Showing 42001 words to 45000 words out of 142410 words

Chapter 15 - MIJIN BUZUWA COMPLETE

Start ads

08 Aug 2025

41

Middle Ads

ma yayi nesa ki gan shi nan ai ni abin har mamaki nake ji wallahi tace don dai kince buzuwa ce matar shi amma da sai in ce wani namiji zai samay ki ya bari ki kufce mashi khadija.
Kyau Allah ya baki tsayi da gashi ga ilimi addini dana boko kin tara ranan da naji kina karatu wallahi har rudewa nayi na raya a raina da naje gida komawa zanyi makaranta ni ma na samu in sauke.
Tun ina karama fa na sauke maryam yanzun haka ban bar karatu ba don ina nan ne bana zuwa amma a gida ban wasa da karatu ko kadan kinga yayata malama ce sosai wallahi.
Tace ai naga alama tun haduwa na dake idan kuna waya da ita zata tana makaranta ko gata tana shiri fita makaranta may yafi wanan dadi ga mace.
Nace kinga mu zama yakawo kakannin mu zama garin minna amma aslin mu yan wani gari ne da ake kira ka,oje tun ana hade da sokoto da Niger yanzun haka mu bamu san gida ba mu filani ne na asali wallahi.
Mahaifiyar mu ce kwarin minna amma saboda zama muka juye muka zama mutanen minna baki sanin mu baki ne idan ba mun fada ma ba.
Haba nature din ki yayi kama sosai da na fulani ashe ma ke ruwan su ne nace ada ke nan ina so zuwa garin mu sosai inga yan uwana wallahi.
Don ance har yanzu yan uwan mu suna garin don daddy din mu shi yasan gari har yakan je lokacin da bai tara iyali haka ba.
Tace ya kamata ku nemi gida su san ku fa nace muna da burin haka nida ya Amina ai sai dai kin san abin sai an shirya ne .

