Showing 3001 words to 6000 words out of 142410 words
gidan .
Shi kan shi maigidan ba a banza ta barshi ko yanzu kuma bawai ta fasa abinda takeyi din bane sai ma abinda yaci gaba a cikin halayen nata.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU🧠MIJIN BUZUWA🧠
2️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
NOVEL DIN NAN NA KUDI BIYA DARI UKU KO KATIN DARI UKU TA WANAN ACCOUNT DIN 2254380105 ZAINAN IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KI KIRA TA WANAN LAYIN 09026931792 KO 08036959257 ASHA KARATU LAFIYA
Hayaniyar yaran da suka dawo daga makaranta ya dawo da ita ga tunen tace shike nan nawa ta samay ga Affan da dan banzan wayo kawai na shiryasu zuwa cikin gida wurin kakanin su tasan idan sunje can sa samu abinda sukaci a cikin su.
Yaran suna shigowa suka fada mata a jiki suna fadin mama mun dawo yunwa nakeji sosai wallahi karamin ya fada take taji gabanta ya fadi don hakan halin su ne .
Sai subar abinci a cooler makarantarsu su dawo dashi kuma suce yunwa suke ji halin yaro ke nan oya a cire uniform kuje cikin gida wurin su hajiya kwaci abinci a can banson yawan hayaniya yau.
Acan cikin gida kuma dawowan yaran gidan makaranta yasa hajiya ta kasa kunne taji shigowan jikokin nata da take zaman jiran tsamanin su tunda safe.
Ba afi min ashrin ba ta fara tsinkayo hayaniyar su daga kofan shigowa gidan tace a ranta nasan a rina dama tabbas hashe na ya tabbata ke nan wanan yarinyar har takai can.
Yaran suka shigo dakin da murnan su don anan kawai suke samu su sake suyi yadda suke so batare da wani tsangwama ba.
Suna shiga Affan ya cire rigan jikin shi ya rage daga shi sai singlet yana fadin hajiya maman mu tace muzo nan muci abinci a wurin ki wai yau bata son damuwa.
Yar ta Aisha ta kwala wa kira tazo ta basu abinci sai gata ta fito daga daki tana saye da dogon riga a jikin ta tana ganin yaran tace a a su Affan ne yau da rana tsaka anan zakuci abincin rana ke nan ?
Hajiya tace zuba masu Abinci don Allah ki kawo masu nan ta wuce kitchen cika umurnin mahaifiyar nata da sauri sai gata dauke da plate din abinci ta kawo masu.
Hajiya na zaune gefe ta kurawa yaran ido tana kallon yadda suke cin abincin gwanin ban tausayi dasu tunane tayi aranta da yau babu ita fa kamar yadda babu ran kakarsu ta wajen uwa yaya Fatima zatayi da wanan ukuban haka ?
Hajiya kubura da take matse ita tunda rana sai gata ta shigo wurin hajiyan da mamaki a fuskanta tana fadin yaya kin ga hasashen yana son ya tabbata a kan yarinyar nan ko sai ga hajiya karima uwargidan su tashigo a bayan su tace tabbas maganan mu ya zama gaskiya.
Ya tabbata ke nan ta ki bari yarinyar nan ta girka abinda zasuci a gidan abin har ya tashi ga ta hana mai aiki yi masu girki suci ya koma ta hana masu abinci.
Sallama ake daga kofan shigowa dayar yarinyar gidan ta leko daga kofan hajiya karima tana fadin sannu da zuwa yaya Suraj.
Bai amsa mata gaisuwa ba sai tambaya yayi ba kowa a gidan ne ina sallama gidan shiru tace suna dakin hajiya mama ina gani can yanufa dakin don yasan idan sunyi irin wanan taron akwai abinda ke faruwa da ya shafi dayan su ne don don iyayyen nasu nada hadin kao sosai a gidan.
In ka debe ko wanan ya kasance amaryan su Asiya bata gida ne a lokacin da su hudu zasu hade a dakin kofan ya nufa yana saye cikin uniform din shi na sojoji.
Sallama yayi a bakin kofan daga ciki suka amsa mashi mahaifiyar shi hajiya karima tace kamar muryan suraj nake ji a kofa yace nine ummi.
Dakin ya shiga kallo daya yayiwa iyayyen nashi alokaci guda ya gane akwai wani matsalan da suke fuskanta wanda ya shafi hajiya mama a gidan.
Gaida su ya fara yi a cikin ladabi kamar ba soja ya samu wuri ya zauna bayan sun karba mai gaisuwa.
