Showing 6001 words to 9000 words out of 142410 words
yawaita ta sadaka akan diya yake bibiyan shi a yanzu.
Don a baya in zata iya tunawa bata da aiki sai yawai ta sadaka fiye da kowa a gidan in anyi magana sai tace ba neman duniya nake wa kaina nemawa na baya nake madogara.
Ga yawan taimakon na kasa da ita tundai idan ance yaro maraya ne sai mama tasan yadda takai alherin ta ga yaron ko ta saka yayan ta suyi mai alheri daga abinda suke dashi na jikin su mai kyau wanda zai farauta ran yaron da za a ba abin.
Don Allah iyayye mata mu kula kada muyi sakaci da wanan dama akan marayu da muke gani zaki iya dafa kan yaro maraye zai ji dadin hakan da kikai mai har a cikin ranshi.
Bawai duka maraye bane zai bukaci taimako wasa ma da dariya a gare su sadaka ce dan abinda zai farauta masu rai sadaka ne Allah ya bamu ikon yi ga maratun dake a kusa damu.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU🧠MIJIN BUZUWA🧠
3️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
NOVEL DIN NAN NA KUDI NE BIYA DARI UKU KO KATIN DARI UKU TA WANAN ACCOUNT DIN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KI KIRA TA WANAN LAYIN 09026931792 KO 08036959257 ASHA KARATU LAFIYA YAN UWA.
Tsaye take gaban mirrow tana gyara rigar da ta sa a jikin ta na tampha wanda akai mata dogon riga dashi mai wani launi kamar jikin damisa brown colour.
Dinkin mai dan kwala sai da wuyan rigan V neck akayishi wanda yasa gaban ta ya fito dakyau daga cikin rigar kasan rigan ma an bude shi free yadda zata iya walla kafafuwan ta ba cikin matsuwa ba.
Turare ta dauka ta feshe jikin ta dashi ta juya ta dauko gyalen ta dake saman godo gefe ta fesa mashi turare ta mayar a hand bag din ta dan kwali ta dauko ta dan daki lokaci tana daurawa take fuskanta ya fito tsonen a jikin mudubin.
Duk wanan shirin da take yi ranta ba dadi don bata son zancen zuwa kaduna a zuciyar ta tafi son tayi rayuwan ta a gidan ubanta dake a cikin garin Minna.
Inda gidan su yake a kwangila road asalin su su hausawa ne zamane na kakan ni ya kawo su garin minna har suka zama yan ainihin gari baza kace su bakin gari bane yanzu don kowa nasu anan aka haifeshi.
Daga wajen gidan wanda irin ginan da can bayane na siminti wani murya ya kirata da fadin Khadija kina makara fa a cikin irin hausan mutane Niger shiba kananci kuma ba hausa pure ba do ya dan hade da surkin harshe.
Muryan Khadija ne ke fadin mama shiri nakeyi gani fitowa yanzu da sauri ta karasa shirin ta jawo dan trolley din da ta sa tufafin ta a ciki tare da rataya handbag din ta a kafada ta fito waje.
Kallon ta mama tayi wace zance a wurin ta khadija ta debo kyau da na saba kafin in ga mahaifin ta farar mace ce doguwa yar kabilan gwarin may kunkele dake a cikin minna din.
Kallon yar nata tayi tace kin fi son ko yaushe kiyi tafiyan marance mama nina fison in shiga da yamma yafi ba wanda yasan zuwan ka sai dai a ganka.
Maimakon tayi haraman tafiya sai ta ja kujera roban dake gefenta ta zauna kallon ta uwar tayi tare da fadin yaya haka kuma ?
Banbara nake jira na aika a sayo dashi zan tafi bana son in mising din shine idan naje ke dai yanzu na gane baki son zuwa wurin yar uwan naki tunda kika girma kika fara karatun jamia .
Ta dan ya motsa fuska mai kama da sallo ko yanga wanda ba haka bane kusan yanayin yan garin ne haka suke maganan su da kamar sallo da yanga tace ni nafison in yi hutu na a gida.
Amma ita ya Amina kullun sai tace sai mutum tafi wurin ta hutu yanzu kuma ba da bane ban son ina missing din gida sosai murmushi kawai uwar tayi don tasan halin yar nata.
Ba ajima ba mahaifinta ya shigo gidan yana ganin ta yace a Khadija an fito ke nan eh baba zan tafi hannu yasa ya fara laluban aljihun shi sai ya fito da dubu biyu ya cire guda ya miko mata.
