Showing 135001 words to 138000 words out of 142410 words

Chapter 46 - MIJIN BUZUWA COMPLETE

Start ads

08 Aug 2025

53

Middle Ads

su tafi.
Godiya sosai sukai mashi suna kara min nasiha akan hakkurin aure anan kan dariya saida ya subce min a fuska na.
Bude min baya yayi wai in shi ga naja na tsaya a wuri daya bakin motar tare da fadin kada ka manta na fada ma bazan sake shiga motar ku ba again.
Haba khadija ai ko don idon mutane nan da nayi wa karya ki daure ki shiga ji yadda matan nan ke hada ki da Allah tana fada maki yaji fa baida kyau ga mace .
Wa nayiwa yaji din ai gara su san gaskiya tinda ban san inda zan kara haduwa dasu ba yanzu idan mun rabu don haka please sauke min kaya na in tare wani motar in tafi.
Don gidan mu a motar haya muka saba tafiya tunda bamu da motar yace please kanwa na kada mu tsaya jayayya anan kiyi hakkuri don girman Allah mu tafi yamma keyi yanzu hanyan kuma babu kyau kin sani.
Girman Allah da ya ambata ne yasa na shiga motar ba tare da nayi wani magana ba kuma sanyi da kamshin motar ne suka daki fuska na a lokaci daya.
Kira, a ke tashi a cikin motar a hankali muna shiga sauran motocin suma suka tashi muka kama hanyar kaduna ga yamma yayi.
Sai da muka danyi nisa da tafiya yace kin daiji abinda manyan mata suka fada maki fushi baida kyau khadija don ko wanan tafiyan ya ishe ki ki gane mu da alheri muke bin ki khadija.
Sai yanzu AA yayi magana da cewa ke kina haukane ko rashin sanin ciwon kai ne yakai ki bin motar haya cikin wa yan nan mutane haka masu yawa.
Idan wani abu yaje ya samay ki a cikin jejin nan fa kina son ki salwantar da rayuwan ki ne a banza ko may ?
Tunda ya fara magana ban dago kai na kalle shi ba kaina yana a wayata sai da naji ya fadi hakane na dago kaina nace a tsiwace .
In salwantar da kaina kamar yaya don kawai nabi motar haya zan salwantar da rayuwana yace a zurke yana kallona.
May yakai ki shiga motar haya a wanan hanyar ?
Nace ai kasan ubana tallakane ko banda motar da zan shiga inwa mutane tsiwa asan ina dashi, don banda motar ya wuce ta haya a yanzu don kowa yasan ubana ban kwadayin karaya ko abin wani a rayuwa.
Wani kallo ya watso min daga inda yake zaune ya kada kai ya koma ya zauna yana maida numfashi.
Yusuf ne yace kaunata kin san kowa ke din mai tsada ce a yanzu don Allah kibar wanan gangancin da rayuwan ki murmushi nayi nace ganganci kai nama rasa may zance dasu alokacin.
Gudu suke shararawa da mu sai can ya juyo kamar mai maganar lalama yana fuskantana yace kina jina daga yau duk inda zaki ki buga ma Yusuf waya a turo maki mota bana son shiga irin wa yan nan motocin please I hope you understand me ?
Malam bafa don na shiga motar ku bane yanzu zaisa ka dinga bani commad son ranka ina dai nike da rayuwana bawani ba.
Ya ce haka kika ce nace kwarai kuwa don may zan ka so takura min kamar wani wanda ya ajeni can a gidan shi.
Ya juyo ya kara fuskantana yace haka kike so kiga an adanaki a gida ko sanan zaki bi maganan da ake fada maki na kula da kan ki ?
Nace haka din ne ai shiya na fada haka kawai ba matar aure nake ba zaka wani kafa min doka kamar wace ke karkashin wani.
Yusuf yace kai kanwa ta ba kayau ne haka yasa kikaji ana maki magana kada ki dauki zancen da zafi mana.
Yace barta ai ka santa da bakin tsiya wanan bakin naki ya kai karshen tsiwan sa daga yau zaki kula kisan abin fadawa mutum.
Wai ma may zaki je kaduna a wanan lokacin haka kuna karatu ko kin fara wasa da karatun ki ne yanzu ?
Nace kai wanan ya dama ni gurin yar uwata zanje in dubata karatu kuma nike da abina ba wani ba.
