Showing 114001 words to 117000 words out of 142410 words

Chapter 39 - MIJIN BUZUWA COMPLETE

Start ads

08 Aug 2025

40

Middle Ads

shihiri ne in kunyi diba ga irin matar nan nashi zai yuyu wani aike tayi mai wanda bai zauna a jikin shi ba sai ya iya haifar mai da hakan.
Idan ba kasan da irin shi ba ba kowa ne yake gane hakan ba zaka mutum na fama da ciwon kai mai tsanani ayi ta magani kamar ba a yi.
Nima gani nayi a makwabtar mu haka ya faru koma dai ba shi bane ya kamata ku hada da na gargajiya tunda likitoci sun ce basu ga komai ba su .
Shiru yayi na wani lokaci ba tare da yayi magana ba abubuwa da dama yake tunane a ranshi sai can yace maganan ki na da kamar gaskiya khadija.
Don dai a yadda yake rike kai yana kugi zakace zai iya mutuwa ne a lokacin kuma kan sai cikin dare kawai yake damun shi .
Nace abinda ya ban mamaki ke nan nima ace ciwon kai kamar na sihiri sai dare kawai yake tashi cikin ne ma wani lokaci yake dan tashi da safe ko idan ya ci wani abu.
Allah ya sauwaka nace maryam dashi suka amsa da amin lokaci daya maryam tace gashi har ya ci ayaba ya zauna mashi ciki lafiya abin ya ban mamaki ai.
Nidai har muka shiga hostel ban yi magana ba sai dai ido da sauraren su da nake yi kawai.
Kwance nake tun bayan dawowan mu da nayi sallah magariba da ishai na kwanta nan iya cin komai ba na kwanta zuciya na cike da damuwa.
Washe gari tunda safe da na tashi ina shiri jikina ba karfi a tare dani sai tunane nake na yadda na ganshi kwance jiya yana jin jiki sosai wai a haka yaji sauki ke nan.
Waya na nadauko ba tare da na tsaya tunane ko yana barci a wanan lokacin ba na dana mai kira wayan ya shiga yana ta ringing ba a daga ba.
Sai kusan zai katse aka daga wayan muryan shi da alaman barci a tare dashi yace hello Deedar ya kike nace ina kwana ya amsa da lafiya nace ya jikin yace jiki da sauki nagode.
Sai nayi shiru yace hello dayaji shirun yai yawa nace kaji sauki sosai ko yace mm a ji sauki Deedar ya kuka koma jiya nace lafiya a sanyaye.
Can nace nagode Allah saka da alheri yace namay fa nace na tsaraban da ka kawo min ranan nagode kwarai Allah saka da alheri tsaraba haka da yawa.
Yace ba komai nagode sai an jima na kashe wayan ajiyan zuciya na sauke ina aje wayan cikin hand bag dina tare da lumshe idona.
Haka na shiga makaranta jiki ba karfi duk yinin ranan haka nayi shi a sukurkuce dani yau ma kamar jiya na dawo ban dade ba a cikin makaranta na dawo.