Dakin shi ya nufa ya fara cire kayan shi zuciyar shi yana mai soya yana jin kamar ya ganin a gaban shi ya shake ni don haushi da takaicina da yake ji.
Nafisa ce tazo dakin har lokacin a hasale take daidai ya fito daga wanka ta yi mai wani mugun kallo tace yau sai ka fada min gurin wace kaje har ta dauki wayan ka ta kirani dashi.
Baiyi magana ba sai kokarin saka jallabiyan da yake yi a jikin shi ta karaso tana ce mai wata yar iska yar kasada ke son shiga rayuwan ka Samad ?
Ido kawai ya tsura mata yana kallon ta batare da yayi mata magana ba ta sake maimaita tambayan shi samad ka fada min wa cece kaje wurin ta har ta dauki wayan ka ?
Ta karaso tana rike mai kwalar dogon rigan da ya a jikin shi yanzu kama hannuwan nata yayi ya murde ya wurgata saman goda ya nufi inda turaren shi suke ya dauko yana fesawa jikin shi.
Ta kara juyowa ta nufo shi a hasale tana cewa kunji kun gama iskancin ku shine ka dawo gidana kana min wankan tsarki anan.
Da mamaki yake kallon ta ya bude baki da kyar yace Nafisa yau ni kike wa zargin aikata zina da wata kace tace dole in maka samad may ye hadin ka da wata mace , ?
Yace dani mazanaci da akan ki zan fara tunda dashi kika gabatar min da soyayyan ki farkon haduwan mu dake.
Haushin maganan shi taji sai ko ta haushi da duka da yakusa tana ture shi tsayawa yayi yana kallon ta da mamaki.
Jayeta ya kara yi ya hakadata gefe ya fice daga dakin ta biyo shi tana zagi ta uwa ta uba ya shige dayan dakin ya kyale ta.
Yana shiga wayan shi na kara ya dauka Yusuf ne yake son fada mashi ya gama tsara masu tafiyan da zasuyi kaduna.
Yace sai dai abinda zamu saya wa yaran nake son mu dauko khadija ta zaba muna abinda ya dace dasu tunda mu ba zaben kayan yara muka iya ba.
Yusuf ya ambaci sunan shi a kasalance Yusuf din ya amsa mai yace don Allah ka rabani da wanan yarinyar dake batun tarwatsa min gida da rayuwa na.
Cikin mamaki Yusuf din yace tayi ma wani abune kuma ban sani ba yace may ne ma batai min ba yanzun haka in ka saurara zaka iya jiyo hargowan Nafisa akan khadija.
Da sauri Yusuf din yace dashi kai haba sun hadu ne komai ko ta samu labarin khadija din ne yace basu hadu ba sai dai yau kaddara ya hadasu a wayana.
Nan ya koro mai abinda ya faru yau din dariya sosai Yusuf ya kwashe dashi lokaci guda yace kai khadija akwai jan magana da rashin tsoro.
Yace ni yau taja min masifa da fushin Nafisa a gidan nan ban son wanan bakin kishin na Nafisa wallahi idan ya tashi bataji bata gani imagine wai har ni Nafisa ke ma zargin zina yau.
Intrested ashe yau tasan zaka iya kara aure ko wani lokaci ke nan wow i am impress da jin wanan labarin Allah yasa haka yasa ta fara gyara halin ta.
Rikici kake son jawo min Yusuf da ka hada ni wanan aljanan yarinyar mai shegen rigima wai dole sai itace zatai min wanan aikin ne ?
Kana son mu canza wata ce ya tambaya shi a cikin gatse yace No da sauri yace ta faye matsala ne wallahi.
Yace da matsalan nata za a gyara komai kai dai ka kara hakuri don Allah yace wallahi yarinyar ta fara shiga raina amma kuma ta faye matsala ne ai.
Yanzu yaya zan iya shawo kan Nafisa a gidan nan gaba daya ta birkice min yau kan kishin wace ma bata sani ba har da duka na fa takeyi.
Duka kuma subbahanallahi kai kuma sai kai tsaye tana dukan ka ko mai yace to may zan mata Yusuf kit Yusuf din ya kashe waya alaman yaji haushin maganan abokin nashi.
Dariya ya soma yi bayan ya kashe ma Samad waya yace komai na zuwa yadda nake so da alama samad ya fara son khadija.
Wayana ya kira bayan mun gaisa yake tambayana ashe yau mutumin yazo gurin ki shi kadai nace eh dan matsalan yazo min wai bashi da lafiya.
Sai bayan na taimaka mai da magani yaji sauki ya soma karanta min haukan shi wai na fita mai a motar shi tunbai balbalani ba.
Dariya yayi yace may ya hada ku har haka nace bakin rigima na yasani daukar mai wayan matarshi da take neman shi ganin kamar barci yake wayan nata ruri nikuma sai na dauka.
Dariya yayi sosai a lokacin yace aiko nasan yau suna can suna tafka fitina a tsakanin su kin ja mashi aiki yau
Nace shi ta sha matsoracin namiji kawai wanan ma ko ga maza yan uwan shi nasan matsoracine wallahi dariya Yusuf yayi sosai.
Yace to yanzu na kiraki ne don Allah gobe indan kina free zaki taimaka muna da sayen kayan yaran samad don Friday zamu shiga kaduna insha Allahu.
