Showing 18001 words to 21000 words out of 142410 words
cikin school tunda ajike nake da kudi yanzu.
Naje na gama komai har na samu shiga lecture a lokacin sai karfe uku na juyo zuwa gidan mu a hanya na tsaya sai da na sai abinda zanci na wuce zuwa gida.
Sallah na fara yi don lokaci ya shige sosai koda na dawo wanka nayi na dan huta sai na shirya don zuwa sayo abincin da zanyi amfani dashi na wanan time din tunda ina da waddatacen kudi a hannu na saboda wanan tafiyan a saa nayi shi nake gani.
Don ga kudin da ya Amina ta bani wanda dama ita ke sallama na idan zan dawo sai dai kudin bai kan isheni sai na je gida na dan kara roro abinda ke akwai in kara kafin time ya kare.
Sai gashi wanan karon na samu a wurin mama da kuma dan su mijin buzuwa da ya driver ya bani dariya nayi don tuna sun da nayi nace jamgwangwan ke nan.
Ai sune maganin mazan dake ketare matan kasan mu su auro su don kawai ace buzuwa mutum ke aure ko may ko kuwa jaraba ne irin na mazan Nigeria oho ?
Na watsar da maganan su na mike na sabala jakata na rufe kofana na nufi bakin titi don samun abin hauwa a lokacin sahad yana tashe sosai a cikin abuja do haka na yanke shawaran zuwa can in sayo komai da nake so a saukake.
Ban samu wani matsala samun abin hawa ba ni kadai na dauki shata har can bakin sahad mai Napep ya aje ni na karasa shiga ciki.
Ban tsaya wani feleke ba abinda ya kawo ni na fara yi inda na dauki basket na fara zagayawa ban gare su indomie da taliya wanda shine abincin dan makaranta.
Sai shikafa karamin buhu dana dauka da su kayan miya yadda zai kai min time kada yazo ya kare in rasa mai taimaka min.
Bayan na gama da wayan nan sai na nufi bangaren kayan tea madaran Nidor na dauka na gari dan madaidacin gwagwani na juya zan sa a basket din da nake tara kayan a ciki .
Kamshin turaren mijin buzuwa ne ya daki hanci na kaina na kasa ban dago ba sai takalman mutumin da na gani bakake a kafan shi hakaya na dago kai na dan kalle shi.
Mijin buzuwa ne tare da Yusuf suke sayayya a shagon su ma dan daburcewa nayi da ganin su kamar ba zan gaida su ba sai wata zuciya tace min ko dan kudin da ya baki ai kya gaida su.
Sannu ku nace dasu tare da juyawa na fara tura keken kayana Yusuf din ne ya amsa min tare da fadin a a yar garin mu ke ce.
Ummm kawai nace dasu na wuce abina na karasa saura sayayyana na dungura keken zuwa wurin biyan kudi na aje a gaban wanda ke lissafi ina jiran inji ko nawa na kashe a cikin shagon in biya.
Ya gama lissafi kaina yana akan wayana ya dago yace thirtythree thousand five hundred nace OK na bude jakkan dake makale a kafada na zan biya kudin yace ai an biya maki kudin ga canjin ki ma ya rage yana miko min kudin.
Yana kokarin miko min ledojin yaron shagon ya mike da sauri yana karba da mamaki nake kallon shi ina kallon kudin da yake miko min din.
Waya biya nace mai duk da nasan ba wanda ya sani in ba mijin buzuwa da Yusuf dana hadu dasu yanzu ba a ciki.
Yace gasu can suna fita su suka bada kudin sukace indan kin gama sayayya a biya maki suka tafi da sauri nabi bayan su har na samu sun tayar da motan su suna ribas a lokacin.
Ganina Yusuf ya tsaya na dago da zuman fadar wani magana kuma sai na kasa yaya akayi yar garin mu nagan ki a sukwane ko hanya zamu rage maki ne ?
Nace murya a tausashe aa nazo inyi godiya ne mai shago yace kun biya min kudin kayan na mika mai canji nace ga sauran kudin daya rage nan.
Nuna min mijin bazuwa yaya yace bani na biya ba ogana ne ya biya maki albarkacin ki na yar mama mun yasa ya biya maki ban san sanda nace mijin buzuwa na gode ba.