Murmushi yayi yace yarinyar nan ina tausayawa ranan da bakin nan naki zai dinke ya koma shiru wallahi kaina na kawar wanan karon ban biye mashi ba ya koma ya jingina da kujara ya dafe kan shi da hannun shi daya.
Sai Yusuf ne ke dan jana da hira jefi jefi ban bashi amsa sosai sunyi sayayya a hanya sai ba a wani dade ba sai gamu mun shigo garin kadauna garin gwauna.
Lokacin duhun yamma ya fara a yi sosai nace ku sauke ni in karasa a motar haya wani irin kallo ya watso min daga inda yake zaune yace saboda kin saba shiga motar hanya baki mai dashi komai ba ko ?
Koda muka shigo layin mu har an fara kira a wasu wurare na magariba daidai get din gidan Ya Amina Yusuf ya tsaya da motan da muke ciki na fito tare da fadin yayana na gode sai da safe.
Ki gaida sister idan kin shiga kice muna mata yaya jikin kafin mu shigo gaida ita zataji kawai nace dasu na dauki jakata na nufi ciki.
Sai dai may daga get din har ciki a rufe na gansu waya na ciro ina kiran ta har ya katse ba a dauka ba nan dai na sake kira karo na biyu yana gab da katsewa ne aka daga wayan nace.
Ya Amina kina ina nazo gida ban samay ku ba gida a rufe khadija ce nace eh don ba muryan ta naji ba a wayan.
Tace mommy ce Amina tana gidan mu sallah take yi nace ok ina wuni mommy tace lafiya kalau yaya hanya nace Alhamdullahi mommy.
Na kashe wayan don ban son dogon magana da ita nasan dai tunda mommy tasan nazo kamar Ya Amina taji ne na zo din.
Na dan jima a tsaye sai can na hangota da saurin ta tana fadin ke tafiya haka babu sanarwa ashe kina hanya ne ?
Don Allah bude min gida ni fitsari ya damay ni tun a mota nake jin shi wallahi tace kika ki magana a tsaya maki kiyi haka fa na jawo matsala ga mata.
Tsuki nayi lokacin da ta bude gidan na fada da sallama a bakina ban tsaya ba na aje jakka kawai na fada ban daki da sauri.
Har da alwala na dauro kafin in fito na zo falo na tayar da sallah don bata cikin falon a lokacin ban daga gurin ba sai da na gabatar da ishai.
Wayana ake kira na dauka maryam ne take tambaya na yaya hanya kuma mun isa kd din nace mun iso yanzu tace an gyara motar ne nace ina fa ke dai bari maryam.
Muna wurin ana gyara motar ba sai ga dan fitinar ga ba mai shegen izzan tsiya tace wa nace wa kika sani ni wallahi da nasan yau zai shigo kaduna ne da ban zo ba wallahi.
Wai kina nufin su AA wallahi maryam su muna tsaye a jejin nan da na fada maki sai kawai ganin su nayi daga sama kamar a mafalki a gurin.
Fitowa yaya Amina daga dakine yasa nace ma maryam ta bari idan na huta zan kirata muyi magana, muryan Ya Amina ne naji tana tambayana mota ce ta baku wahala a hanya.
Nace bari ya Amina banji dadin wanan tafiya ba yau don dai kawai na kwallafa son ganin ku ne nayi shi dana koma wallahi.
Gashi ko abinci ban tsaya nayi ba na ranane na rage wa yara don mun shiga gidan su mommy kin san ana buki a gidan nace buki kuma ina suka samu buki ?
Tace a, a kin san ai da gidan su da gidan su Fati matar Abdulsamad kamar Family daya ne kannen ita fati din ke aure ai.
A raina nace no warder ashe shi yasa mutanen nan nan suka zo garin ashe buki suke yi gaskiya naga an shake mota da kaya haka ?
May zakici yanzu in dafa maki ko in shiga aurin mommy in karbo maki abinci don ni naci ko acan tun dazu.
Nace barshi ko tea ne zan sha idan na watsa ma jikina ruwa zan kwanta muna wurin zaune muna hira sai mukaji sallama.
Binta ce da zainab da wasu kawayen su biyu da ban san su ba suna dauke da basket din abinci a hannun su.
Da ihu Binta ta karaso inda nake ta rungumay ni tana fadin wallahi khadija Adamu nafi kowa farin cikin zuwan nan naki ko kema dama kin san da zancen bukin ne wai ?