Nace idan dashi ne gaskiya ba zan tafi ba yace saboda may khadija kefa kika kawo wanan idea din zaki ce kuma bazaki tafi ba.
Ki daure ki karasa ladan ki don Allah ai ba don shi zakiyi ba yaran fa kika dauki alkawarin taimakawa saboda Allah shiru nayi yace may kikace nace a hankali naji sai dai idan ya wuce gobe ba zan samu fita ba don ina da exam talata kuma zan wuce gida.
Yace nagode khadija Allah ya biyaki da alherin sa yadda kike muna Allah ne kadai zai saka miki sai mun hadu goben zamuyi magana Allah ya kai mu nace dashi.
Na kwanta cike da tunane a raina wai dama da gaske akwai mazan da suke irin wanan rayuwan a gidajen su don dai ni nasan mahaifin mu zaki ne a gidan shi akan iyalin shi.
Wai duk gidajen masu kudi haka yake ne rayuwan su sai mata ke juya su yadda suka ga dama idan ka gansu awaje sai kai masu kallon isa da izza amma a gidajen su sai ka raina su.
Yaya matashi kamar Samad zai zauna mace tana juya shi haka yadda take so wai kuma yana sunan miji a gidan shi gashi da ilimi daya dace yayi amfani dashi ako ina ya kama amma mace ta na juya shi son ranta.
Kwafa nayi nace wallahi gobe zasu ga tsiya don sayayya zanyi masu kamar na hauka inta gani ta haukace da tushe.
Washe gari nace ma maryam ta shirya zamu fita da su yaya Samad zasu zo mu muyi wa iyalin shi sayayya tace tau da murnan ta.
Mun shirya tsab don Yusuf ya bugo min waya suna kan hanya zuwa wani dan abu ne ya tsayar dasu yanzu.
Sun iso wayan Yusuf ya shigo min gasu a kofan mu nace gamu tafe yace keda wa khadija nace da kawata maryam zata tayani zaben kayan ne sai kun fito yace min.
Mun fito daga gidan kwanan namu na dalibai muka hango su can nesa kadan inda suka aje motar su muka karaso wurin .
Motar Yusuf ya fito ya bude muna muka shiga ya rufe sai da muka zauna muka fara gaida su wanda nidai kusan Yusuf kawai na gayar maryam ne tace da Samad yaya jikin shi yace cikin daga hannu da sauki.
Sai looacin ciwon kan da yazo dashi jiya ya fado mashi a rai don fitinan da suka kwana sunayi da Nafisa yasa ya manta da komai nashi.
Kawar ki bata magana ne Yusuf ya kawar dashirun da motar yayi a lokacin maryam ne ta bashi amsa da fadin ai itace dai magana ya zama aiki a gare ta nikan ko aku ya ganeni ya kauce min wurin zuba.
Ashe kuna da aiki shi yasa abin yazo maku daidai naji mamakin da kika iya zama da wanan mai zubin yan ruwan dariya ta danyi tana cewa ashe kaima kyaunta na ruda ka haka.
Haka take ruda maza a cikin makarantar dama wajen makarantar amma kunsan may wai duk wanan bata ga may mata ba har yanzu ga kyau yana tafiya a banza a gurin maza.
Tsuki yaja tare da juyowa ya dan watsa mata harara lokacin da take fadin ni wallahi ina son ganin lucky man din zai iya sace zuciyar wanan yar kwalisan yarinyar.
Zaki ko sha zaman jira don maza basu son zuben mace irin wanan da ko ina tabi surar ta na rawa sun fi son mace mai natsuwa da kamala.
Yusuf yace har kin sa yau na fahinci wani abu da kika kawo wanan maganan haka nayi real sign ba karamin kyau ki ga khadija ba da har na kasa fahintar abinda yasa abokina yake yawan rudewa idan ya hadu da khadija ashe kyawon tane yake yawan tsorata shi yana mata kallo mai kama da tsoro but still yanzu da yai maganan nan sai na gane kyauta ne yake yawan ruda shi.
Da na dan shiga rudanin wanan abin amma yanzu maganan nan da kikayi yasani a hanya watau a takaice aboki na yana rudewa idan yaga khadija sai take mashi zubin yan ruwa idan ya kalle ta.
Tayi saurin fadin ya gano sirin da Allah ya boye ne anan ai khadija matar manya ce wallahi duk namijin da yai saa ta kalleshi da manyan idanun nan nata yakan shiga rudu ne ya rasa inda yake ina ga shiya take tsoron fita wallahi.
Don Allah malam idan kun gama kaja mota kakai mu inda zamu ko ka mayar damu inda ka dauko mu zaifi ya fada batare da ya juyo gare shi ba
Yi hakkuri malam abinda na gani na fada yasin khadija ta hadu ba karya a gurin nan kai mai dani inda ka dauko ni ya fada a dake.
Nidai nayi kamar badani suke yi ba kaina yana duke ina danna wayana dake hannu na muna charting da zarah.
Yusuf yace karkai fushi dani abokina gaskiya muka fada anan take a deep breath and confess khadija ta fi matan da kake gani haduwa.
Bude baki yayi ya zaro ido yana kallon yusuf da mamaki kalaman shi dayaji na bazata yasan Yusuf ne kadai duk duniya yake iya fahintar shi lokaci daya.