Ido ya waro waje jin abinda na kirashi dashi shiko Yusuf dariya abin ya bashi yace kwarai kuwa mijin buzuwa ne abokiyar fadan ki ko ?
Sai nayi kasa da kai kunya ya kamani nace ga sauran canji ina mikawa Yusuf din kudin kai ya girgiza min yace ai shi bai kyauta ya karba jeki dashi Allah ne ya baki sai a kara ayi provition ko don naga alaman sayayyan yan makaranta kikayi.
Kallon ledan da yaron ke biye dani dasu nayi nadan yi murmushi nace na to gode kai mun godiya wurin mijin buzuwa zai ji yace dani.
Ai da kizo mu sauke ki don naga gaki da kaya dayawa abin hawa zai maki wuyan samu a nan da sauri mijin buzuwa yace amma dai kasan sauri nakeyi ko ?
Haba baka gani marance yayi ina zata samu abin hawa mu sauke ta mana sai mu tafi aiba dadewa zamuyi ba a can ko may kace yana bukatan jin ra ayin shi.
Da sauri nace a a zan hau napep a bakin titi zaku iya tafiya na gode yana kokari bude mota yace a a ai ba zamu bar yar mama a nan na shiga kawai mu sauke ki kada ki fada ma mama mun ganki muki rage maki hanya tayi muna fada.
Ya fito ya bude booth din motan yake magana ban da yadda na iya dole ina kallo yasa mun kayan a booth din su ya bude min bayan hangamaymay jeep din su na shiga sanyi da kamshi kawai ke tashi a cikin motar.
Ya shigo ya tayar da motar muka fara hanya shiko mijin buzuwa ko ta kan mu bai yi ba sai faman aiki yake a sytem din shi saman jukin shi.
A hankali yake tukin motar mun dan bar sahada din Yusuf yace mijin buzuwa sorry fa mun bata maka lokaci ko ?
Ban son iskanci yace a harzuke sai kuma ya juyo gare ni yana fuskanta yace and ke kuma duk na kara jin kin kirani da wanan sunan sai na bata maki rai wallahi.
Da sauri nace ni kada kaga laifi na haka naji kowa na kiran ka da mijin buzuwa bani na fara fada ba ina magana ina jujuya idanuwa na manya.
Dariya Yusuf keyi muna yace a a mijin buzuwa da haka kowa ya sanka a layin mu don ta fada yanzu shine zakaji haushin ta nace ai shi nagani nima.
Yace dakyau yar mama har lokacin wani kallon takaici yake min yaja tsuki ya mayar da kan shi ga abinda yake yi ya fita batun mu da Yusuf din.
Yace yar mama ke may sunan ki sai naji mijin buzuwa yaja wani uban tsuki yace kai malam kafa san aiki nake yi ka samu yarinya kana biye mata don wauta.
Kasa kasa nace wai yarinya yarinyar dai tafi buzuwan matarka yasin ban dauka maganan duk sun jini ba a motan sai gani nayi ya rufe laptop din ya dafe kan shi da hannu daya.
Shiko Yusuf cewa yayi a sosai ma yasani ai gashi yana gani a gaban shi yace kai Yusuf tsaya in fita motar nan don Allah kun isheni wallahi ban son damuwa kasani.
Maimakon ya tsaya kamar yadda yace sai ya kara ma motan wuta ya harba saman titi da sauri shi yana dariya ya sake cewa baki fada min sunan ki ba mana.
Khadija nake yace suna mai kyau a uni ke karatu ko ina nace eh anan nake yace dakyau aji nawa yanzu nace ban dade da farawa ba biyu muka shiga yanzu.
Kai amma kinyi kokari nake ganin ki yarinya ashe yarinyar da kwazon ta yace may kike karantawa anan ?
Ban kai ga bashi amsa ba yace yaushe ne kazama dan jarida haka Yusuf ban sani ba wanan tambaya ai yayi yawa haka yace ai ba zaka san na zama dan jarida ba sai na karasa tambaya na tukun.
Kawar da kai yayi gefen window motar yana kallon titi Yusuf din yace baki bani amsa ba nace bari in ogan ka ya fita bai san ni nafishi rashin son magana ba ma .
Yace aini naga alama shi ne dai kamar bai ga hakan ba ke nan zan bari sai next haduwa mu sai mu dora a ida muka tsaya tunda ku dukan baku son hayaniya jin nayi shiru yasa ya dan juyo yana satan kallo don jin banyi magana niko ina kokarin ciro wayana daga ciki jakkata da ake kirana.
