Showing 87001 words to 90000 words out of 142410 words

Chapter 30 - MIJIN BUZUWA COMPLETE

Start ads

08 Aug 2025

34

Middle Ads

gari kawai kana barnan man motar ka.
Haka kika dauki fitan namu dama nace hakane mana tunda ba wani guri muke zuwa ba.
Ke ce baki fahinci muhinmancin fitar namu ba kila amma ni yana da ma,ana masu yawa a gare ni matuka khadija.
Don kasan cewan mu a tare you have change me now na fahinci su abubuwa da dama da ban taba fuskantar su ba a baya.
Maganan gaskiya yau kin dawo min da farin ciki rayuwana har iyayyena sun zo gida da sunan kwana biyu a wuri na.
Da sauri nace cikin murna wai da gaske kake yi yace kwarai kuwa deeda don yanzu haka mommy da gwagona iyan bawa na gida maganan nan da muke yi dake.
Taya kike ganin bazan maki godiya a wanan kangin da nake ganin kin fitar dani wanda a da nake dauka da shirmay irin naki na yara kike yi.
Sun kuyar da kai nayi kasa ina tunane hankalina yayi nisa bani jin abinda yake fadi tsoro na daya ne kada mommy tasan ina tare dashi ta fasara haduwan mu a wata manufa.
Ban sauri maganan shi ba na katse shi da fadin zan roke don Allah kada ka bari mommy tasan kana zuwa inda nake don bansan da wani ido zan kallesu ba har hajiyan ka.
Ya lura da irin rudewan da na shiga sai dai baice min komai ba ganin bai yi magana ba yasa nace please yaya Abdulsamad ka boye wanan a matsayin siri a tsakanin mu don Allah.
Kallo na yayi ya sauke murmushi yace saboda may kike son kada su san ina tare dake nace dashi wayyo Allah kana son su dauke ni yar cin amana ne ko may ?
Cikin sanyi murya nace kasan su ba zasu gane mutunci ke tsakanin mu ba sai su dauka muna tare da wani manufan da bashi ba.
Hakan kuma yana nufi na ci amanan su ke nan gama yadda suke son Fatin ka a gidan yanzu kuma sai su gan mu tare yaya kake ganin zasu dauki abin.
Kai tsaye yace zasufi kowa farin cikin da hakan na sani tunda sun san ki sun san halin ki zasu yi farin ciki da hakan.
Daga yau magana ya kare ba sauran wani abu a tsakanin mu tunda bukatar mu ya biya ka shirya tsakanin ka da yan uwan ka.
Mamaki magana na ya bashi yace juyo yana kallo na sai can yace ai deal namu bai kare ba tukun ko kin manta baki karasa aikin ki ba akan fati ?
Na amsa da fafin kwarai bamu kai nan ba cikin takaici nace wana kuma yanzu ya rage gare ka sai kasan yadda ka shirya da matarka.
Ba wani sauran magana yanzu a tsakanin mu kuma na fada cikin tsiwa ya juyo da kyau ya kalle ni yace don mommy tazo duk kike fadan wanan magana ko may.
No ba don tazo ba in ma don tazo din ne haka ne bana son su dauki abinda wani fassarane kawai.
Ya zura min idon sa yana kallin yadda duk na rude yace a ranshi ashe karyan rashi kunya nakeyi a da gashi yanzu daga jin mommy tazo duk na bi na birkice lokaci daya.
Motar tayi tsit kowa da abinda yake tunane a ran shi sai da ya shafa kan shi naji yace relax deeda wace dake mommy zata san da wanan maganan dake tsakani mu wai ?
Wata zuciyane ta bashi shawaran ya min wayau kawai don yadda na rikece din nan daga jin mommy tazo zai iya sa komai ya faru idan ya biye min.
Kawar da zancen yayi da fadin zuwa nayi ki ban shawara yaya zan yi da Nafisa don batai farin ciki da zuwan nasu ba yanzu haka.
Da sauri na dago kai na kalle shi da idona da suka sauya kala nace baka fada mata zancen zuwan su bane dama , ?
Kai ya girgiza min yace ban fada mata zasu zo ba tunda ba itace ta aje ni ba yan uwan ta dake zuwa ai ba fada min take yi ba itama.
Kada kaga laifinta a yanzu don kai kai sake har haka ya kasance tun farko saboda tsoron ta da kake nuna kanayi da farko.