Yusuf tunda ya aje mu hankalin shi ya koma kan maganan mu kawu salisu ya kira yana fada mai matsalan Abdulsamad din.
Kawu yace zai je a ga malam yayi mashi bayani komai kai tsaye asibiti ya nufo inda ya samu Nafisa na fada da security a bakin get.
Nan ya tsaya rai bace yake masu magana abin mamaki sai ta maida fadan wurin shi tana fadin sune ai munafukan da suka ja a wullakanta ta din sun dauko karuwa sun kawo ma samad har cikin asibiti tazo tana iskanci.
Da mamaki yace karuwa may ya hada AA da karuwa kuma tace in ba karuwa bane may zai sa tazo tana bashi ayaba a baki ?
Kai ya girgiza yana mamakin inda maganan ya fito mata yayiwa security din magana akan su kyalesu su wuce basai sun tura ta ba.
Ciki ya shiga fuskan su kawai da ya kalla yasan akwai damuwa a tare dasu yace mommy ya akayi har Nafisa tazo nan da fitina haka ?
Yusuf Nafisa tana fada ne bisa ka,ida zuwa tayi nan tana hauka nasan kawayen ta ne da suka zo dazun suka fada mata don dun samu yana cin ayaban da suka shigo.
Ya girgiza kai yana murmushi yace mun dai auna arziki bata samu su khadija a nan ba da ba karamin tashin hankali zasu yi ba don ko ita khadija ba baya ba da alama wurin fitina.
Khadija ce kaidai zata yi daidai da gidan Abdulsamad a halin yanzu mommy don itace kadai nake ganin zata iya da Nafisa a yanzu.
Shi babangidan yace yana son ta ne ko ya nuna wani alama na ra,ayin tane da dai zanyi hakan gaskiya da yayi dace da kamilan mace a gidan shi don ni yarinyar tanayi min wallahi.
Don akwaita da natsuwa da girmama na gaban ta ga ilimi addini da na boko ta samu a tare da ita kaga kowa ma zaiyi kwadayin wanan mace a gidan shi ai.
Tun farko ina ma yaran gidan mu kwadayin ta sai dai kasan yaron yanzu ba ai masa haka gara inshi yagani da kanshi yace yana yi shine za a zauna lafiya.
Duk da nasan khadija tana da masoya ko anan kaduna din amma haka bai hanani jin wani nawa ya so ta ba.
Amma kai da kake fadin haka akwai wani abu makamancin so ne a tsaka su dama kodai dacewan haka kaima ka hango yasa kai magana ?
Mommy gaskiya ba zan boye maki ba akwai sai dai dan nakine miskilanci da ji da kai da izza yahana shi tsaya su fuskanji juna shi da ita kin san kuma ba a son mutum da haka.
Shi yana ganin idan yaje mata da zancen so kamar ya zubar da kiman shi a gare ta ita kuma khadijan kallon yan uwa take muna a yadda na fahinta ni.
Sai dai dukkan su suna boye feeling din su ga juna ne amma indan so akwai so gaskiya miskilanci shi dai ne ya hana ya nuna mata haka din.
Murmushi mommy tayi tana fadin dana ai ba a haka yanzu matan yanzu sai da so ake saye zuciyar su bawai da kudi ba kawai don ba ko wace mace bace kudi yake gaban ta ba.
Mommy dan nan naki in kiyi duba gare shi bai fa san so ba shi don a yadda ya auri Fati da Nafisa ba wai an tsaya anyi wani soyayya bane dasu.
Auren fati dai kin san komai akai hadine na iyayye tun farko ita kuma Nafisa abu biyu ne nake ganin ya kai su ga aure.
Na farko kin san akwai shi da son fararen mata dogaye sai na biyu ita din batazo mashi abanza ba sai da ta asirce shi.
Wani kallo yayi ma Yusuf din dake magana yana kwane ya harde hannayen shi sama kirjin shi kafafuwan shi a harde yana karkada su a hankali.
Ni kake wa sheri haka Yusuf kuma a gabana Yusuf yace ba sheri bane abinda nagani nake fadi ni baka son khadija ne karya ne maka ?
Ke nan ashe sun dade tare da ita mommy ta tambayi Yusuf din cikin son karin bayani gare shi.
