Showing 75001 words to 78000 words out of 142410 words
muke iyajin saukar numfashin junan mu a lokacin ka sake ni don Allah wai may kake nufi da nine haka wai ?
Fada min amsan tambayana mubar aurin nan kada masu gadin nan su dauke ni dan iska nace sake ni in fada ma to yace sai kin fada jin irin rikon da yaimin yana kara manna ni a jikin shi nace jarabbabu irin su mana.
Sake ni yayi ya daga bai ce komai ba ya tayar da motar muka bar gurin sai da naga mun hau titin da zai sada mu da hostel din mu hankalina ya kwanta dashi.
Don yadda a lokaci daya naga canjin yanayi a gare shi ya firgitani ainun sai da muka dauki hanyar hostel din yace ki shirya shiga cikin jarababbun mutane daga yanzu.
Ban iya magana ba bukata na shine inga kafata a kasa yanzu a wani shago ya tsaya ya shiga har ya dan dade sai gashi ya fito ina hangen shi tun daga nesa na raya a raina Allah yayi halitan namiji a nan .
Baya ya bude aka saka mai kayan a ciki ya sallami yaron ya shiga muka tafi bakin hostel din mu ya tsaya bai bude motar ba niko a kage nake da in fita daga motar.
Yace zan yi tafiya may yuyuwa baza mu hadu ba sai idan na dawo Allah ya tsare hanya nace dashi tare da kallon shi ya bude min motar.
Kina level nawa yanzu a karatun ki nace two a takaice yace yayi nisa da yawa gaskiya nace ai ni ke yi ba wani ba ban ga amfanin karatun ba a guna amma ai naga su Binta da zainab sunayi suma ?
Wanan matsalar su ne ni nawa matsalar na sani bata wani ba su ya shafa wanan bani ba amma kai mugu ne ko ?
Zaki iya ba kan ki amsa idan kin so ko wani kalar nake ya bude min motar tare da miko min ledojin dake bayan motar ina karba na fice ina fadin mugu kawai da karfi.
Girgiza kan shi yayi ya tayar da motar ya tafi sai da ya fara tafiyane tunanen Nafisa ya zo mashi a rai yana tunanen ko ina taje dazun ya dawo bai samay ta a gida ba.
Ya iso gidan ya shiga a falo ya samu su Hadiye zaine suna hira suna ciye ciye gaishe suke da dawowa yace Nafisa ta dawo sukace bata dawo ba ya shige ya barsu a gurin zaune.
Ya shiga ran shi a bace ya dubi lokaci yaga tara da wani abu na dare goma saura kadan wanka ya shiga yana tunanen Nafisa a ranshi har ya fito ya kwanta shiru ba Nafisa.
Ni na fado mashi a rai jarababu irin ku murmushi ya danyi yana rufe idon shi kamshin turen oud dina yake tunowa daya shaka.
Ya lumshe idon shi tare da gyara kwanciyar shi yana lumshe ido yaji dadin kasancewa mu a tare yau hiran da nake mai na buzaye ne ya dawo mashi a rai.
Ba abinda na raga daga halin da yasan Nafisa dashi zai iya cewa kila wani ya fada min kadan daga cikin halinta daya fahinta.
Sai dai abinda ya tuno inda nace suna barin mazan su a gida su zo duniya su auri wani mijin na daban sunayi suna zuwa ziyarar mazan nasu.
May wanan maganan yake nufi kodai shiyasa Nafisa take yawan ziyaran gida akai akai bai sani ba da sauri ya kawar da wanan zancen kada zargi abinda bashi ba yashiga zuciyar shi.
To wai ma ina Nafisa taje ne uban may tafitayi da tun safe har wanan lokacin bai ta dawo ba yaja tsuki yace zan gwada ma Nafisa matsayin ta na mace a gidan nan.
Goma, sha daya shabiyu saura ya mike zubur hankali a tashe ya mike yana zura riga a jikin shi ya sauko zuwa kasa komai na falon a kashe yake .
Su hadiye sun shige dakunan kwanan su kayan da sukaci abinci gurin babu kowa a wurin tsuki yaja ya fita waje ya nufi gurin maigadi yana tambayan shi ko yaushe nafisa tafita a gidan.
Maigadi yace rabon shi da ita tun shekarajiya da kawar ta tazo suka fita komawa yayi ciki yana tunanen tun shekaran jiya da kenan Nafisa dama bata gidan tun lokacin da shima yayi tafiya ko may ?