Ba tsoran ta nake yi ba deeda kaunane kawai na tsakanin miji da mata wanda ita ta dauka tsoron tane yasa nake mata hakan.
Sai yanzun kasan da wanan yana iya faruwa ka manta a lokacin da take saka abu kana mata shi koda kuwa baka son abin ?
Ya gyara zama yana fadin shine babban kuskure dana tabka a farko wanda nake nadaman yi shi a yanzu haka.
Duk abinda zakayi ko zatayi kada ka bari rainin matarka yakai ga iyayyen ka don ko zaka iya canza mata amma ba zamu iya canza iyayye ba.
Wai ke wake koya maki wanan hikimar haka nr ya tambaya cikin son in bashi amsa nace baka son maganan ke nan.
Yace No idan ban so ai ba zan fada maki zuciyana na ba a yanzu don da zuwan su abinda tayi masu yaci min rai sosai ba zan boye maki ba don yanzu ke ce abokiyar shawarata shiyasa nazo maki da zancen.
Yaya zanyi khadija ina son in fita daga cikin dana shiga a bayane gida na yanzu bana son su mommy su fahinci sakaci na a gida na.
Nace na yaushe kuma saidai kada a kara muma makwabta ku mun sanni balle su mommy dake gidan tare ku.
Ina son mata na khadija shiyasa har haka ya faru da ni kallon shi nake cikin mamakin kalamin shi na wai yana son matan shi da yace.
Shin shi wani iriin mutum ne wai nace nafisa dai kake so amma baka son fati kowa ma yasan da hakan ?
Haka kuke tunane ya fadi cikin zafin zuciya amma ita ai tasan ina sonta halin ta ne kawai baizo daya da nawa ba shine matsalan mu.
Kalon shi nake sororo kamar na samu tv da alama yarasa yaya zaiyi da damywar shi ne ya tsinci kanshi cikin fada min sirin zuciyar a matsayi shi na mutum mai shekaru kamar shi.
Tausayi ya bani don na fuskanci bayan Yusuf da suke tare baida wani wanda zai fada ma zuciyan shi ya fahince shi shiyasa yazo gare ni.
Nace wallahi rayuwan ka na cikin hadari ya kamata ka koma ga Allah kayi abinda Allah yace shine kawai mafita a gare ka.
Lokaci ya duba yace zai tafi lokacin sallah ya gabato zai dawo gobe tunda ba school mu karasa tataunawa mukai sallama ya tafi ya barni cike da tausayi shi.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU2️⃣4️⃣Gidan ya nufa kai tsaye tare da sayayyan da yayiwa bakin shi na abubuwan bukatun su ya nufi part din fati dashi.
Babu kowa a falon sai yake mamaki yau ina mutanen gidan su shiga haka duk da basu ciki hakan bai hana falon nashi jin tashin yanayin da jikin su ke dashi ba a falon.
Hakana har ya isa gurin su mommy zuciyar shi cike da tambaya da tunane ya samay su a zaune suna hira yarinyar da suka zo da ita tana cin abinci.
Sai da ya aje kayan a gaban mommy ya zauna lokacin ya fara gaida su suna kara mashi yaya sula samay su yace mummy lafiya sai hamdala.
Nan dai ya zauna dasu suka dan taba hira har wani lokaci sai ga Nafisa ta biyu shi har dakin dags kofa ta tsaya ta kira sunan shi.
Bayan ya amsa kamar ba zai tashi ba sai kuma ya mike ya tafi sude su mommy kala basu ce ba suna kallon ikon Allah kawai.
Ya fito ya samay ta zaune falo tana ganin shi ta mike da kyat ta fara fadin muje sama ina da magana dakai ne ta juya ta fara tafiya yana biye da ita a bayan shi.
Ko da suka hau sama bai tsaya bin ta nata ba don har ta juyo da nufin tayi mai abinda ta kulla a ranta sai hango shi tayi yana bude kofan dakin shi kai tsaye.
Ido ta bishi dashi tana fadin samad maganar nakira ka muyi zaka shige kuma yace baki san dakina bane ko a kan hanya kike son maganan da ni ?
Sai lokacin ta dan juya ta dubu wurin da suke tsaye din sai kuma tayi shiru don ita bata ga komai a nan ba don sunyi magana ai gidan su ne.