Duban hajiya kubura yayi yace mommy akwai matsalane su Affan dake cin abincin su hankali kwance ta nuna mai tana fadin wanan fitinaniyar matar uban tasu ce kila ta rufe dakin girkin gidan ne yau ko da safe a nan suka dauki abincin zuwa makaranta.
Yanzun kuma kaga uwarsu ta turo su nan su da sauri yace ita Fatin fa may zataci to ya tamnaya yana kallon fuskokin su gason jin amsan su.
Mommy tace ai shi muke tunane a nan dafe kai yayi yace wanan mata ban san abinda take nufi ba a gidan nan tana son mayar muna da dan uwa binan.
Kada kaga laifin ta ai shine mai babban laifi mama ta fadi a hasale sai mummy tace ba yin kanshi bane yaya bar irin shuuman matan nan wallahi.
Suraj ya mike a hasale yana fadin yau sai naci mata mutunci idan haka gaskiya ne wallahi ko a gidan maza ana ma mutum horo da yunwa ne balle gidan brother za a ce anyiwa mutum haka.
Ko maigadin gida ai yana iya kyauta da abinci tunda bai rasa ba balle diyan shi ummi ta kalle shi lokacin da yake shirin fita daga dakin tana fadin ina zaka ?
Kai tsaye yace gidan zanje wallahi idan na samu gaskiya ne yau sai tabar gidan nan wallahi ummi tayi saurin cewa dashi kaifa mahaukaci ne na sani a dai karbe key din ka bude wurin shike nan.
Kasan yadda dan uwanka ke son ta hakan zai iya kawo matsala a tsakanin ku yace wallahi sai dai ya kawo ummi wanan wani irin bakin haline haka ?
Ai haka suke mommy tace mashi abinda ake mai gudu ke jan tun farko bai gane ba basu son kowa sai kan su da yan uwan su kawai wanan halin su ba wai ba.
Mama dai ta rike goshin tada hannun ta sai wanda duk yai magana cikin su ta bishi da ido kawai shine nata yayin da zuciyar ta ke mata soya a ciki tana jin wani irin ba dadi a ranta.
Yana tsaye daga kofa mommy tace bari muje tare dakai zaifi da sauri ummi tace haka zaifi kan don wanan kin san mahaukaci ne ya shawo Alluran shi ja sojoji kar yaje ya sauke wa yar mutane a kai.
Ai da zai sauke din haka zai fi gani take duk ta gama da kowa a gidan babu wanda bata iya takawa shiyasa take abinda taga dama inji mama.
Yanzun dai bari mu tafi idan munje ni zan fara shiga wuri ta inji ba asin yin hakan da tayi sai asan abinyi sukace yayi kyau hakan mikewa tayi zuwa dakin ta ta dauko hijjib din ta ta saka suka fice da suraj din a motar shi suka karasa gidan.
Daidai lokacin Abba ya dawo shi da anty amarya daga asibiti da dan ta da bai da lafiya ganin motar suraj ya gilma ya nufi gidan dan uwan nashi yasa suke mamaki.
Anty amarya ke fadin yau suraj ziyara zaikai gidan Abdul ne haka mahaifin nasu yace kila yazo ya samu Fati ta koma dakin ta ne zai dubuta.
Sai da suka shiga gidan ne suke jin abinda ke faruwa karban key anty Amraya tayi bata shiga dakin taba ta bar yaron wirin uwar gidan nata ta mara masu baya.
Sun samu kofar gidan a rufe wai taba maigadi sallahu cewa kada ya bari kowa ya shigo gidan ya damay ta don yanzu ta dawo da yarta daga makaranta zasu huta.
Da kyat ya bude masu kofa sai da suraj yayi mashi jan ido wanan abin shiya kara harzuka suraj din rashi ya baci sosai kusan a tare suka shiga gidan da anty amarya don samun delay din shiga da sukayi.
Bin gidan Suraj yayi da kallo daga sama har kasa kafin ya karasa fitowa daga motar shi cikin hasala mommy tace ashe kun dawo ke nan take cewa anty amarya tace mun dawo ina shiga ake fada min abinda ke faruwa nace barin biyo ku don ba mutunci ne da ita ba.
Anty tasan ida take rashin mutunci ta ai nika yau idan tayi min wallahi balbalata zanyi in daki banza sai dai mu rufe da mijin ta ai mun saba.
