Showing 99001 words to 102000 words out of 142410 words

Chapter 34 - MIJIN BUZUWA COMPLETE

Start ads

08 Aug 2025

1021

Middle Ads

bari sai da safe idan zasu wuce su shiga su gaisa da su hajiya mama.

Barci nake bayan na gama mata komai sai na koma in huta can cikin barcin naji muryan Y Amina a kaina tana fadin khadija don Allah tashi ki shiga gidan su mommy ki karbo min lemun tsami.
Na dago idona cike da barci nace haba ya Amina nifa ban son shiga gidan nan har in koma tunda ba dadewa zanyi ba.
Khadija magani zan hada dashi don Allah daure ki shiga ki karbo min dole na daure na mike ta fita daga dakin ta koma falo ta zauna.
Na fito sai take cewa dani wurin hajiya mama zaki karbo min don mommy bata nan tana Abuja gidan Abdulsamad takai wata can an dauka matar shi zata haihu a lokacin suka tafi gashi har yanzu bata haihu ba.
A raina nace ai nafiki sani na fita ina ce mata sai na dawo a gidan sunyi mamakin ganina don basu san da zuwa na ba .
Sai da nabi kowa na gidan na gaida su na nufi dakin hajiya mama nan falon ta na samay ta na zube kasa ina gaida ita take cewa hadija yaushe a garin ?
Nace jiya da safe na shigo nazo duba Ya Amina ce da jiki tace ayyah ai amina taji jiki wallahi haka take cikin ta ita.
Nayi murmushi nace tace in karbo mata lemun tsami a gurin ki ne tace to barin in tashi in duba maki ko akwai saura.
Sallaman su ne ya katse muna magana ta amsawa tare da fadin yaushe kuka shigo garin nan kuma ba labari don da gani anan kuka kwana.
Hajiya jiya muka shigo munje zaria ne gurin kawu salihu sai dare yai muna a can kafin mu dawo cikin fadada murmushi tace toh daga wurin yaya din kuke ashe.
Wuri suka samu suka zauna suka fara gaisawa dasu kaina na duke a kasa na somay da gani du sai bayan sun gama gaisawa ne hajiya ta tuno dani tace Aff.
Kinga khadija na manta dake wallahi zuwan wa yan nan na bazata da sukai muna da sauri suka kallo ni kowan su na mamakin ganina a dakin mahaifiyar tasu.
Mikewa tayi tana fadin khadija ga yayan ku nan wanda ya taba rage maki hanya kwanaki ashe suna hanya suma da kin sani ai dasu kika biyo koda yake kin ce ke shigan safe kikayi.
Ina wuni nace dasu cikin jin kunya ban ko saurari amsar su ba na kawar da kaina gefe ina wasa da yan yatsun hannu na.
Fita tayi zuwa wurin fridge din ta dake waje fitan ta naji muryan Yusuf yana fadin khadija yaushe kika zo garin nan ne ?
Nace don Allah malam ban saku ba ku bari in rabu lafiya da hajiya don kunyar ta nake ji sosai na fada ma wanan aljanna ce wallahi.
Inba ba wanda ya saba dashi ba ba zai dauka shi yayi maganan ba alokacin ban basu amsa ba don na hango hajiya tafe da bakar leda a hannun ta.
Miko min tayi tana zama tana fadin ki gaida min ita da jiki in na samu lokaci zan kara shigowa in duba ta.
Nace to mama an gode na mike da sauri ina barin dakin naji tace yaushe ne zaki koma Abuja ke.
Nace gobe zan koma mama tace ku yaushe ne zaku koma tana tambayan su suka amsa mata da yau insha Allahu.
Ai na dauka sai goben zaku tafi sai ku rage mata hanya nidai na wuce na barsu nan ina sauri in fice gabana na faduwa da ganin su.
Har nayi nisa naji muryan Yusuf a bayana yana fadin yar gidan mama gani fa na biyo bayan ki.
Tsayawa nayi ina jiran karasowan shi inda nake ya iso yana fadin surprise to see you dama ashe kema zaki shigo kaduna baki fada muna ba ?
Yaya tace bata da lafiya nazo duba ta yace gaskiya naji dadi da na ganki nan nace namay fa baka san ina zuwa nan bane dama ?
Yace na sani amma banyi tunanen zuwan ki nan a wanan lokacin bane sai abin ya ban mamaki matuka.
Nace zai shige sai mun hadu idan mun koma yace shike nan amma da wata mota kika zo ne nace motar haya mana ina wucewa nake bashi amsa.
Naba da baya naji yana fadin zamu biyo mu gaida yayar tamu nace basai kun zo ba an gode na shige gidan ya tsaya yana kallon gidan da na shiga.
Abdul ya fito ya samay shi waje yake fadin dama kasan zata zo garin nan ne ita ma ko ta san da zuwan mu ne ta biyo mu.
Murmushi yayi mai yace haka dai Allah ya tsara abinsa nima yanzu na ganta wallahi.
Ina shiga nace dana sani wallahi da ban shiga gidan nan ba yanzu wallahi ina mika mata ledan nake maganan tace saboda may?
Nace wai fa mutanen nan nagani a gida da sauri tace suwa nace su Yusuf da Abdulsamad mana tayi murmushi ta fara bude ledan tace a haka da yawa aiko na gode.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Ido Ya Amina ta bini dashi kaawai na shige daki iya yanzu haushin su su duka nake ji shiru shiru basu zo ba yasa na saki jiki na koma normal life dina a gidan.
Kwana hudu nayi a kaduna na juya na dawo Abuja ban tsaya na sallami kowa ba don dama banda gidan su mommy ban shiga ko ina ba .
Tafiyan marance nayi don ban da kaya a tare dani ba zansha wahalan zuwa hostel ba daga inda na sauka.
Maryam ta tare ni da murna tana fadin wallahi har hankalina ya tashi da naga yau ma har dare baki dawo ba nace na tsaya ne inga yadda jikin nata ya kara sauki.
Ban mata hiran haduwan mu dasu ba itama din bata tambaye ni ba don batayi tsamanin zamu hadu dasu ba a can.