Kamar zai tayar dasu hadiye ya tambaye su sai kuma ya fasa ya koma ya kwanta suna barin mazan su a gida su je wani guri su kara aure suna yi suna ziyarar su.
Abinda ya fado mashi a rai ke nan karfe daya agogon da ya kalla ya nuna mai da sauri ya mike zaune biyu saura na dare yaji ana buga gidan maigadi ya bude kofa motar ta shigo sai ganin nafisa yayi ta fito daga motar ta dan tsaya suna magana da ta cikin motan.
Ta shigo gidan a gajiye take kafafuwan ta har sun dan kunbura saboda zaman motan da tayi mai tsawo dakin su hadiye ta fara zuwa.
Ta samu suna barcin su hankali kwance ta ta da ita a cikin magagin barci tace kin dawo da yare tace na dawo bata gane komai a guta ba ta juya zata shige tace Alhaji ma ya dawo dazu da safe.
Dam taji gaban ta ya fadi da sauri ta fita zuwa dakinta ta kayan sihirin da ta dawo take kokari boyewa a wardrobe din ta sai taga an kuna wutan dakin ta.
A fusace ta juyo sai ganin Abdulsamad tayi tsaye yana kallon ta da sauri ta kara gare shi sai yayi saurin juyawa ya fice daga dakin .
Boye kayan ta karasa yi ta rufa mai baya ta murda kofan dakin a rufe taji shi gam ta juya zuwa dakin ta ciki da fargaba da tsoro a ranta.
Washe gari ta samay alokacin ya gama shiri zai fita yana daura agogo a hannun shi yana gani ta ya daure fuska tankar bai taba dariya ba a rayuwan shi.
Rudewa tayi tama rasa may ta fada mashi can dai tace Samad kayi hakkuri na san ban kyauta ba na fita ba da sani ka ba.
Jakar laptop din shi ya dauka zai wuce ta zube kasa gaban shi tana fadi ka yafe min gurin buki naje shine naka wanan lokacin ban dawo ba.
Nasan nayi laifi fita in dade baka nan amma kayi hakkuri haka ba zai sake faruwa ba insha Allahu.
Yace don gani saunar na miji ki fita gida na kwana da kwanaki yanzu kizo kice inyi hakkuri haka kai tsaye bayan kin gama yawon gantalin ki a can.
Kin kwaso kafan ki kin dawo min gida ki koma inda kika fito zai fi maki sauki na baki minti awa daya ki fice a gidan nan da kowa naki.
Samad kayi hakkuri ka yafe min ba zan sake ba yace rufa min baki munafuka wace bata san ciwon kan ta da darajan aure.
Ya sure jakkar shi ya fice a dakin da kyat ta iya mikewa tsaye daidai lokacin ya dawo yana fadin fita min daga daki zan rufe abina ne .
Ta bishi da kallon mamaki a kofan tana tsaye ya rufo dakin shi karo na farko a gidan abin ya mata zafi saidai cikin ranta tana fadin yi abin ka a hannu na zaka dawo kwanan nan.
Ya fice ta bishi da kallo tare da juyawa ta wuce zuwa dakin ta tana mai jin haushin shi.
Kutayani da addua yan uwa
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUTunda ya je office ya kasa aiwata komai a office din ga Yusuf bai shigo ba har lokacin ranshi ke kara baci idan ya tuna da kalaman nan daya dana fada shi yafi bata mashi rai ko yaushe.
Shigowan Yusuf office din tun daga nesa ya karanta zuciyar abokin nashi ya karaso gaban tebur din shi yana fadin wani abu ya faru ne na ganka haka.
Tsuki yaja tare da juya kujeran da yake zaune sama yace may ye ma bai faru ba Yusuf wai kasan matar nan bata gida tun ranan da muka tafi kaduna.
Ba ita ta dawo ba sai karfe biyu da wani abu ta shigo gida jiya da sauri Yusuf yace ina taje haka ko da sanin ka ta tafi yace idan na sani abin zai damay ni haka ne ?
Kai wai may yasa wasu matan samun wuri ke sa su wuce limit din su ne na mata akan may mace mai ciki zatayi irin wanan tafiya haka ba tare da sanin mijin ta ba.