Kai ta girgiza mai tace baba ka barshi kawai kudin da anty ta turo min zai ishe ni na gadone a daidai lokacin yaron da ta aika ya sawo mata banbara ya iso da leda a hannun shi yana mika mata da canjin karike canjin tana bude ledan ta debo banbaran ta mika mai ta mike tana gyara jakkan ta yaron ya taima ya fita mata da kaya ida ta tare Napep zuwa Abdulsalam garej .
Tana isa saura mutum daya ta biya suka shiga suka kama hanyan garin kaduna yamma lis suka shiga gari lokacin kuma akai hadarin marancen nan da Nafisa ta dawo ta samu Napep din da zai kaita unguwar da yar uwar nata ke aure wanda kusan rabin zaman ta a baya a nan tayi shi sai data girma ta koma gida karutun da take yi Abuja yanzu shine silar mayar da rayuwan Khadija gida Niger state.
Tun ranan da khadija tazo kaduna bata fita ba tana daga daki sai falo indan ta fito ko kuma ta shiga kitchen tayi masu girki a gidan.
Yau da yamma ya Amina ne ke kwala mata kira tana zaune tana cin banbara da tayi worming din shi kamar yanzu akayi shi bai kwana ba.
Ya Amina gani ta fito tana fadi cikin ranshin kallon fuskanta don Allah zo ki shiga gidan su mommy ki karbo min sako tace yanzu in tura a karbo min.
Fuska khadija ta ya motsa tace ni ban shiga ba tunda nazo banje na gaidasu ba Amina tace wai khadija may ke damun ki ne haka ?
Ke a rayuwan ki sam baki son shiga jamma a ban san inda kike dauko wanan rayuwa naki ba haka cikin bacin rai ta juya dauko gyalen ta kayan da tazo dasu garin ta kara sakawa a jikin ta.
Yaran anty nata biyu ta, ta kira su rakata gidan da aka aike ta din fitowan su bakin get din gidan yayi dai da zuwan wata mota a guje ta watso masu ruwan dake kwance a wani dan rami saman hanya.
Cikin bacin rai Khadija ta dago kai tana fadin you are very stupeid bakya gani ne kika watso ma mutane ruwa haka.
Horn kawai Nafisa tayi masu ba tare da ta tsaya khadija tabi motar da hararan takaici tana dan kakabe riganta da ruwan ya dan taba a lokacin.
Raina yayi matukar baci haka muka doshi gidan mutane ina mita wani saurayi dake tafe a bayan mu naji yace yar iskan buzuwan nan ne haka take tuki kamar mahaukaciya wallahi.
Dan juyawa nayi na kalli mai maganan nace sannu yace yawa bata dai zuba maku ruwan sosai ba ko nace kadan ya taba mu inayi har lokacin ina kakaban ruwa a jikina.
Gidan muka shiga wanda har lokacin raina a bace yake da buzuwar da naji saurayin nan yace min da sallama muka shiga gidan.
Wanda sai kawuce kofan falon gidan kabi wani dan siririn hanya da zai sadaka da cikin gidan da muka shiga wanda babban gida na ba yau bane farkon shigana gidan don duk zuwa nayi sai anty ta aike da gidan ina shiga akai akai yanzu tunda na girma bani shiga idan nazo sai da wani dalili.
Sallama mukayi inda kofan uwargidan ne fara isa sai na mama daga can ciki sai kuma wasu biyu dake kallon nasu din na mommy dana anty Amarya ke facing din su.
Hajiya ummi da yaranta nake jiyo hayaniyar su daga kofan part din ta na dan matsa daga kofan dakin ina gaida su dakyat aka amsa min ban tsaya ba na wuce.
Lekowa akayi daga dakin ummi don ganin mai gaidasu din da bai shigo ba bata gane ni ba alokacin har nakai kofan mama shiyasa ban son shiga wanan gidan don yawan dake garesu kuma sai kabi kowa kagaida shi dole don hadin kai irin na matan gidan.
Koda baka gaida mutum ba wanda kaje wurin shi zaice dakai ka ko gaida mutanen gidan sanin haka danayi yasa na fara binsu daga daga ina gaida su.
Dakin mama ma a kofa naja na tsaya ina fadin ina kwana mama ta amsa min daga ciki tana fadin waye shigo mana ciki.