Suna gaisawa da Abba shine Nafisa ta kira shi tana fadin bata jin dadin jikin ta yau tun da ta tashi yace subbahanallahi yanzu zamu taso.
Sun iso sun samu taje asibiti ance haihuwa da sauran lokaci suka dawo gida duk wanan abin su mommy dake gidan basu san wainar da ake toyawa ba a gidan.
Don dama sai taga dama take gaida su da kwana bayan nan zasu wuni basu ganta ba a gidan.
Ga A,A sun ga sauyi a gare shi sosai tun bayan zuwan wanan matar a gidan komai da yake masu na kulawa ya rage a yanzu wani lokaci har fita yake bai gasa dasu ba.
Ya dawo duk da yadda yake ji ya rage jin shi yau direct gurin su mommy ya fara zuwa ya gaisa dasu sukai mai sannu da zuwa tare da tambayan shi mutanen gida.
Ya amsa da suna lafiya suna gaida su ya fito ya nufi part din su kwance ya samu Nafisa tana barci ya dan dade a tsaye kanta yana dubata ya juya zai fita ta falka.
Shima juyowa yayi yana fadin kin tashi tare da zama a kusa da ita yana tambayan ta jikin ta tana wani yamutse fuska take fadin da sauki.
Taje asibiti an dubata ance ba haihuwa bane da sauran lokaci Allah ya sauwaka yayi mata ya mike zai fita tace samad yanzu ya dace katafi kai zaman ka ka kyale ni.
Haba Nafisa jiyane fa nayi tafiyan nan kwana daya nayi a can kawai shine kike fadin na tafi na kyale ki haka ?
Nasan wurin wanan yar iskan matar taka fati kaje ka fake ga wai aiki ne zai kai ka can barin fada maka wallahi baka isa kace zaka wullakantani ba ka dawo da Fati a gidan ba.
Kallon mamaki yake mata yace idan baki yarda Fati ta dawo ba ai zaki yarda wata ta shigo gidan nan ta zauna ko ya fadi a hasale.
Ke baki damuwa da abinda ke gaban ki sai bakin kishi kawai dake cin ki haka har zaki ce wai saboda fati naje kaduna.
Idan ma naje gurin ta ai ba laifi bane don fati matanane kowa yasan ina da hakki a kansu yana fadin haka ya juya ya fice daga dakin.
Bin shi tayi da kallo mamakin shine ya rufe lokaci guda a lokaci daya ya juye mata haka har yana da corrage din bude baki yana fada mata magana son ranshi.
Amma sai ta basar da zance da fadin kila gajiya ne a tare dashi ita kuma ta tare shi da zancen Fati da bai kaunan ayi mashi.

