Showing 78001 words to 81000 words out of 142410 words
ke mana don Allah tashi kije kada ki bata mai lokaci dan hararan ta nayi nace na kirashi ne ?
Sai da na tsaya shirya nasa wasu material a jikina din kin buje da riga akai min wani zuwa kaduna da nayi maron colour dinkin yadan matse min jiki kadan don dan jikin dana kara yanzu.
Sun kama min jiki tam sai kitson da mukayi satin nan na ghana wiving ya kara fito min da fuskana shar ga matsiyacin kamshin dake tashi a jikina wanda ke tafiya da imanin wanda ya shaka.
Tun daga nisa ya zuba min ido yana karewa shiga na kallo har na karaso inda yake kofan motar ya bude min wai nashiga.
Naki nace cikin girgiza mashi kaina yace common shigo don Allah mu tafi rakiya zaki min wani guri da sauri nace a hakan zan tafi wani gu.
Ko banza kuma ba zan shiga motar ka ba again agogon hannun shi ya duba yace cikin dakewa kina bata min lokaci ki shiga mutafi.
Tunda muka fara tafiya ba wanda yai magana a motar sai shi dake tuki a hankali cikin wani irin yana yi yana yi yana wani furzo iska daga bskin shi lokaci lokaci.
Sai can ya juyo inda nake yace zakici wani abune kaina yana a waya na da sauri na dago kai nace wani sai kuma ja girgiza mashi kai nace ni a koshe nake.
Ok rakani inci wani abu tun safe banci abinci ba da sauri na zaro ido nace azumi kayi ne ?
Dashi nayi ma da zai fi min sauki yace ba tare da ya dube ni ba na mayar da kaina ga titi ina kallo sai kuma can kamar an tsunkule nace matar ka tayi tafiya ne ?
Bai bani amsa ba sai karya kan motar shi da yayi zuwa wani restaurant din abinci mai kyau gurin da daukan ido ya parke a wurin .
Mun shiga naga tsarin wurin yana da kyau sosai da alama yasan wurin da kyau don wani ke bebben wuri naga yana nufa a cikin wurin.
Min zauna masu aiki gurin suka zo suna tambayan shi mai za a kawo muna ne yace ferfesu kawai zai sha bayan an mika mai dan takarda ya duba.
Koda aka kawo mai bai wani sha da yawa ba naka ya aje cibin yana goge bakin shi tare da fadin tashi muje kawai nikan mike wa nayi nabi bayan shi.
Sai da ya biya su kudin su muka fice muka bar gurin ina mamaki a raina nace yaya mutum kamar shi baici komai ba sai a wurin cin abinci zaici kuma bai tsaya yaci wani abin kirki ba.
Kasa hakkuri nayi nace amma wanan ba girman ka bane cin abinci a waje alhali kana da iya li kuma a gari.
Kamar bai jini ba yana tukin shi sai dai ban san ida muka nufa ba can naji yace dani yaya kike son inyi khadija in banci abinci a waje ba ?
Kamar yaya kuma kana da mata a gida zaka ce haka yaya Abdul yace sunana Abdulsamad ko ke ma zaki bata min suna ne ?
Yi hakkuri bani na kashe karen ba ratayan buzu ba zai zama nawa ba in bai zama naki ba wace ki dauki karen ?
Naci yau kana da magana ke nan yace da yawa khadija iam not in good mood at all.
Ayyah sorry Allah ya sauwa koma maye yayi maka mafita a kan shi yace amin na gode da adduan ki gare ni yaci gaba da tuki.
Matsala a gun aiki ne ya taso maka yace matsala a gida na yake subbahanallahi nace dashi tare da dan kallon fuskan shi.
Yace khadija dole in ci abinci a waje ko in zauna da yunwa ko zaki taimaka ki dinga bani abinci in dinga zuwa wurin ki ina ci idan na taso office.
Kai don Allah ka daina zolaya abincin yan makaranta ne zakaci wanan ai sai mu da yazama muna dole muci shi.
Badai ke kina ci ba nace sosai kuwa yace to ni mai zai hana inci tunda ke kika iyaci sai dai idan rowa zaki min kuma beside ke kika ce na daina cin abincin waje.
Nace matar da ran ta da lafiyan ta zaka wai ni na dinga dafa ma abinci kamar wata wacce ka aje da zaman banza.