Nace cikin fara,a wallahi bansan da zancen wani buki ba zuwa nayi duban ya Amina na kawai don nayi kewan ta da yarana.
Aiko wallahi kinzo a sa,a don akwai casu wallahi nace ke har yanzu baki daina maganan wani casu ba can tace ba dole ba mutumiyar fa za aiwa engament jibi .
Da sauri nace wa kenan kuma ta nuna min zainab tana fadin gatanan a gaban ki kuwa wallahi wayo take son muna nidake.
Kallo na mayar ga zainab din dake zaune tana faman taba wayan ta nace wai da gaske ne ko sherin Binta ne kawai dayar yarinyar tace da gaske ne wallahi.
Dan ihu nayi nace amma zainab kin bani mamaki ashe da Allah bai kawo ni ba da saidai inji labari.
Tace a wani yanayi ba haka bane khadija nima ban dauka a yanzu za, ayi abin ba na dauka ko da sauran time ne shiyasa ban fada ma kowa zancen ba.
Ta fada cikin izza da yanga sai yau nake ganin mugun kamar su da yayan nata komai nasu iri dayana sosai sunfi dauka kamanni da mahaifinsu fiye da kowa a gidan.
Nayi murna kwarai sai can na kallo ta nace wai waye wanan lucky guy din da ya iya sace zuciyar wanan yar kwalisan yarinyar haka a lokaci daya.
Binta ne ta bani amsa da fadin ina guy fin nan abokin yayan mu da always Suna tare da yayan mu Abdulsamad mijin buzuwa din nan wanda ake ce Yusuf.
Shine ya sace zuciyar wanan mai zurfin cikin tsiyan da kike gani nima da muke daki daya da ita ban taba sanin wanan labarin ba sai da abin yanuna ya fashe naji.
Kin san matar shi ta rasune a wurin haihuwa shakara biyar da ya wuce shine bai yi wani aure har yanzu ashe rabon zainab ta shiga gidan shi ne ya kashe matar .
Harara zainab din ta aika mata na ki kama kan ki dinan nace amma zainab kinyi dace da mutumin kirki dan arziki daya san mutuncin mutane.
Binta tace kin san shi khadija da kike fadin haka wallahi kin canka daidai kuwa don har yau ban taba jin wani hali nashi na assha ba da aka fadi.
Na dafa zainab din ina fadin yar uwa ina tayaki murna da wanan babban kamu da Allah yayi maki muma Allah ya kaimu ga danshin ki.
Zainab tana murmushi tace baki dai so bane khadija da tuni wani yayi wuf dake wanan zubin naki sai kace wata halfcas dake wani namiji zai ganki ya kau da ido gurine kawai maza basu samu ba.
Kiba da dama yanzu ki gani in bakiga layi a kofan gidan nan ba har ba iyaka na maza a kofan gidan nace ba zasu samu ba yanzu zainab baki ba dai in nan gaba na kammal karatuna na fara aiki ko shi sai kila.
Ya Amina da tunda muka fara magana baita magana ba sai yanzu tace yarinya in tunanen ki ke nan ki canza don baba a jirace yake dake wallahi.
Nace Ya Amina baba ai yafi kowa sanin matsalana karatune burina inga na zama babban lauya wata rana Binta tace wai da mun sha dauri wallahi.
Nace kamar ko kin sani don da na gida zan fara sharia na kada ma kiji wai binta ki rike dakayau a ranki.
Zainab tace kinga mun kama zuba kamar ba gobe ga abincin nan mommy tace mu kawo maki a gurin ta ma muke jin zuwan naki yanzu.
Daga inda Ya Amina take zaune tace wai mommy dai bata gajiya yanzun fa muke maganan abincin nan kamar ta sani sai gashi ta aiko muna dashi.
Mommy ai tafi danan wallahi inji dayar yarinyar ta fada kowa yace wallahi halin mommy ai yayi ne sosai.
Basu jima ba sukai muna sallama akan gobe zamu hadu sai mu kara tatauna abinda za a yi nace dana san da wanan zance ai da tare muka zo da maryam.
Binta tace Allah sarki ban tambaye ki maryam din ba nace tana can na barta tace gobe ita ma gida zata tunda na wuce na barta.
Har bakin get na rako su suka tafi na dawo ciki a inda na bar ya Amina zaune a nan na samay ta nace wai ina yaran suka tafi ne tace suna can gidan kakannin su zasu kwana masu biyu.