Dole na shiga daga cikin dakin tare da kara gaida ita inda nakai gwiwana duka biyu a kasa irin gaisuwan mu na mutanen Niger.
Daga kuryan dakin ta aka fadin muryan wa nake ji kamar khadija Adamu da sauri mai maganan ta fito falon ida nake wani irin ihu ta sake a lokaci daya tare da kwalawa binta kira tana fadin ga khadija Adamu ashe tana garin nan mukayi maganan ta jiya.
Murmushi nayi ina dagowa daga gaida mama da nake nan suka shiritar dani nace anty ta aiko ni wurin mommy.
Bayan nagaida amaryan su ne na wuce zuwa dakin mommy ta tareni da fara anta mun dade tana jana da hira wanda ni ban iya sake jiki dasu muyi hiran sosai saboda mutunci da girma da nake gani a idona.
Sakon ta dauko min na fita mukai sallama dasu nan suka rakoni suna dan taka min in baki mantaba mai karatu na fada maki a nan kaduna nayi rabin rayuwa na.
Kamar abin tsokana wanan motar dai ne na dazun ta dawo a guje ta kara yin facali da ruwa a take nace wanan wani irin iskanci ne wai haka ?
Har motar ta wuce sai ta dawo baya a hankali zuwa gare mu a lokacin zainab ke fadin Nafisa ce fa ta dawo zai tai muna cin mutunci kila taji zagin da khadija tayi ne.
Gab damu ta tsaya tare da sauke glass din motar wata farar mata nagani ciki tare da wata zaune a gefen mai zaman banza.
Tace wace yar iska ce cikin ku take zagina shiru naji sunyi suna soke kai kasa nan san lokacin da nace mata kece dai yar iskan da baki san darajan mutane ba kika gudu da mota haka a wulkance cikin gari kamar yar koyo.
Ke tafadi a zafafe tana kokarin bude kofan motan da sauri naji su Binta da zainab na fadin yi hakkuri anty bata san ke bace .
Cikin zafin rai nace ke wacece da zaki watsa ma mutane ruwa kice kada ayi maki magana wallahi ko diyar shugaban kasa kike sai nayi maki magana .
Karasa fitowa tayi daga motan tana fadin ke yar gidan uban waye a garin nan take raina ya kara baci nace kedin yar gidan uban waye da baki da tarbiya fada min naki in fada maki nawa.
Fisgan hannu na Zainab keyi ni kuma ina turjewa don ban ga wani kimar ta da suke gani ba idons a lokacin don sam ban da tsoro akan gaskiya na.
Ke yar waye da zaki tsaya kina fada min magana son ranki nace ni yar gidan ubane ke kuma cewa akai titin na gidan ubanki ne da zaki dinga gudu kina watsa ma mutane kura da ruwan titi.
Yadda taga ina yi sai ta tsaya tana kallo na kafin ta mayar da fadan akan su Binta da zainab din tana fadin zamu hadu da kune wallahi don nasan da sanin ku take min hakan.
Nace wai kun san wanan banzan ce da kuka tsaya tana fada maku maganan banza saman hanya haka ?
A harzuke tace nice banza nace an fada maki idan ba banza kike ba may kike zaki tsaya kina ma mutane son raki ke gaki mai kudi ki takamu ki wuce lafiya kin taki banza ko ?
Zaki gane kurenki wallahi wani kallon banza na watsa mata nace sai dai mu gane kuren mu amfada maki don kina da kudi zanji tsoron ki ne ko may kudin ki bai damay ni ba tunda ban taba zuwa wurin ki neman wani abu ba.
Matar da take cikin mota ne taji abin yayi yawa kuma dukkan mu munki bari ta bude mota ta fito tana jan ta tana fadin haba Nafisa zaki tsaya kan wanan karamar mara kunya kuna raba hali a saman hanya ai sai ta ja maki raini ga jama, a.
Kuta tayi ta watsa min harara na mayar mats ta shiga mota tana fadin zaki san kin shiga hurumi na nace inga alheri .
Fisgan mota tayi sai da yayi wani irin kugi suka nufi hanyan cikin gari zainab tace wai Khadija kin san kowacece ita din ?
Wacece kuwa banda kila matar wani ko wata kusan gwaunati shike nan don muna kasa sai ta rena mu Binta ce ta katse ni da fadin matar yayan mi ne kishiyar anty Fati.