Bai kara magana ba sai horn da yayi a bakin wani gida aka bude mai muka shiga dayan motar da suke zuwa wuri na da farko ne na gani a gidan.
Maigidan na ciki ya tambayi mai gadi ya na gaishe shi bai amsa ba ya jefa mai tambayan shi sai maigadin yace yana nan bai dade da shigowa gidan ba.
Fita yayi daga motan ya zagayo ya bude bangare da nake zaune jin ya tambayi mai gidan yasa banji wani tsoron shiga gidan ba.
Sanyin A C ne ya tari fuskana da kamshin air freshner da falon ya dauka falon ya tsaru komai akwai a ciki ga wasu manyan kujeru da aka kawata falon dasu.
Yana waya koda muke shiga gidan yana fadin kafito gamu a falon gidan ka yace a wayan baifi second ba naji ana bude kofan daga cikin gidan sai ganin Yusuf ya fito yana saye da kayan shan iska irin ta maza wando dogo tare da yar riga armless a jikin shi.
Yana gani na ya bude baki da mamaki yace kace yau ina da babban bakuwa a gidana ina kafito da yar mama da yamman nan haka ?
Ya nuna mun kujera da hannu yace bissimillah zauna mana khadija bamu hadu ba sai yau nace ina wuni ya amsa da lafiya kalau ya kike ?
Ina nan lafiya yace Alhamdullahi yau sai gaki a gida na kwatsam na gan ki ba tsammani nace wallahi ga wanda ya dauko ni nan bai fada min ida zamu zo ba yace dai wani guri zan raka shi.
Yayi maki wayan manya kenan don ya baki mamaki dan hararan gefen da yake nayi mikewa Yusuf yayi yana fadin barin kawo maku abinsha sai dai kiyi hakkuri kin san gidan gwauro kika zo.
Da sauri na dago kai ina kallon shi da mamaki nace baka da aure ne dama yace eh baki sani bane yar mama ?
Ashe mutumin bai fada maki komai game da ni ba yace ma Yusuf din an fada ma kowa irin ka ne mai zuba a lokaci guda.
Yusuf yana dariya ya wuce inda fridge din shi yake ya dauko drink a ciki tare da kofuna ya kawo gaban mu ya aje nidai ido nake binsu dashi kawai.
Ya aje tare da zama yana fadin bissimillah kusha lemon shi yasha nin ban sha ba gani nake kamar plain ne suke shirya min in fada ciki.
Yayi yayi dani don insha nace wallahi na gode mai zai sa ka damu haka idan bata sha ba yace mai kasan bakuwa tace ita dole in damu idan tazo gida na bataci wani abu ba.
Daukan cup nayi na tsiyayya kadan na dan kurba na aje cup din ina fadin na gode shima tunda ya kurba sau biyu ya koma ya jingina da kujera tare da dafe kanshi da hannun shi .
Yaya dai Abdulsamad lafiya ko dan tsuki yaja tare da kara dafe kan nashi fuskan shi ya nuna alamun bacin rai da damuwa.
Juyawa yayi guri na yana fadin may ke faruwa ne khadija nace nima haka naganshi wallahi ko maganan da nayi mai ne yasa shi bacin rai ban sani ba ?
Ni kuma gaskiya na fada mai ba girman shi bane cin abinci a waje ban san ranshi zai baci da kalamina ba na fada mai haka.
Dariya ya dan yi tare da fadin see you akan dan wanan maganan zan bata raina ai gaskiya kika fada bai dace ba nima na san da hakan.
Watau khadija mutumin naki yana da matsala ne a gidan shi wallahi wana abin ya dade yana damun mu muma.
Ace mutum kamar wanan ba abinda ya nema ya rasa a duniya amma cin abincin gidan shi ya gagare shi sai na waje ?
Shiru nayi ina kallon shi yace ya zama dole mu samu mafita akan wanan matsala kada abin yazo yai yawa na yaushe kuma ?
Ko sau daya aka ganka a waje kana magidanci kana cin abincin sayarwa ai girma ya fadi ko a wurin mutane sai dai a gyara don gaba.
Yarinya kamar tsuhuwa wurin iya tsara magana haka ashe shiya take karatun lauya ya fada a ranshi.