Ban san zaki zo ba aida ban kai su can ba don in samu yadda nake so ne yasa nakai su can inji dadin shiga mutane babu takura.
Wanka na shiga na fito na saka wani dogon riga a jikina na shan iska mai dan karamin hannun yadin rigar baida kauri sosai falo na dawo na samu ya Amina tana kallo.
Zama nayi ina jawo kulan abincin da mommy ta aiko min dashi nayi mamakin ganin abincin haka kamar na wata hamshakiya.
Ban san lokacin da nace wai mommy irin wanan hadin haka wallahi ni har kunyar matar nake ji Allah kuwa.
Dariya Ya Amina tayi min tace ko har kun fara sarakutane da ita ban sani ba nace wa zata bani cikin diyan ta haka dai kawai nake jin nauyin ta yanzu.
Wai ni ina Abdulsamad ne ina zancen ku ya kwana dashi ne tun lokacin ban kara jin labarin ba ko da yake yanzu kin fi zama minna ai.
Tsuki nayi ina zama kasa nace ina ruwa na da wanan miskilin mutum da bai san darajan mutane ba halin su au daya da matar shi shiyasa nasu yazo daya da ita.
A,a wallahi baki ko fahince shi ba khadija Abdulsamad mutum ne wallahi mai mutunci da sanin ya kamata ke dai kice Allah ya hada shi da yar banza mata ne mara mutunci kwanaki fa har gari nan tazo taci ma iyayyen shi da matar shi mutunci.
Don Allah ya Amina abinci zan ci kada ki fada min maganan haushin nan ai ita bata da laifi shine mai lefin don ni wallahi da nice Fati da tasha takaici a wurina.
Don wallahi tsab zan zauna da ita don tun yanzu na karanci iya shegen ta balle fati da suka zauna tare tasan halin ta da komai nata may zata gwada mata.
Ke dan Allah can kin san aure ne da kike wanan haukan haka auren fa akace maki khadija ba wani abu ba ita mace dama ta gaji ganin haka walau mai kyau walau akasin hakan.
Abincina naci gaba daci ban taka mata ba ganin nayi shiru itama taja bakin ta tayi shiru tunda ta fahinci ban son zancen .
Ina gamawa tace min a dakin ta zan kwana tunda ita kadai ne a gidan kuma ba a gyara dakin nawa ba don bata san ina tafe ba.
Nace aiko dakin baiyi wani datti ba dan fes na ganshi har da ban dakin tace duk sati ina shiga ina gyarawa don gudun irin haka duk da haka ki bari sai gobe idan an gyara ki kwana a ciki.
Bayan nagama don naci abincin sosai na kwashe kayan zuwa kitchen daki na koma nayi shirin kwanciya wayana kawai na dauka da hijabin da zanyi sallah da safe na fito xuwa dakin ya Aminan.
Na samu ta shiga wanka haka yasa na kwanta abina don dakin ba bako na bane wayana kunna na bude data sakone ya dinga shigo min daga ciki biyu kawai na duba na farko sokon mamud ne yana tambayana karatu.
Sai kuma karshe da yake ce min ya matsu in gama muyi aure in haifa mai yara masu kama dani yana yawo dasu a mota a gari.
Tsuki naja ina fadin baka da hankali mamud nice zan shiga ma ta uku gida don na rako matan duniya komay ?
Sai sakon maryam tana fadin hostel din ba dadi dana tafi don haka gobe gida zata tunda safe duk da tasan yayan ta basu gari da mijin ta.
Zatai zamane na kadaici koda taje amma yafi mata zama a hostel bani amsa na bata nace niko kinga nazo na samu ana buki anan har da engement din zainab da Yusuf alama murna ta nuno min tace yaushe ne bukin nace mata sturday idan Allah ya kai mu.
Gobe zaki ganni tace kai maryam da gaske tace insha Allah ko naje gida Anty basu kasan suna waje da mijin ta ai gara inzo inda kike muyi hutun tare.
Mukai sallama ina murna har ya Amina ta fito ta samay ni hakana nake fada mata gobe maryam zata zo tace ashe ina da bakuwa gobe a gidan kin ga sai kin min list din abinda take ci

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login