Yusuf ya sake kallo shi ya dan lagabe kai tare da girgiza mashi kai yace dont give me that look just say yes to your mind she is realy beautiful as you see.
Take ya daure fuskan shi tamau tankar bai taba dariya ba yace Yusuf kayi kuskuren furtan hakan a gare ni don kafi kowa sanin banda lokacin yin hakan .
Nace kunyi babban kuskure Yusuf da kuke son kamanta da wanan mutum matsoraci ko kuna zaton sakewan da nayi daku kun dauke shi da wani manufane ?
Ba so ko wani abu makamancin haka cikin zuciyana don ban taba daukan haka ba a tsakanina dakai sai mutunci da niyar taimakon ka a zuciyata don rayuwan ka na bukatan taimako da agaji ga wanda yasan shi.
Tsakanina daku kuma sai dangantarkar irin na zumunci na an fito wuri daya da biye min da kukeyi da kyautatawa .
Da ka sani da baka dauki haka ba da zafi don zuciyar ka ta baka ba daidai ba me yasa zakayi zaton soyayye zai yuyu a tsakanin mu don kana kyakyawa mai kudi maiji da ilimi da wayewa ko may ?
To ni duk wanan nasaban naka baya burge ni don ni ina fatan samun miji ne wanda yasan kanshi yake iya mulkata ba in mulkeshi ba ko wata tana mulkanshi.
Barin fada maka ban taba jin son ka wallahi a raina don halinka bai mun ba bai kuma taba burgeni ba tausayi ne da fatan alheri ka shirya da iyayyen ka takowani hali .
Don halinka da dabiar ka yanayin rayuwan da ka shiga da komai naka yana bukatan gyara a yanzu.
Ya isa yace da karfi ya fada cikin kuna rai, yayin da maryam tunda na fara magana take rufe min baki waina bar maganan .
Idon shi yayi mai jawur hankalin shi yana neman barin jikin shi zuciyar shi yana son tarwatse mai yace ba laifin ki ba ne.
Yaja wani irin huci ya furzar a bakin shi yace Yusuf ka juya mu sauke su inda ka dauko su don Allah.
Bana son inkara ganin fuskan yarinyar nan na tsane ta wallahi bana son kara haduwa da ita a rayuwa na .
Shiko Yusuf a ranshi ya gigice da fadan mu sosai yana rayawa yaushe ne zai samu cin ma manufar shi a kan mu yaushe zasu bar wanan halin may yasa Samad ke biye mata suna haka kamar wasu yara kanana.
Ya zama mai dole ya shiri mu tun yanzu tun kan mu rabu a hakan ba wani ci gaba gashi ya fara ganin hasken alamarin tun ba a je ko ina ba.
Ya zama dole ya gyara wanan abin tun anan don ba zai yarda abokin nashi yaci gaba da zama haka ba yanzu in ya bari muka watse a hakan abin bayi ba wallahi.
Naji Yusuf din yace Khadija ba nufin abokina ke nan ba baki fahince shi bane tun farko kin san tun jiya fa yana da haushin ki a ranshi don haka don Allah bashi hakkuri ya huce dake haka please.
Yadan juyo yana kashe min ido sai na gane manufarshi da sauri sai da na hade wani bakin ciki na iya furta to kayi hakkuri don Allah ban fahince ka bane na fada a sanyaye.
Da kyau Khadija matar na tuba ko bata laifi komai rintsi ya juya gurin shi yace kayi tsamanin jin hakan daga bakin ta yanzu a yadda tahau din nan.
Wani iri yaji yace a ranshi may yasa na kasa fahintar wanan yarinyar ne wai me yasa na fadi wanan maganganun masu zafi gareta yanzu bayan nasan gaskiya Yusuf suka fada.
Halinta daban ne da na sauran matan dake bina suna ribibin in so su kai tsaye zata iya fada ma gaskiya batare da tsoron komai ba kuma ya amfane ka.
A sanyaye yace Yusuf ban san may yasa take son bata min rai ko da yaushe muka hadu ba zan bata dama taci gaba da min yadda take so ko yaushe.
Motar ta tsaya a bakin wani plaza babba ba wanda yayi magana Yusuf ne yace bissimila mun iso mu shiga mu fito tukun.
Fita mukayi a motan har lokacin jikina a sanyaye nake jin shi don abinda ya faru a motan Yusuf ne yazo daidai inda nake yace khadija na gode da kika fahince ni ba komai nace dashi cikin yake.
Muna shiga shi yana bayan mu yana tako a cikin izza da kamala maryam tazo daidai kunne na tace dan dakata mai ku jera mana.
Hara na aika mata nace sai dai ya mutu idan sai na jera dashi din ya dai ci albarkacin Yusuf da kuma na iyayye wallahi.
Ban garen kayan yara muka nufa inda maryam ta fara duba kayan ina tayata har lokacin ban sake ba nan muka shiga jidan ma yaran kayan sawa da sauran abubwan yara.
Mu koma bangaren takalma da dasu sauran abin bukatan yara harda su tawul da sabule da su kulan zuwa school muka hado dashi a hankali na taka wurin kayan mata na zaba ma anty fati kusan kala goma masu kyau da tsada.
Su dai ido kawai suka saka min har lokacin da muka gama

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login