Don ni na dauka zuwan nan na su Binta ne kuka hadu da khadija din har kuka santa yace a,a mommy ba zuwan su bane muka santa don gaskiya dama muna tare da ita.
Ikon Allah a mu kuka boyewa mawa dama amma yaran nan kun iya taku har karshe yanzu ashe kuna tare da yarinyar nan kuna nuna ba komai a tsakanin ku da farko ?
Hakan na da kyau da kuka boye ba laifi bane haka yayi daidai nima zan kama baki na inja ga wanan maganan badon komai zamuyi haka ba sai don matan shi.
Duba yadda Nafisa tazo nan tayi muna yanzu bata san da komai ba ke nan ina ga inta sani din sai idan abu ya kankama a tsakanin su lokacin da wani bai iya komai za a fitar da zancen ga kowa yaji.
Don idan ba haka ba maganar sai yazo yabi ruwa azo ba ayi shi ba sai dai babangida ya kamata ka daina wanan halin naka don ba haka ake neman ba yanzu.
Kamata yayi ka bata lokacin ka ka nuna mata so da kauna ta yadda zata saki jiki dakai har a cin ma abinda ake so.
Mommy sheri Yusuf ne kawai yarinyar nan a yan uwa ta dauke mu har ta gabatar muna da wanda take so ta aura fa.
Tayaya zaice kuma ni na kutsa kaina ga abinda ta riga tayi nisa ga wani gare shi da sauri Yusuf yace.
Wanan magana ba gaskiya bane dakai da mamud din da tace wa yariga wa ta riga sani cikin ku biyun kai ta fara sani kasani ba wancen ta fara haduwa dashi ba kaine ta fara sani.
Yusuf kabar wanan zancen don Allah yarinyar da kaji mommy ma ta fada tana da masu son ta akan may zan tsaya bata lokacin gun ta karamar yarinya ma da ita haka da tara maza ai babu komai sai wulkanci a gurin ta.
Da sauri Yusuf yace ta taba yima wullakanci ne da zaka fadi haka san nan kuma kowa ai da karfin shi yake zuwa ya gwada tashi sa,an akan mace idan tai ruwa rijaya idan batayi ba masai.
Banda wanan lokaci kai ka sani so don Allah kubar wanan zancen na Deedar please zan dai yi hakkuri ina zauna da wa yan nan da Allah ya hadani dasu.
Munyi magana da Abba Fati zata dawo dakin ta karshen watan nan ya kuke son inyi da mata uku yanzu biyun ma yaya na iya dasu balle na kara ma kaina wani wahala can.
Aure ne kawai mafita gare ka a yanzu saboda ta haka ne kawai zai kawo fitar da zargin da ake maka akan Nafisa ta mallake ka don ni nasan matsalan ku da Fati wanda ma kowa ya sani in ba wani aure kara yi aka gani ba, bazaka fita bakin mutane da zargi su a kan ba.
Mommy ban damu da abinda mutane suke cewa a gare ni ba tunda nasan ina tsare kaina ga duk wani abin hani.
Mommy tace babangida kada kace haka idan kasan kana son yarinyar nan kada ka bari wani yazo ya kwace ta daga gare ka.
Shawaran da zanbaka shine ba,a kin shawara idan na kwarai ne ka gwada a gani ko hakan ne mafita a gare mu kaga sai a wuce wurin a manta da komai sai fatan samun zuri, a masu albarka.
Murmushi Yusuf yayi Allah yakawo lahadi don litinin yai niss inji maza ranan nasan ni za,a kira da munafuki yafi a kirga gun Nafisa.
Yanzun dai maganan mommy ne mubar wanan zancen a yadda yake a rufe sai munga komai ya kan kama za a ji.
Mommy kaifin basira irin na khadija yasa nake mashi kwadayin ta a gidan shi don khadija yarinya ce mai tunane wallahi.
Mommy ta tashi taje yin alwala lokacin ne Yusuf ke fada mashi gobe yana son ya je zaria da safe akan ciwon shi yaga malamin nan na gurin kawu salisu.
Yace kana ganin zuwan ka wurin shi yana da wani alaka da ciwo nane ko may ko wani abin ne zai kaika wurin shi.
Sai da ya mike tsaye don zuwa sallah ya bashi amsa da cewa akan ciwon ka nake son zuwa can don yanzu wanan shawaran yazo min .
Bai mai magana ba sai mikewan da yayi shima don zuwa yin sallah magariba data gabato a lokacin.