Bayan na dauko naga baba nane ke kira da sauri na dauko ina fadin daddy i miss you ina mama yace gata kusa dani jiya anty ki tace kin dawo makaranta nace eh daddy amma ban zan zo minna yanzu ba sai dai hutu ina gani.
Mun gama watan da naji Yusuf yace ashe ke yar Niger state ne nace eh ni yar minna ce yace a cikin garin minna kuke da zama ?
Ohh god wanan wani irin abune haka for god sake in kana son jin kwab ne basai kuje gidan redio ba kuyi wannan abi damay yai kama don Allah.
Ku ajeni daga nan don Allah zann karasa da napep don ma mun kawo kusa da inda nake ai a haba ke ko baki son muga a inda kike ne don watarna idan za a bamu sako mu baki.
No I no wan wahala ne ji yadda yake ma fada ban son in ja maka matsala gun ogon ka ne don naga kamar bai so dauka na da kayi ba beside nima din ban son shiga mota dashi don takurawa.
Ke yace yana kallo na a zurke yace ka neman min rai ni a wurin wanan yarinyar Yusuf harta kalli idona tace ina takura mata.
Ya kara yana jan tsaki don Allah yaya Yusuf ka tsaya in sauka anan tun bai yi ball dani waje ba don ban daukan irin wanan na karasa fadi a hankali.
Ina zamu bi don mun kawo unguwar Yusuf ya ke tambayana nace wancan layin zaka bi anan gida jen namu suke ya dan gangara kadan sai nace wancan get din zaka tsaya nagode ina kokarin mikewa ya ja ya tsaya get din a wagale yake a lokacin.
Bai bode motar ba sai yace a nan kike da zama ke nan eh kawai na bashi amsa yana sake bin gidan da kallo sai can ya bude mota nima na bude gefen da nake na fito.
Ya fito ya fara fitar min da kayana daga cikin motar ina tsaye gefe har ya gama ya dago yana cewa kona shigar maki dashi ne ciki.
Abinda yasa ni murmushi ke nan har dimple dina ya dan lutsa kadan yace ko maza basu shi nace ko haka na gode Allah ya saka da alheri kai min godiya wurin mijin buzuwa.
Dariya ya kwashe dashi ya shige mota yana dariya ina tsaye a wurin suka ja motar suka wuce na sauke ajiyan zuciya a hankali na duba tarin kayan dake gaba na a lokaci.
Shiko yana shiga motar ya sauke ajiyan zuciya yana fadin kai yarinyar ta hadu wallahi ga kyau ga zakin murya kamar dai ita tai kanta ji idanuwa karmar ita ta tsaya ta halici kanta wallahi.
Tsakiya yaja yace wai yaushe ka koma haka ne don Allah ka koma kamar wani sabon shiga a ganin mace mai kyau.
Wanan din kyaunta na daban ne ai dole ne a yabata wallahi don komai akwai zamzam wanan sai irin gidajen ku ai.
Gidan wa ya juyo da sauri yana fuskantan shi cikin alaman tabaya a fuskan shi yace ban ga laifin Nafisa ba da ta haukace min jiya a gida.
Hauka fa kace yace hauka mana don kawai mama tasa mun rage ma yarinyar nan hanya take ta hauka wai mama na son shirya wani abune akai.
Jiya koda na koma gida gaba daya duk ta hargitsa komai na falon sama da daki wai tana kishin wanan din.
Kaji ba Nafisa tasan abinda ta gani anan ita ke nan ma mace taga inda kyau da fari ke aiki ba farin bane kawai irin nata.
Yace cikin gatse gashi fa in akwai kyau ba gashi may akayi yace kasani ko duk ta hada kai dai ka kwantar da hankalin kasha kallo kawai a nan.
No warnder Nafisa take fadin bata yarda dakai ba ashe tana da gaskiya yau kaine da bakin ka kake fadin inso wata bayan ta ni wata mace kuma zan so yanzu nidake da Nafisa a gida na.
Baki Yusuf ya tabe yace ai ko baka kai namiji ba idan ka buge ga wanan buzuwa ke nan ka zama mijin buzuwa da gaske.