Washe gari na idar da sallah ina zaune wayan Binta Abdulrahim kaunan Abdul samad ya shigo ga wayana.
Na daga in fadin B,A ya kike tace wallahi khadija Adamu baki da kirki yanzu kizo kd ko neman mutane bakya yi in ba mama da ra fada muna yanzu muna maganan ki ba wai kin zo kin shigo har gida mu baki ne may mu ba
Dariya nayi nace Binta Abdulrahim ke nan ni da na shigo gidan ko amsan abu kuma ban dade ba wanan miskilin yayan naku mai jin kai ya shigo na fita.
Ashe kwana biyu kika yi kawai nace hudu dai don jiya na dawo Abuja da dare tace baki da kirki naji nace da ita.
Zamu shigo Abuja idan matar yayan mu ta haihu zan nemay ki ai idan mun shigo kin san mommy na garin gurin shi ai.
Nace Ya Amina ta fada min da nazo kd ai tace kin san yanzu mun dan fara samun kan shi yana dan kula mutane sai dai ba can ba.
Nace da san nu zai kula ku ai watarana tace ai shi nace ma hajiyan mu da ta tayar da hankali kin san shegiyar matace buzuwan nan.
Don su mommy sun je gidan kawai sai ta kule kitchen wai ba zasuyi mata girki a gida ba ki san muguwa wai da yunwa zata hore su kuma ?
Don kawai su bar mata gida tunda bata kaunar ta bude ido taga yan uwan shi sun rabe shi ko kadan nace wanan yayan naku kamar soko yake ai mutum ya zauna haka mace tana juya shi.
Khadija kin fa san buzayen nan yadda suke wurin mallake maza ai ke da gani kin san ba banza tabar shi ba idan munzo dai ai zamu sha kallo don nasan sai an kwasa da ita.
Nace idan haka ne may zai kawo ku kuma ba sai ku zauna gida abinku ba tunda ba dole bane sai anzo din tace kindan haihuwar ta ke nan na farko a gidan shekara shidda da aure sai yanzu ta samu ciki dashi ana ta cin duniya.
Wani abu da ban sani bane na ji ya tsaya min arai nace ku kuka sani ni dai idan kin samu lokaci don Allah ki shiga ki duba min jikin yar uwata don in san halin da take ciki.
Tace insha Allahu zan shiga in duba maki ita nace halan ina Z,A take ko ta fita ne tace gata zaune tana jin mu wai fushi take da ke .
Dariya nayi nace su zainab manya fushi akan may idan batai hankali ba sai na hada ta da buzuwa matar yayan ku ta latsa min ita da kyau.
Tace ai kawar ki ce gaku kuma zaune a gari guda waya sani ma ko kun kulane da ita dariya ne ya kamani sai naji wayan ya mutu nasan kudin ta sun kare ne.
Ita Binta bata jin ta kiraka ta dade kuna hira har sai kudin ta sun kare zata kyale mutum sai kuma tunanen buzuwa ya fado min a rai .
Tsuki naja ina fadin lalle wanan takai shu,uma nan nake ba maryam labari muka zauna nan muka rage mata zunubin ta wurin cin naman ta.
Bayan kwana hudu da dawo wan shi cikin dare ana ruwan sama sosai na kuda ya taso ma Nafisa gadan gadan da kyat ta iya saukowa falo hayaniyar su ne ya tayar da su mommy inda mijin duk ya rude saboda bai taba ganin mace tana labour haka ba sai wanan karon don anty fati haihuwan da tayi duk a gida take haihuwan ta bai nan.
Ganin ga haihuwa yazo mata gadan gadan bata ko iya daga kafa yasa mommu tazo da sauri gurin tana fadin ta duka anan shiko duk ya rude sai fafin yake mommy ku kamata mu kaita mota muje asibiti.
Tace bata iya tafiya Iyan bawa ne tace don Allah mazan su fice su barsu zasu kamata zuwa waje su Yanyala ko komai sun kasa iya sai yare suke sun rude .
Da taimakon Iyan bawa da mommy ta samu ta haifi yarta a gurin kukan yarinyar da ya karade falon ya dawo da hankali wa yanda ke waje suna jiran a fito da ita.