Khadija ni na rasa samun mafita ka wanan matsalar wallahi don ko nafisa ba gyarawa zatayi ba tunda in ita batayi ba bata bari kuma ya dauko yar aiki irin namu na nan wace ta iya saidai yan uwan ta zasuyi.
Wanan kuma shi ya daukar mata don shi yaga zai iya zama a haka don may ba zai dawo da matar shi hala tsoron ta yake yi ?
Sai lokacin ya cire hannun shi da ke saman kanshi yace tsoro tsoron wa nace ka alamu nan sun nuna kuwa buzuwa ta shiga gaban ka.
Ke fa baki da kunya din kikan wuce limit din ki nayi saurin fadin wurin fadin gaskiya ba haka nan Ya Amina na ke fada min wai banda tsoron fadin magana ga kowa.
Ni kuma naga idan gaskiya tazo a fadeta komai dacin ta kuwa dayake baki da kunya ba zaki iya fadin maganan da wani bai iya fadi ai .
Ciki ciki nace a nan zaka zare idanu agida ko a zare maka idanu matsorancin banza kawai.
Ban yi aune ba na gan shi a gaba na waye matsoraci yace cikin zare min idanu Yusuf nace ni gaskiya na fada ai Yusuf ne yace daga fadin gaskiya sai leifi ?
Laifin ka ne mana kaima ka sani ai in ba tsoro ba ka dauki mataki mana a kan haka mugani nace aishi na gani walla, , ,
Hannu shi yake ya kamo bakina yana fafin wanan wanan baki sai nayi maganin shi wataran zai shiga hankalin shi.
Don Allah ka bari bana son namiji yana taba min jiki wallahi kin dauke ni dan iska ke nan ashe nace bai da kyau yin haka ka sani.
Yusuf yana dariya yace ina zuwa ya barmu a gurin zama yayi a kusa dani yana fadin bari ma yau in nuna maki dan iskan nake.
Tsoro ne ya kamani yadda ya zauna a kusa dani din nace may ye haka malam ?
Malama iskancin nake son nuna maki kalan tawa ki gani ya rankwafo inda fuskana yake har muna iya jin hucin numfashin juna a lokacin.
Cikin sanyi murya nace ka dai san hakan bai dace ba a addinance ai kin san ban san addini ba ni yace wanan ba gaskiya bane don gidan ku kaf hazifai ne kuna karatun addini tun kuna kanana .
Sai naga ya maida kanshi saman kujera yana zaune kamar yadda yake bai daga kusa dani ba yace khadija ina cikin matsala wallahi ina son in gyagyara wasu abubuwan da suka baci min a yanzu.
But i don't know how to make things easy ?
Tausayi ya bani nace ka yawai ta addua da sadaka ga dukan al,umurorin ka sai kaga Allah ya kawo maka mafita a ciki.
Sai ya mike daga hannun kujeran yana fadi n muje in mayar dake yamma ya fara yanzu saurin mike wa nayi ya kira yusuf a waya yana fadin mun tafi.
Yafito da sauri tare da fadin har kun gama hiran ta masoyana zaku tafi kai haba yayana firan masoya kuma a haka ?
Har ya fara tafiya shi muka mara mai baya yusuf ya bani hakkuri akan bai bani komai ba gashi na kawo mai ziyara.
Ba koma nace muka kama hanya na tsaye sai da yaga wucewar mune ya sauke murmushi tare da fadin ikon Allah komai yana da sanadin shi.
Wanan karamar yarinya kuma Allah ya jefo a rayuwan Abdulsamad mutumin da magana da mace a wurin shi aiki
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUYau take son ta gwada abubuwan da aikin boka dan Ondo wanda ya ja mata kunne da gujewa aikata kuskure tace zata tsare in sha Allahu.
Ya shigo bai jima da dawowa ba ya fada wanka Nafisa ta shigo dakon kai tsaye tasamu yana ban dakin gurin wanka nan ta zauna a bakin gadon cike da jiran mijin nata.
Ya fito daga ban dakin ta taso ta karbi duk wani abinda yake ma jikin shi tana mai gama daga goge jiki da shafan mai da saka turare da sauran su.
Shidai ido kawai ya saka ma ta yaga iya gudunta don zuwa yanzu ya fara gano shirin ta sam bai yarda da wanan abinda take mashi ba .
Ya gane sai tana son abu take mashi ladabin shegu a lokacin yake miji da zaran ta samu abinda take so shike nan ta koma ma halinta na I don't care da ta saba dashi.