Dakin ta samay shi tsaye yana rage kaya a jikin shi ta fado dakin babu ko sallama ya dan juyo ta kalle ta ya kawar da kanshi gefe yaci gaba da abinda yake yi.
Bayan shi ta tsaya tana kama baya tare da fadin Samad wai may wanan mutane suka zo yi ne a gidan nan ?
Yaushe zasu koma don ban son sa ido da takura a gida na sai da ya gama cire kayan ya rage daga shi sai boxes a jikin shi yace cikin duban ta ina fatan wa yan nan mutanen da nace su bar min gida na yau sun bari ?
Tsaye tayi sororo tans kallon shi ta shige ban daki ya barta a wuri tsaye tana mamakin yau wai itace samad ke ba amsa haka daidai da nata tambayan.
Da dane da yanzu ya fara matairaice mata yana bata hakkuri akan zuwan su mommy din itako tana cika tana batsewa tare da kafa mashi sharudda dole ya bi ya juye mata makudden kudi yana lalashin ta.
Yanzu ko da yake kokarin kwato kanshi daga sherin ta sai take ganin wasu ne suke kokarin bata mata aikin ta ta baya.
Tunda ya shiga bayin taja kafanta ta zuwa bakin gadon dakin ta zauna tare da tin tagumi don ta fahinci ba maganar da zatai sanyi bane dashi sai da yanzu cikas din ta shine cikin da ke jikin ta don bai bari tayi yadda take so sam.
Da mamaki samun ta wurin yake kallon ta da ya fito daga ban dakin don yayi zaton tuni ta tafi dakin ta ta kwanta sai ganin ta yayi zaune cikin damuwa.
Samad wai may kake nufi danine yanzu da ke tsiro da wasu halaiya na daban da ban san ka da su ba a da don may zakace sai na sallami yan uwa na gidan nan ?
Yace saboda ba gidan yar uwasu bace su bari idan kin kaiga naki gidan sai su kwaso gaba dayan su su dawo inda kike ba dai nan gida na ba.
Da bakin ka kake fada min haka Samad yaushe ka tashi ga samad din da na sani mai so na da tausayina da son duk wani abinda nake so a rayuwa na.
Da ke nan Nafisa a lokacin da ban fahinci koke wacece ba amma yanzu da na fahinta yasa kike ganin sauyi daga gare ni haka .
Ban taba yarda da halin ki ba sai yau Nafisa da har mahaifa na zasu zo gida na ki tsare ni kina tambaya na wai yaushe ne zasu koma ?
Alhalin ke ga yan uwan ki nan a gidan sun hana ni shakat dani da gida na ba daman in huta in samu natsuwa a ciki ga dan banzan kazanta da kuka bata min gida dashi ya koma wani iri.
Samad mune kazamai dani da yan uwana kake nufi ko may yanzu ne kasan da kazantan mu din ko may yace da na dauka idan idon ki ya bude zaki daina Nafisa ashe abin ba haka yake ba a gun ki.
Komai ai zaka iya fada a kaina tunda kaga yanzu banda moriya a gareka yadda kake so a da, da kake yawan naci a kaina da banda komai.
Wanan ne tunanen ki ashe kike min yadda kikaga dama bakin ce in dauki matakin da zan dauka ki gani ba ranan to matakin ne yanzu na fara daukar wa kaina.
Su mommy kuma da kika gani nan sun zo gidan nan ke nan harsai kin haihu kinyi arbain zasu koma gida.
Ido ta zaro waje tace ina zasu zauna din yace a inda kika gan su and bari kiji idan naji wani rashin mutunci ya fito daga gare ki zan baki mamaki sosai a gidan nan.
Mamaki ne ko rudewa ya kamata a wanan daren na Abdulsamad wanda take gani karfin haline irin nashi daya iya fada mata wanan magana haka babu ko dar a idon shi.
Bai kara kulata ba ya shiga gyaran jikin shi ya barta zaune a gurin cike da mamakin shi fita yayi ya duba ko an rufe gidan ya samu ko ba a rufe ba shi da kansa yaja kofa ya rufe yasa mashi key.
Washegari mommy da wanan yarinyar da suka zo mai suna Aisha bayan sunyi sallah basu kara kwantawa ba suka fito falon gidan suka gyara tas ta saka turaren wuta dana tsunke a ko ina na gidan.