Sai da suka gama komai ne suka ce a shigo daga ciki mommy ta kamata zuwa sama dakin ta ta zaunar da ita a ciki tace tayi wanka sai suje asibiti a dubata.
Shine ya shigo dakin yana gaida ita da yima mommy sannu da fama iyan bawa kuma tayiwa yar wanka bayan an yake ci bi.
Ta fito wanka ya kara dawowa dubata tana zaune ta dubar yar ta da tasha kayan sanyi a jikin ta tana barci don ruwan zafin da iyan bawa ta gasa ta dashi .
Da murmushi dauke a fuskan shi yake fadin baki kwanta kin huta ba har anyi sallah fa tace yanzu dai zan kwanta.
Yace ki dan kwanta idan mommy ta dan huta gari yayi haske sai muje asibiti a duba ku tace ai ko bamuje da mommy ba ga Yanyala nan sai mu tafi da ita.
Mommy dai zamu da ita itada tasan kan komai yanyala mai ta sani yanzu ai kinga ranan dauko su danayi suzo su zauna damu ko ?
Tace ko basu zo ba ai haihuwa dai zanyi yau balle ni kadai na sha wahala na ai ba da wani ba yace yanzu zaki fadi haka amma da kike son taimako ai sunan ta kike kira ta taimaka maki.
Fuska ta daure da alaman bata son magana ya mike yana fadin yanzu dai sai ki huta kafin gari ya kara wayewa mu tafi ya fice daga dakin.
Ranta ne taji ya baci bata so su sa mata hannu ga alamarin ta ba sai gashi haihuwan ma a hannu su mommy tayi shi taja tsuki tana jin haushin yan uwan ta da suka kasa taimaka mata a wanan lokacin.
Taja dogon tsuki tana kwanciya tare da tsurawa yar baby ta idanu tana son gano inda tayi kama da uban ta sai dai don kankantan yarinyar bata gane komai ba a gare ta illa yawan kaman da yarinyar keyi da ita na zubin buzaye.
Shiko yana shiga ya fara kiran yan uwa da abokan arziki yana fada masu karuwan da ya samu .
A ban gare na Binta ce ta fara kirana tana sheda min zancen haihuwan wanda yayi masu daidai don a karshen sati ta haihu don haka zasu samu daman shigowa wurin suna.
Bayan mun gama waya da ita ne na shiga tunane a raina maryam na shigowa nake fada mata zancen haihuwan matar A,A din addua tayi ga yarinyar sai cewa tayi saura muje barka ko ?
Da sauri nace wa ai ni nan da kika ganin ba abu kadan zai kaini gidan nan ba sai ya kama dole balle idan bai kira ya fada min ba ko barka ba zan mai ba, .
Dariya ta dinga yi wai ko ina kishine zai sa ba zan tafi ba nace yanzu idan nace zan tafi gidan shi ke ba zaki min fada ba maryam.
In dai ya samu nayi masa a waya ya gode a watse taro lafiya dai indai wanan yar barikin mata nashi ne in ba a watse da tsiya ba da yan uwan shi.
Nan nake bata labarin da binta ta bani na hana ma su mommy dafa abinci a gidan da sauri tace abincin da muka sayo masu ke nan fa khadija ?
Nace wa ya sanar mata mara mutuncin mata kawai wai kamar mommy zataiwa rashin mutunci irin haka saboda ta samu guri a wurin shi.
Dariyan mumuke maryam take yi nace wanan dariyan fa haka kamar wace taga an cuci wani ?
Ganin bata da niyar dainawa ne yasa nayi banza da ita har tayi ta gaji ita kadai sai bayan kwana biyu ne Yusuf ya kirani yana fada min wai an masu haihuwa.
Nace nako taya ku murna Allah ya raya yasa dadin musulmi ne aka samu yace amin sai dai baki tambaye ni ko wa ya haihu ba koda yake bazaki rasa ji ba a wan gurin.
Wa yasan na san ku da zai fada min an maku haihuwa ni yanzu nake ji a wurin ka Allah ya dada sa albarka ga abinda aka samu .
Amin yace tare da godiya kamar shi akaiwa haihuwan ya tambaye ni jikin anty na nace da sauki na gode mukayi sallama ya kashe wayan.
Wurin gi nayi da wayan gefe na naci gaba da karatun da

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login