Bata tsoron wani abu yaje ya samay ta a can yace ma Yusuf ni ba wanan ne damuwa na ba damuwa na shine ina taje ?
Jiya jiyan nan Khadija taban wani mugun labari wai buzaye sukan baro mazan su na gado su shigo nan suyi auren bugi don kudi ni wanan abin shi abinda ya tsaya min a rai na.
Ita Khadija ta fada ma hakana sosai kuwa jiya muna tare da ita tana zayano min halin buzaye sai naga babu abinda ta rage daga cikin halin Nafisa har ma da wasu da ban sani ba takara min haske akai.
Lalai Khadija jarumar gaske ce tunda har ta tsaya ta iya fahintar dakai wanan abin yace ka san hauka irin nata ita bata dauka maganan ai zaiyi tasiri a raina ba haka.
Yanzu fa har na fara zargin yawan tafiyan Nafisa kasan su akai akai da takeyi tunda gashi har yakai ta fara satan tafiya haka.
Da fa shi yayi yace kada ka zargeta da wanan don ta fadi haka ba lallai ne haka ya zamo gaskiya ba akan Nafisa din sai dai idan wasu sun su suna yin hakan bance a a ba don son kudin su yayi yawa.
Kai ina bazan yar da ba Yusuf ko na yarda da komai ba zan yarda da wanan gantalin da Nafisa ta dauko yi ba dole ne in dauki mataki a kai.
Tunda ta fara haka maganin abin kawai ya kamata kayi don tana ganin ita kadai ke gare ka yasa take abinda taga dama a gidan.
Yanzu zabi biyu shine nake ganin mafita a gare ka na farko walau Fati ta dawo ko nabiyu ka kara aure don ganin da takeyi ita kadai ce yasa take wa yan nan abubuwa haka.
Ido ta kura wa Yusuf dake magana sai da yayi shiru yace Fati ita ta kasa zama saboda rashin hakkurin ta.
Kai ya girgiza mashi yace ka daina fadin Fati bata da hakkuri halin Nafisa dai ya kori Fati gidan ka wanda a lokacin baka ganin haka kai.
Zaka iya bata wani daman a yanzu ko abin zai gyaru a tsakanin ku amma fa sai ka jajirce wa hakan kafin komai ya zama dai dai don Nafisa shuumace ta kwarai.
Ba zata taba bari kuyi zaman lafiya da Fati kawai a gidan ka dole sai da wace mace a tsakani mai kwato mata nata hakkin idan kun cuta mata.
Bai iya magana ba sai jawo file din gaban shi yayi ya fara aiki ba tare da ya san abinda yake yi ba.
Fita yayi ya bar mashi office don yasan halin tunda yayi haka ba amsan maganan shi zai samu ba a lokacin.
Ya kai wani lokaci yana aikin da zuciyar shi raki sakewa don haka ya rufe files din ya mike tare da nufar hanyar fita office din.
Gida ya nufa kai tsaye lokacin sha biyu da wani abu na rana tun daga kofa yake jin tashin sautin wakan yan yaren su cikin harshen buzaci ya karade gidan.
Bai ko kali gefen da suke zaune ba ya hau sama ya shige dakin shi tare da rufo kofan da karfi zuwa yanzu sun fara isan shi a gida.
Mutane haka ba kimsi ko kadan sai bakin ci da ihu yau ma don samun wuri kidan suka sake mai haka a gida anya ma suna wani cikaken ibada kuwa tunanen da yake kenan Nafisa ta turo kofan dakin ta shigo.
Sau daya ya kalle ta ya kawar da kanshi gare ta ta karaso kusa dashi da shi ra tsaya cikin murya da maida hankali gare shi tace lafiya yau kadawo a wanan lokacin haka ?
Kallon ta yayi ya kawar da kan shi gefe daya ta sake cewa magana fa nake maka wai may ke damun ka ne haka ?
Ya dago ido ya sake kallon ta da idanun shi da sukayi jawur yace ban son damuwa a wanan lokacin tace haba mai gida ai wanda duk ya ganka a wanan lokacin yasan akwai damuwa a tare da kai.
Matsalar ki ce ta isheni Nafisa in ma ina da damuwa bai wuce halin ki ba tace halina na kamar yaya wani abin nayi maka ko may ?
Au baki ma san abin da kikai min ba ke nan kike nufi tace don kawai na fita na dade shine zai zama matsala haka ?