Inda motar yabi nabi da kallo nace yanzu wanan matar matar dan uwan ku ne wallahi na dauka irin matan bariki din nan ne masu zaman kasu nima ban san yaya akayi idona ya rufe haka ba naci mata mutunci.
Nan nake fada masu abinda tayi muna da zamu shiga gidan su yanzu kuma ta sake maimaita muna shiyasa raina ya baci don naga kamar da gaiyya tayi hakan amma kuyi hakkuri don Allah.
Binta tace ai mu yau kin muna daidai wallahi don ba karamin dadi naji ba da kikaci mata mutunci nan a gaban mu.
Mun da jima a tsaye dasu karshe mukai sallama muka shige gidajen mu har lokacin ina da zafin matar nan a raina.
Nafisa ko sai fada take kawar ta na bata hakkuri tana fadin ban son ki biye mata ba tunda kinga kannen mijin ki a wurin may yuyuwa tasan ki ke baki santa ba.
Zanyi maganin ta wallahi sai ta rena kanta zata san ba a taba ni a zauna lafiya ko wacci tuwo dani miya ya sha na san dai ba yar gidan uban kowa bane ita.
Su zainab na shiga gidan su suka fara bada labarin arangaman mu da matar yayan nasu nan mutanen gidan suka fito suna sauraren su.
Mommy tace kai amma wanan yarinyar wallahi ta burge ni sosai yau da haka Fati ke daurewa ta mayar mata da martani da abin nata ya rage.
Anty amarya tace ai ba zata iya ba ne don ta riga tasa mata tsoron ta a zuciya kuna ganin a banza ta bar mutane ne haka da kowa ke shayin ta.
Ummi tace kwarai ai irin su ba a banza suke barin gida ba sai sun kama bakin kowa sun daure yadda ba mai iya motsawa a kan su.
Sai lokacin mama tayi magana tace aini wanan yarinyar ta gama shereni wallahi tayi min daidai yanzu zata san in ta daure bakin wasu bata iya daure na wasu.
Nikan da muka shiga gida ya Amina tana daki mika mata sakon nayi a cikin wani dan leda wanda ban san abinda ke ciki ba dakina nakoma na fara rage kayan jikina.
Na mayar da dan riga mai karamin hannu da bujen body hook dana cire sai hula dana dora a kaina kitchen na nufa don dora abincin dare saboda yamma yayi.
Kafin wani lokaci har na kammala na gyara wurin na mayar da kauan da nayi aiki a inda suke daki na kofa nayi wanka kafin a kira sallah na fito na canza kayan jikina.
Kananan kaya na kara sawa a jikina don idan ina gida sune kayan sawa na wayata na jawo ina duba sakon dana samu daga abokaina da muke karatu dasu.
Lokacin sallah yayi na mike na gabatar da sallah ban daga ba sai da na yi har isha,i na nike abin sallah na fito din in ba yaran anty na abinci.
Anty ce ta fito daga dakin kwanan ta muryan ta naji daga baya na tana fadin har kin fito eh kawai nace mata ba tare da na juya ba ina zuba abincin a plate na mika ma yaran dake zaune suna jirana.
Juyowa nayi inda nake tsanmanin take zaune nace in zuba mata abincin yanzu ne kallo na naga tanayi cikin mamaki tambayan da ta jefo min a lokacin ban zaci ji ba.
Khadija may ya hada ki da buzuwa yau kin ko san waye buzu kin san ko matar waye don Allah ki rufa min asiri tunda nake unguwan nan ban taba fada da wani ko wata ba ina jin tsoron rashin tsoran nan naki wallahi.
Kara daure fuska nayi nace ina ruwa da wata buzuwa ko baturiya take ba zan yarda ta wullakantani ba ga banza don tana takama tana da kudi tunda ba kudin ta nace ta bani ba.
Don Allah dai ki bari ban son irin haka ni na dauka kin bar halin nan naki yanzu da kika girma ashe halin na nan baije ko ina ba.
Mijin ta fa na iya sakawa a kore mu a unguwan nan wallahi don suke fada aji yanzu a garin don Allah dai ki bari.
Kamar zan yi magana sai nayi shiru ranan banci abinci ba saboda haushin buzuwan nan dake ci min rai haka na kwana da tunane kala kala a raina.
Hajiya mama haka ranan itama ta kwana tana tunane a ranta kan yadda zatayi da danta akan buzuwan da