Da dare yana kwance na kira shi muka gaisa na ba maryam ita ma tayi mashi yaya jiki yace da sauki ya gode muka kashe wayan.
Maryam ne tace ni har yanzu sai nake ganin kamar jikin nashi da sauki a yadda naji muryan shi a yanzu nace haka nima nake tsammani danaji.
Daga haka ban kara cewa da ita komai ba ina kwance rigingine ta dauko waya tasa muna kira,a shine naji hankalina yana kwantawa a hankali naji damuwan da nake ciki wanda ban san dalilin shi ya fita a raina har barci ya dauke ni daga hakan.
Washegari na tashi wasai dani wanka nayi na shirya na kama hanya zuwa cikin makaranta don ina da test a ranan gashi banyi wani karatu ba isashe.
Ban fito ba sai yamma lis na fito daga cikin makarantan alokacin yunwa ne ya addabe sosai a sukwane na shigo dakin ina wurgar da handbag dina ina cire hijjab din dake kaina a lokacin.
Maryam kuma bata dawo ba nake gani alokacin don haka na fara kokarin hada jeloup din taliya don ina ganin shine mafi saukin dahuwa a gare ni a wanan lokacin.
Agurguje nake aikin daidai lokacin da na kusan gamawa ne wayana kira ya shigo min sai da na duba abincin sama sama na dauki wayan.
Ban tsaya duba mai kiran nawa ba naji murya shi yana fadin yau ba akira anji jikin nawa ba dan banufen naki ya dauke maki hankali ko ?
Murmushi nayi a baiyane ta yadda har yaji a cikin wayan mommy bata nan ne daka bugo min waya ?
Kina tsoron taji ina waya dake ne a gaban ta komay ?
Ina da kunya da girmama na gaba shiyasa amma ba don tsoro ko wani abuba kawai don kawaici ga manya ne .
Gata zaune tana jin ki ko in bata wayan ku gaisa ne kana fara shi wanan ma ai fadi ne kawai nasan mommy tafita yasa ka kirani kamar yadda nake da kunya kai ma nasan zakaji kunyan waya a gaban ta ai.
Muryan mommy ne take fadin khadija kun koma lafiya jiya ya karatun Allah ya tsare ya kare ban iya cewa komai ba sai daburcewan da nayi a lokacin.
Hello khadija ba kya jine ina magana kin yi shiru nan ma ban iya magana ba shiru nayi mata a lokacin sai naji tayi murmushi.
Wayan na kashe sai da na gama girkin sai kuma cin abincin ya gagare ni duk da yunwar da nake ji din da farko .
Waya na dauko na tura mashi text kamar haka baka kyauta min ba ya zakai min haka ka san girman mommy a idona kuwa ai sai kasa ta zargi wani abu a zuciyar ta a gare mu.
Na gama na tura mai maryam ta shigo dakin tana fadin wai yau na gaji wallahi zama tayi tana kallon yanayin da ta samay a ciki.
May ya faru tace tana kallon fuska na cikin damuwa ga yadda ta ganni din sake tambayana tayi tana maida hankalin ta gare ni.
Ga abinci can ki diba ina kika tsaya har yamma haka lis wallahi mugun malamin nan namu ya tsaida mu haka yau test din yayi wuta sosai tamike tana fadin har kin ci ne ke tana kallo na.
Kaina girgiza mata tace kin ci wani abin ke nan ko naga ko karyawan kirki baki tsaya kinyi ba kika fita yau.
Wallahi da yunwa na dawo sai da na gama kuma naji ban son cin komai ki sha wanu abu mai ruwa kila yunwa ne yai maki yawa ya hanaki cin abincin.
Ta debo ta fara ci tayi nisa ga ci nake cewa da ita kin san may wanan mutumin yai min yau maryam.
Da sauri ta dago kanta tana fadin wani mutumi mamud ko wa nace wani mamud kuma AA fa don ya maidani karamar yarinya wai a gaban mommy zai kirani yai waya dani.
Maimakon inga damuwa itama a fuskan ta sai naga sabanin hakan a fuskanta dariya ta soma tana fadin lalai wanan dan barki ne .
Ya daure tamau yanzu a gurin mommy ta gama sanin komai a tsakanin ku ke nan ?
Komai kamar yaya ya dai daure ni wallahi tace ai maganin ki ke nan tunda bakya jin shawara ai gara da ya fito maki tanan.
Haushin ta naji sosai a rai na don rashin nuna jin haushin hakan dayayi min da ta nuna rashin damuwan ta akaina.
Bayan ta gama ta mike lokacin nayo alwala zanyi sallah itama ta shiga bayin ta dauro alwala muka gabatar da sallah mu.
Zaune nake bayan na idar da sallah ban bar wurin ba sai da nayi isha,i na mike ina nade sallaya maryam ta mike ta dauki heater tare da dauko cup ta hada min shayi mai kauri saida ta gama ta miko min.
Kamar ba zan karba sai dai na mika hannu ko ba komai nasan shan tea din zai taimaka min ga yunwa da ke ciki na.
Tunda na kwanta ban sake bi ta kan komai ba har barci ya dauke ni a haka yadda nake cikin dare na falka na ga ta rufe min kofa itama tana kwance a kusa dani ranan a dakina ta kwana.

Zaune take a falon madam datai ma tsuke tunda safe ta isa gidan madam din a yadda ta ganta sai take tambayan ta ko lafiya haka da safe.
Madam gaskiya yanzu samad ya rikice min tunda na haihu din nan na rasa gane kan shi gaba daya.
Jiya fa a gaban wanan kishiyar uwar tashi yake fada min wai aure zai kara saboda kawai nace sai ya fada min wace yarinya ne tazo gaida shi har take bare mai ayyaba

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login