Take gidan ya dauki kamshi da sanyin Ac kitchen suka koma sai da gaban mommy ya fadi ganin yadda kitchen din yake kamar ba mata ke amfani dashi ba.
Nan kuma suka shiga aiki a kitchen din gyara can gyara nan take kitchen din ya koma na macen da tasan kan ta girki suka dora na abinda zasu ci a gidan.
Sai da suka kusa gamawa ne matan dake gidan jin kamshin girki yasa suka fara fitowa daga dakunan kwanan su daya bayan daya.
Suna lekawa kitchen din suna masu ina kwana don tsaron mutuncin su ga maigidan.
Bayan sun gama girki mommy ta zuba masu nasu taba Aisha nasu ta shige masu dashi ciki tabar saura da mutanen dake gidan zasu ci.
Yanyala ce ta shiga dakin Nafisa take kwarmata mata abinda ke faruwa a gidan da fushi Nafisa ta sauko kasa zuwa kitchen din don taga abinda ke wakana mata a gida.
Komai na gidan neat yake yau ya samu gyaran da ya dace daga bakin su ta shiga kitchen din taga yadda suka gyara komai suka jera shi a inda ya dace.
Fita tayi zuwa sama ta samu Abdulsamad ya gama shirin fita tsab ta fado dakin da fushi tana fadin ban san may kuke nufi ba kaida wa yanda kake fadi wai iyayyen ka ne ?
Ya juyo yana fafin kamar ya fa tace don may zasu zo min gida suna min abinda suka ga dama a ciki suna matsayin baki a gare ni.
May sukai maki ya tambaya cikin bata lokacin shi yana sauraren amsa daga bakin ta tace a hasale yanzu ya dace ace sun shiga kitchen sunyi abinda suke so haka ?
Sai da ya dubeta dakyau yace kada ki manta gidan dan su suka zo suna da ikon yin komai da suke so a gidan nan.
Dansu ko dan ta da sauri ya kalleta yace may kike nufi da wanan maganan naki tace dashi gani nayi itama arziki tazo ci kawai a gidan nan do ba itace ta haife ka ba.
Au dama wanan ne tunanen ki ke nan dama raba daya biyu a gida to bari kiji mommy tankar hajiya mu take gare ni don matar mahaifina ne ita ma kamar hajiyan mu don haka nake daukan su daya.
Yanzu ke baki jin kunya baki tashi kin tare su da abin karyawa ba sun tashi sunyiwa kansu har kike fadan akan haka don baki da kunya ?
Tace ba zan yarda da wanan wuce wurin ba irin nata dama na dade da sanin halin ta tun shigowa na cikin ku do haka kayi saurin taka mata burki a hakan.
You're very stupid ya fada da karfi sai data razana yace kada ki fara kice zaki saka masu ido a gidan nan ko bayan fitana ne don zan saba maki sosai kuwa.
Fita yayi daga dakin ya barta cike da mamaki tana ganin wankin hula zai kai ta dare wai itace samad din ta keyi wa abubuwa haka yanzu.
Lalai duniya na shirin juya mata baya idan batayi da gaske ba tin yanzu dakin ta ta koma ta jawo wayan ta cikin tashin hankali take fada wa madam abinda ke faru da ita.
Sai da ta gama sauraron ta tace Nafisa sai kin hada da hakkuri fa yanzu don ni a gani na akwai ida aiki ki ya samu matsala ko kuma don cikin dake jikin ki ne asiri ya daina kama mijin ki yanzu.
Ina cikin wani hali walahi haka na nufin yan uwan samad zasu dawo gare shi suyi yadda suke so gidan nan ke nan wanda ba zan taba yarda ba sai dai duk abinda zai faru sai dai ta faru.
Madam tace Nafisa kibi sannu fa ba kullun ne ya zama dole mutum yayi nasara ga abinda yake so ba kowa kika gani sai yanayi yana hadawa da hakkuri da kuma kissa bawai ga magani kawai muka dogara ba.
Madam ni abin ne yazo min a bazata wallahi tace yanzun dai ki kwantar da hankalin ki mubi komai a sannu.
Tace na ji amma duk da haka zan nuna masu gidana suka zo ba zan bari suyi min abu gaba gadi ba haka tace kiyi a sannu dai na fada maki.

Shiko

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login