A tare suka shiga gida jin karan bude get din gida ta fito a fusace tana fadin maigadi wani dan bura, uba kabudewa, , , , , ganin su mommy yasa tayi shiru ta juya da saurin tana zaton basu ganta ba suko sun ganta.
Kafin su iso ta wuce part din ta ko da sauri don tasan ba bakin ta bane na Fati ne don ita suke zuwa gidan su .
Tunda ta sallamay sallah la,asar take zaune saman sallaya ta tun tana addua ta koma tunane ga tunanen ya bowayeta don yunwan da ke cin ta.
Sun shiga da sallaman su aka gaisu tace mommy kune tafe ashe mune fati har kasa takai tana kara gaida su cikin mutunci suka amsa mata ta dago tana fadin yaya Suraj marmari daga nesa.
Ke kin ci abinci yau ko baki ci tambayan da ya jefo mata ke nan a lokaci daya tayi murmushi tace kajika da wani magana kuma ba a gida ka samay ni ba zakai min wanan tambaya haka ?
Mommy tace Fati ba tambaya muka zo yi ba don mun san abinda ke wakana a gidan ko yau dai bakici komai ba tunda garin Allah ya waye haka ne ko ba haka ba.
Kai ta sadda kasa tace hakane mommy tace to akan may Fati zaki zauna ana maki horo da yunwa dake da diyan ko haka abincin nan akwaishi ba babuba kuma.
Mommy yau fitina take ji tun jiya data dawo ta samu na dawo gidan ta fada min bakaken magana har tana ikirarin sai na rami ya fini shan iska a gidan nan.
Shine yau da safe zan shiga kitchen na samu ta kulle komai tunda asuba wai kada a dora girki a gidan ta fadawa Laraba ni kuma ban koma ta kanta ba tunda nasan don ni tayi hakana.
Haba Fati sai ki zauna da yunwa ai zaki kashe kanki ne idan kina haka yanzu bari muje mu samay ta muji may take nufi wai.
Suraj bai bisu ba ya dan tsaya ganin Fati din yana kuma tambayan ta may zataci yaje ya sayo mata tace duk abinda ta samu yace kayan tea fa tace suna store acen muke ajewa fita ya yi ya mara masu baya.
Sun shiga da sallama cikin isa ta karba masu sai suka tsaya gaisawa da ita tunda iyayye ne su bayan gama gaisuwan mommy tace munzo ne dama muji dalilin rufe kitchen da tsore din gidan da akayi wa mutanen gidan.
Hajiya nan fa gida na ne ina da daman da zan rufe ko ina nake son don Abdul bai bar abinci da Fati a gidan nan ba tunda bai cata dawo ba ta dowo don haka sai ta jira idan ya dawo ya bata abinci ita da diyan ta suci.
Karya kike yi munafukar Allah kuma baki isa ba wallahi muryan Suraj ne da batayi tsamani ba ya fado dakin yana zazzare mata ido a cikin hasala yake magana yana huci.
Tare da daka mata tsayawa yana fadin ban makulin nan tun ban balbalaki yanzu a wurin nan in kuma sa sojoji suzo su kwashe ki sukaiki barikin mu su daure har ranan da miji ku ya dawo inji shiku idan shiya ai horo da yunwa haka.
Kallo da tayi wa Suraj raga fuskan nan nashi ba imani a cikin sa zai iya aikata abinda yace a kanta tsoran ta Allah tsoran ta soja da sauri ta mike ta shige dakin ta yabi ta da harara.
Yadawo da fuskan shi kan yar ta dake cin abincin da tayo masu take away a hanyan dawowanta gida ya watsa ma yarinyar harara da sauri ta noke kanta kasa ta kasa cin abincin da tun shigowan su dacin abincin ta take yi bata ko gaida su ba.
Da sauri tafito daga dakin dauke da key din a hannun ta tana mika mashi cikin ladabi ya fisge a hannun ta har ya fara tafiya su mommy zasu bishi sai kuma ya juyo yana fadin.
Ina ne kitchen din da tsore suke ki taso muje yau za a yi ta ta kare and idan bayan tafiya ko harara naji kin ma yar uwa wallahi yau ba ubanda zai hanani daureki a garin nan jiki na rawa ta bi bayan shi zuwa tsore din yace ta bude da kanta ta bude.
Laraba da mai masu aikin gida namiji da ta dauko dan kabilar su can garin su wanda ya zama kamar CID din ta ga komi a gidan ko tana nan ko bata nan ya kira.
Komai na tsore din aka fito dashi waje aka kasa uku yace Fati ta kwashi kashi biyu ita da diyan ta kashi daya ta dauka nata ne.
