ya kirani yaji lafiyata sai dai yanzu duk lokacin shi na aiki ne dana Nafisa a haka har yayi tafiya tare suka ketara da nafisa zuwa wanan tafiyan.
Satin su biyu suka dawo Nigeria koda suka dawo abuja bai samu kafan kiran na ba don Nafisa ta mamaye komai a lokacin.
Yau suna tare da Yusuf a office din shi Yusuf ma wanda yayi tafiya yake tambayan shi labarina ya yamutsa fuska yana fadin wallahi banda labarin ta itama bata neme ni ba.
Yusuf yace haba kai ma kasan bazata nemay ka ai, amma hakan bai mun dadi ba wallahi dakace baka kirata ba waya ya dauko daga Aljihun shi ya fara neman layina a lokacin.
Ban shiga school ba ranan don na tashi da ciwon mara ina kwance a dakin mu ko karyawa ban yi ba har lokacin don haka ina cikin barci mai nauyi daya dauke ni naji kira a wayana.
Da kyat na lalubo wayan dake gefe na ina jan tsakin wanda ya tayar dani a wanan lokacin dana dan samu sa,ida na samu barci ya dauke ni.
Koda na dauko har kiran ya katse sunan Yusuf na gani akan wayan ban kai ga tunane ba wani kiran ya sake shigowa again.
Tunane nake a raina may kuma zai fada min yanzu mutanen da suka shareni kusan wata daya ke nan yanzu kuma zai kirani yace min may ?
Kamar in share shi kiran ya katse sai dai na danna recieve inji abinda zai fada min a lokacin na amsa da sallama cikin muryan barci da yanayin ciwo a tare dani.
Naji yace subbahanallahi khadija baki da lafiya ne may ya samay ki naji muryan ki a haka ?
Da sauri ya dago kai yana kallon Yusuf dake magana a waya yaji yace ayya sorry sannu ko kin je asibiti ne nace nasha magani ai ba sai naje asibiti ba.
Idon shi har lokacin yana akan Yusuf din yace may ke damun ta ne naji Yusuf din na fada mai wai banda lafiya ne a kwance nake ma.
Taje asibiti Yusuf yace tace ba sai taje asibiti ba wai karban wayan yayi daga hannun Yusuf din naji muryan shi yana fadin ki shirya yanzu gani nan zuwa nakai ki asibiti ya fada kai tsaye.
Nace naji sauki ba sai kazo ba na kashe wayan wayan ya kalla tare da mikewa tsaye yana rufe file din dake gaban shi ya fara tafiya.
Yisuf dake zaune ya mike juyowa yayi yana fadin ka zauna ka karasa aikin barin je na ganta in dawo Yusuf yace amma kana ganin zata saurare ka idan kaje kai kadai.
Wani kallo yayiwa Yusuf din kamar zaiyi magana sai kuma ya juya ya fita Yusuf ta girgiza kai yana murmushi halin abikin nashi na bashi mamaki ace mutum haka da girman kai.
Nikan ina kashe wayan naja tsuki nace mayaudari kawai naja filo na gyara kwanciya na barcin da ban koma ba kenan idona a rufe nake tunane nace yanzu na tabbatar da karkashin mace yake.
Wata kila matan shi tasamu labari ne ta hana shi kula kowa yanzu ya dawo zai yaudare ni kuma ya bata min lokacina a banza.
Dama ban sa zancen ko kadan a raina ba balle ya damay ni in ma junin shi iya yaudaran mata ne ya bata masu lokaci Allah ba zai bashi saa ba anan naja tsuki na gyara kwanciyana.
Na samu barci ya fara dauka na naji wayan shi ya shigo min na duba na bar wayan nata ruri har ya katse kira uku yai min ban daga ba .
Ranshi ne ya baci sosai yana shirin juyawa sai ga maryam kamar daga sama ta dawo don hankalin ta bai kwanta a yadda ta barni

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login