Lumshe ido yayi da Yusuf ya fadi hakan yace yarinyar nan ma ta raina ni wallahi da ganin ta bata da kunya dama don dashi ta tare ni.
Wallahi yarinyar ta hadu ne kai dai kawai ka mace ga son yar buzuwa baka ganin sauran mata da gashi yanzu.
Ina mukayi yace mashi yana kallon shi don son ji yace kaini gida kawai murmushi yayi tare da fadin buzuwa tayi kira ke nan ?
Bai ce dashi komai ba sai lumshe idon da yayi mai kawai yana sauka yace to mijin buzuwa sai gobe ke nan ko don nasan in kashiga ka shige ke nan .
Harara ya watsa mai yana tafiya yana gyara jakkar laptop din shi cikin hasala da abokin mashi.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUAgidan su kuma Nafisa ne ke waya da kawar ta da ta baro kaduna wace suke kira da madam a cikin su tantiriyace ta kwarai na fada.
Da mijin ta sai dai kamar itace mijin ba mata ba don sai yadda tayi da mijin a gidan idan tace kada ya zauna bai isa ya zauna ba.
Atakaice dai ya zama mijin tace ga madam ko kawayen nata zasu iya aiken shi ya tafi komai nisan wuri koda da kafane sai yatafi yadawo.
Itace Nafisa ta kira tana son fada mata abinda ya faru da ita bayan barin su kaduna ta dauko wayan ta madam ta soma nema a wayan sai dai wayan nata ringing ba a daga wayan ba takaici ne ya kama Nafisa.
Ta ja tsaki ta na fadin yar iskan ko gidan uban wa ta shiga waya nata ringing haka bata dauka ba har ya katse bata dauka ba kin sake kiran layin tayi a lokacin sai taci gaba da tunanen ta tanayi tana kada kafan ta daya dake har de.
Babu abin da take tunawa sai irin shirmay da ta tafka jiya din akan bakin kishin dake damun zuciyar ta akan mijin ta wanda take mashi son daba taba yi ma wani abu ba sai dai kuma a kasan zuciyar ta ba so bane can na har abandan don da zai iya shiga wani halin jarabtan rayuwa a yanzu tsaba zata iya gudun shi ta koma wa mai maski.
Wayan nata aka kira ya hanata karasa muna jin birnin zuciyar sai ta dan sake guntun murmushi tana daukan wayan nata tare da fadin Aloh ina kika shiga nake ta kiranki baki daga waya ba.
Cikin muryan barci madam din tace tana hamma baki hangale bata fasa magana duk da tana hamman tace wallahi barci nakeyi tunda rana.
Tsuki Nafisa taja tare da fadin barci sai kace wata mai ciki ko kasa ni don Allah watseke fuskan ki kiji ni magana nake son muyi dake ki ban shawara.
Madam tace ina jin ki matar manya dadi Nafisa take ji idan su madam na fada mata wanan sunan madam din ne tace ke nake sauraro fa.
Wallahi ke dai madam kin san ko sai da munafukar tsohonwan nan ta hadamu da yarinyar da nake fada maku tace mu rage mata hanya ?
Don Allah ki bari madam ta fada itako tace sosai kuwa ai saida muka dauke ta a mota daya mukai tafiyan.
Tace yaya kika bari haka ya faru don Allah kin ko san iein mijin ki neman su mata keyi ido a rufe nasha fada maki ki nisanta shi daga ko wace mace in ba muraharamin sa bace har kika yarda hakan yafaru dake.
Ke dai bari madam nanu mashi rashin yarda na ga hakan amma ya rufe ido yace shi yace umurnin mahaifiyar shi ce dole ya bi.
Madam tace yaya kukayi a motar injin baki basu daman sakewa da juna ba a motan ?
Tace ai in fada maki ban yarda ko daga kai yayi ya kalle ta ba kuma nima ban sake ayi hakan ba sai dai mun kwashi rikici dashi sosai da muka iso gida wai zai tafi office a sauke shi sai a wuce da ita.
Bude mashi wuta nayi sosai in fada maki sai da mukayi kaca kaca dashi na kuma hana shi fita sai da aka kaita a ka dawo san nan ya tafi.
Da haushi da bakin ciki ya kamani duk na farfasa kayan falon nan gaba daya don in nuna mashi bacin raina don gobe kada ya kara min haka.
Madam tace kash aike kinji matsalan