Ga abin magana ba halin yi don tsoron soja da ke zuciyan ta tun da zasu shigo Nigeria sojoji suka latsu a hanya take tsoran soja inda duk ta ganshi.
Yana tsaye a rike kunkurun shi da hannayen shi biyu yake tambayan fati akwai wani tsore da kitchen a gidan tace eh akwaishi a part din ta wanan nata ne ita fatin suke amfani dashi in generar.
Kwashi naki kikai part din ki da sauri taja wani kwali da kyat tana fadin kasiye dauko mun sauran ta matsu tabar wiein wanan dan banzan soja mara hankali dake gabanta.
Dama tun zuwan ta gida da ta fara ganin shi aka nuna mashi ita a matsayin sabuwar matar wan shi bai yi murna da ganin ta ba a fili ya nuna hakan kowa ya gani.
Don shi kyamar irin su yake yi bai dauke su wasu cikakkun mutane ba a idon shi, yafi daukan mayaudara aduk inda ya gasu haka yake kallon su a yatsune.
Shine dan uwan shi ja jini ya auro ya kawo ta cikin zurian su take juya mutane yadda ta ga dama a gidan da takaicin ta ya juya tafi bai shiga gidan nasu ba a lokacin mommy tare da anty Amarya suka koma gida bayan sun yiwa Fati nasiha kadan.
Nan suka tafi suka bar Fati da tsoro a zuciyar ta fam sai dai abinda bata sani ba a halin yanzu Nafisa tafita shiga tashin hankali don tsoranta Allah tsoron ta Suraj soja.
Wanda ta hango mugunta zalla cikin kwanyan idon shi abinda ya fadi tasan karamin aikin soja ne yayi shi ya aiwatar da abinda ya fada din dole ga magana nacin ta da zata fadawa Fati a yau sai dai babu halin yin hakan gare ta dole ta kawo ido ta saka mata a gidan tana jiran dawowan mijin nasu wanda zata sa ya ci fuskan Fati din a gidan.
Ai idan sun san wata basu san wata da makirici zataci galaban su gaba daya don ta gane yan uwan mijin da iyayyen shi duk munafukai ne a kanta.
Can gidan su hajiya sun koma kumshe da dariya a cikin su sai da suka shiga mota suka fara dariyan abinda suraj din yayi wa Nafisa .
Yanzu sun gano takon ta Suraj ne zai dinga mata hukunci irin nasu na sojoji na rashin imani sun shiga gida nan suke bada labarin abinda ya wakana a gidan.
Mama taji dadin har cikin ranta ko banza Suraj ya kwantarwa Fati incin ta yau wanda inba shi din ba, ba wanda ya isa yayi haka a zauna lafiya da ita tunda tayi niya.
Maganan mommy ne ya dakatar da ita da taji abinda Nafisan ke fadi a lokacin shigan su gida da take fadin wai babu rabon su Fati da yayan ta ga abinda maigidan ya bari a gidan.
Lalaima wanan matar tantiriya danta ya dauko mata ba kwai ba donge amma har take ikirarin cewa wai ba abincin su a gidan.
Wani zafi na bakin ciki irin wanda iyayye ke ji a gamay da diyan su idan sun yi abu ba daidai a cikin alumma wanda sai uwa ko mahaifi suka san da irin zafin da mama taji a lokacin.
Haka dai ta shige daki a dadafe bakin ciki da takaicin da matan dan nata ke kumsa mata a zuciyar ta yayi yawa kuma dan nata ya sani amma bai iya daukan wani mataki akan hakan.
Wunin ranan haka suka kare shi da maganan Nafisa wanda hakan ba bakon abu bane agurin anyi sau tari da yawa sai dai na yau din ya banbanta da sauri don ta fito ta nuna masu karfin iko da izan da take dashi a cikin kan dan nasu .
Wanda suka haifa suka tarbiyartar da hannun su kuma ya tashi da tarbiya suke saka ran samun farin ciki a wurin shi kamar yadda duk wasu iyayyen ke fata ga diyan su idan su samu
Amma lokaci guda Nasifa ta shiga rayuwan dan nasu wanda ya watsar da duk wani rayuwan farin ciki da suke hasashen samu daga gare shi.
Gashi a yanzu yana a cikin ganiyan samun duniyan shi wanda bai zauna ba tsaye yake wurin neman na kanshi a rayuwan wanda ba komai yakawo hakan ba sai addun mahaifa da