Zama yayi a bakin gado yana jiran yaji ta inda zata bullo mashi ta dan yi dariya tare da karasowa wurin shi ta zauna itama.
Sai bayan ta zauna ne tace samad a ranshi yace nasan da wanan kan tace wai yaushe ne zamu tafi shopping ga ciki ya fara girma haka ?
Yayi mata kyar da ido sai kuma ya sake guntun murmushi a fuskan shi yace ban san da wanan maganan ba ai.
Ita ko tayine don tana ganin shi ne zai fi saka shi farin ciki har ta samu ta sake da ita ta aiwatar da nufinta gare shi sai kuma taji sabanin hakan a bakin shi.
Sai ta dan tsuke fuska tare da fadin gaskiya ya kamata ace ka shirya wa tafiyan mu zuwa yanzu don kada nazo nayi nauyi da yawa kace ba zan fita ba.
Abdulsamad ya tsura mata ido yana mamakin rigimar Nafisa yanzu bata aje kanta a kusa ba shi kayan bany ko a nan gida Nageria za a samau su ai.
Ya cikin daure fuska kin fi kowa sani komai nake so zan iya odan shi a dan kan kanin lokaci ya iso gare ni ballanta na babu dan da aka haifa a gidan nan da na fita waje na sayo mashi kaya.
Ranta ne taji ya baci don may zaya danganta sauran diyan shi da abinda ke cikin ta a yanzu da ta san tafi karfin kowa ma nashi.
Shikan gado ya hau yana gyara kwanciyan shi don yasan ba tayin abinci zai samu a gurinta ba duk dako yana son saka wani a bakin shi yanzu.
Nafisa kuma bataji dadin haka ba don tana gani idan ta kyale shi bazata samu yadda take son komai ya tafi ba har ya sadu da ita don ta riga ta shafa maganin da boka ya bata tayi amfani dashi.
Tabo shi tayi tana kwantawa a jikin shi da sauri ya juyo gareta yana fadin barni banda lokacin aiwatar da wani abu yau a tsakanin mu.
Tace aiko tunda ni ina da bukatan ka tare dani dole zaka daure ka biya min bukatana haka nan yasan ta da son ya kusance ta akai akai wanda a baya yakan biye mata.
Kara kwanto mashi tayi ya kara daga ta ajikin shi karo na biyu yace ki barni please na fada maki ina bukatan kasancewa ni kadai ne duk iya nacin ta dole ta barshi tafita kamar zatayi hauka take jin kanta a lokacin.
Ta jefeshi da harara ya karkace kai yana mamakin tace ba laifin ka bane tunda kai kana fita waje yanzu kana samun inda ke sauke nauyin ka acan.
Sheri zaki min yau kuma Nafisa tace amma kasan baka kyauta mi ba nima idan kai min haka yau don ina bukace dakai a yanzu yace ki hakkuri nace yau ba zaki samu ba ya gyara kwanciya yana fadin hakan.
A yadda ta rude sai ta bashi tausayi amma bai iya aiwatar da komai a yadda yake jin gabanshi yana faduwa mai.
Jin fitan ta a fusace bayan ta gama mashi mita ta fice daga dakin ya girgiza kanshi ya gyara kwanciyan shi sai barci acikin barcin ne yayi mafalkin mara dadi da Nafisa wanda ya tayar mashi da hankali.
Tunda ya falka bai koma barci ba tunanen mafalkin da yayi ne ya tsaya mashi a rai mikewa yayi ya dauro alwala ya gabatar da sallah tare da samun sauki alamura a gare shi kamar yadda mahaifan shi ke koyar dashi ko wani lokaci.
Washe gari ta tashi gaban ta yana fitar da wani irin kaikayi dake damun ta sam bata kawo cewa aikin boka da ta sakane ya jawo mata hakan ba.
Tunda ya watsa ruwa ya fito yana shiri zuciyar shi cike da tunanen abubuwan da suke faruwa dashi ya yanzu din.
Sai da ya biya dakin ta ya dubata kamar yadda yayi mafalkin a haka ya samay ta tana ta faman da soshe soshe don kaikayin dake damun ta.
Yace may ke damuwan ki haka ne kike wanan soshe soshen haka cikin bacin rai tace dama ai haka kake so dani tunda na bukace ka kashere ni.
Banga