Fita nayi kuma gani na dawo lafiya sai may da zaka dauki wanan a babban matsala kuma ko nace ka barni in fita na san ba barina zakayi ba inje inyi lalurar gabana.
Ina kika je har kwana biyu baki gidan nan tayi shiru tana tunanen karyan da zata yi mashi ya yarda da ita a lokacin.
Ya sake tambayan ta sai tace na tafi bukin kawata ce da ta haihu a jos don ko na fada ma ba zaka yarda in tafi ba.
Duban ta yayi cike da zargin ta sannan yace wata kawa kike da ita haka a jos da ban santa ba har zaki iya zuwa ki kwana biyu a bukin ta ?
Ta dan zaro idanu tace dole ne sai ka san kawaye na duka wai yace da kyau Nafisa wanan halin da kika dauko a yanzu sam ba zan dauke su ba .
Tunda har kika iya tafiya na kwanaki don kawai bukin wata kawa taki buki nawa akayi a gidan mu sau nawa kika taba zuwa?
Sam yanzu zuciya ta ta soma zargin ki da aikata wani abu akaina da ba daidai ba sakamakin hurda da matan barikin da kike a yanzu.
Zargina ka fara ne Samad akan may ba zan rage ki ba halayen ki gaba daya yanzu sun gundureni baki zama gida ba yar aiki ba ba wata yar kasuwa ba amma ke kenan kulun yawo fita.
Gaba daya kin shiga rayuwana kin hana min farin ciki kin hana mata na ta zauna dakinta ke kuma ba kula nake samu a gurin ki ba.
Au matar ka kace kace dama matar ka kake son ta dawo kawai kake wanan kamay kamay haka idan zata dawo zaki hana ne ko may ? ,
Ta dube shi a hasale to ta dawo din mu gani mana sai may yadda ta dawo haka zata koma da kafan ta.
Yace haka kika ce tace na fada sai may ?
Baya ya bata batare da ya kara juyawa kanta ba ta tsaya tana ta jidali wai ai dama ta sani zuwa kadunan da yakeyi yanzu saboda fati yake zuwa da yaran shi.
Mamaki yayi sosai da ta iya karfin halin furta hakan lallai yasan ya cuci Fati da yawa ita da tazo daga baya ta iya fadan haka ?
Ina ga Fatin da zaman gidan ya gagare ta da yaranta dole suka bar mata gidan har diyan shi ita ko tana zaune yan uwan ta da yarta a cikin salama.
Lalai ya tabka babban kuskure a rayuwan shi dole kowa nashi ya tsane shi yanzu don sam shi bai taba hango wanan abin ba sai yanzu da taimakon Yusuf da khadija suka ganar dashi gaskiyar hakan.
Ido ya rufe kamar yana barci don bai son hayaniya ko kadan gashi ya jawowa kanshi yar hayaniya a rayuwan shi bai taba nadamar auren nafisa ba sai wanan karo.
Mikewa yayi ya shiga ban daki ya dauro alwala yazo ya tayar da sallah azahar ya gama ya dade zaune a gurin anan wayan Yusuf ya shigo mai yana tambayan shi yana ina ne ?
Yace gida sai ya kashe wayan yasan damuwa ce taimai yawa yasa ya koma gida yasan ko a gidan ba wani sauki zai samu ba, don ko yasan Nafisa ba zata kyale shi ba.
Sai dayayi sallah karfe hudu ya fito daga gidan kai tsaye ya yanke shawaran zuwa guri na don irin shammatan junan da mukeyi yana sashi nishadi a ranshi haka yasa ya nufi inda nake.
Bai faye son zuwa wurina tare da Yusuf ba yanzu don idan sunje tare hiran kan koma tsakani na da Yusuf ne don bai iya sake jiki yayi komai a gaban Yusuf di yanda ya samu dama a zuwan karshe.
Ya iso bakin hostel din sai da ya kare ma gurin kallon yadda mutane suke ta faman shige da fice ya daga waya ya kirani kamar kullun gani kofan hostel din ku yace ya kashe wayan.
Muna zaune girki na gama muna muna ci kiran shi ya shigo min kalon maryam nayi nace wai may wanan mutumin ke nufi ne maryam jiya fa ce min yayi zai yi tafiya ba zamu sake haduwa sai ya dawo yanzun kuma may zo nema nan ?
Dariya tayi tace