Showing 306001 words to 309000 words out of 325849 words

Chapter 103 - BADAKALA

Start ads

20 Aug 2025

506

Middle Ads

da yafi mishi sauk'i kan tahowarta, yanzun haka ya zo ne da niyyar indai zata koma tare dashi to zai durk'usa har gabanta ma ya bata hak'uri, abune da bai tab'a jin ko tsammanin zai ji shi akan wata hallita ba, zuciyarshi ma saida yaji wani zazzab'i ya kamata.

Da sauri ya matso kusan Ummy da nufin tambayarta ina take? Rik'e hannayenta yayi zaiyi magana Hamna ta fito da towel d'in Ummy d'aure da kuma d'an k'arami ta d'aure kanta dashi, tana ganin ta juya zata koma da wani saurin bala'i yasha gabanta, kallonshi tayi fuskarta a had'e shi ma kuma haka.

Saida ya furzar da iska ya saisaita numfashin shi dake jin kamar zai bar gangar jikinshi kafin yace "...


*Alhamdulillah*
04/11/2020 ร  14:39 - Ummulkhairi: ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ
*BADAK'ALA*
๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ _*AHALI NA*_๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

๐Ÿ’ซโœจ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*๐ŸŒŸ
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_๐Ÿค

โ˜† *[ T.M.N.A]* โ˜† ๐Ÿ“–๐Ÿ–Š๏ธ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_

_74_


"Uban waye yace ki fasa min waya?"

Wani kallon mamaki ta mishi, wayar shi ma yake magana akai? Sake had'e fuska tayi tace "An fasa d'in, me zakayi?"

Rik'e k'ugu yayi yace "Biya na zakiyi ko kuma jikinki ya fad'a miki."

Tab'e baki tayi ta rab'ashi zata wuce ya sake tare ta yace "Sai fa kin biya ni yarinya."

A hassale tace "Kai kasan ni ba matsiyaciya bace, amma ba zan biyaka ba dan kaji dad'in kiran wasu yan iska kana hira dasu."

Da wani mamaki a fuskarshi yace "Iyeee Hamna, ni ne d'an iskan ko yan matan?"

Sama da k'asa ta harare shi ta juyo ta tsaya gaban gadon Ummy, bayanta ya tsaya yace "Allah sai kin biya ni kud'in wayata, na yafe miki sauran ma ki ban d'ari biyu, sauran babanki zai cika min."

Juyowa tayi tace "Saboda shine ya fasa wayar? To ko ni dana fasa ba zan biya ba."

Gashinta dake jik'e da ruwa ya fizgo da k'arfi ya matso da ita kusanshi, k'ara ta saki sanda ya rik'e gashin nata, rik'e hannunshi tayi tana kallon fuskarshi da ido jawur tana shirin yin kuka tace "Sake ni Ammar."

Jinjiga kan yayi yace "Waye Ammar d'in?"

Da k'arfinta tace "Kai, kai ne Ammar, Ammar Ammar Ammar! Na fad'a sunanka ne ai."

Sakin gashinta yayi ya jawo k'ugunta ya had'e da na shi yana mata wani kallo mai ma'anoni yace "Naji zan yafe miki kud'in, amma sai munje b'angarenmu."

Hannu biyu tasa ta ture shi tace "Da wa? Ni? Har abada Ammar, wallahi sai ka..."

Leb'enta na k'asa yayi saurin cab'owa da yatsunshi biyu cikin tsananin tashin hankali yace "Karki yarda bakinki ya sake fad'in ba zaki koma gida na ba, tawa ce ke har abada, kin gane?"

Idonshi ta kalla tana sako da hawaye masu zafi tana fad'in "In dai har kana kula irinsu Amie, to ba gidanka ba kad'ai har da tsanarka saina koyawa kaina, zan tsaneka Ammar tsana ta har abada."

Da sauri ya saketa yana sunkuyar da kanshi, hannu d'aya yasa yana murza fuskarshi yana sauke huci mai zafin gaske, kallonta yayi kallo na basira yace "Babu komai tsakani na da ita Hamna, yau na had'u da ita kuma a yau na bata lambata, amma sam ba abinda kike tunani bane."

Da k'arfi ta tureshi baya tana fad'in "To miye inba haka ba? Akan me zaka bata lambarka? Me take da shi a jiki dani bana da shi?"

Da sauri ya rik'e hannayenta yace "Babu Hamna, bata da komai da yake birge ni ma, ke kad'ai ce ke birge ni a yanzu, bayan ke wallahi babu kowa a gabana."

"Amm.." Da sauri Ummy dake tsaye ta zuba tagumi tana kallonsu, kanta har ya fara ciwo saboda cacar bakin nan (ni ma yanzu haka nawa kan ciwo yake Ummy, tunanin yaranki kad'ai nasa gabana ya fad'i), mamakin yanda suka manta da ita a d'akin suke ta maganarsu ma take, wani na fad'a wani ke d'auka shi ma ya fad'a, ita sun hanata damar fad'an wani abu ma, nuna musu k'asan gadon tayi tace "Ku zauna."

Kallon Hamna yayi saida ta zauna k'asan tana rufe kafad'unta da k'aramin towel d'in kafin shi ma ya zauna yana ta kallon fuskarta, kan gadon Ummy ta zauna ta kalle shi a nutse tace "Me ya had'aka da k'awarta har ka bata lambarka?"

Zunbur ya sake gyara zama kamar mai zaman tahiya yana fad'in "Ummy yarinyar nan bata da hankali karki saurare ta, na kai uwa Zeituna wajen bikin Jumare, na dawo shine na ganta na tsaya muka gaisa..."

Duk abinda ya faru ya fad'awa Ummy kafin ya kalli Hamna yace "Shine dan ubanta ta fasa min wayata sabuwa, Allah sai kin biyani ko kuma na siyar da motarki."

Nuna shi tayi da yatsa tace "Kar sake zagar min uba malam, ya isheka haka fa."

Dafe k'irji yayi da hannu ya zaro ido yace "Lah na shiga uku, Hamna ni kike nunawa da yatsa? Mijinki ne ni fa."

Hararanshi tayi tace "Ka sake zagina ma sai kaji tafi a fuskarka Allah."

Ummy ya kalla yace "Shikenan Ummy 'yarki wuta zata shiga."

Cikin juya baki tace "Sai ka kaini ai tunda kai ke da wutar."

Kallonshi Ummy tayi, wai fa so yake ta koma a hakan har ya fara jigata shi, amma dai nuna tsananin damuwar da kuma lallab'ata shine baisan ya zaiyi ba, har da zagi yake had'awa, to a hakan zata koma ko me yake nufi? Had'e fuska tayi ita ma tace "Taje ta fasa wayar, to bari kaji ba ita ba ko ni naga ubanka na waya da wata Allah bayan na fasa wayar ma saina fasa mishi kai, ai kai ta maka mai sauk'i ma, malam fitar min a d'aki."

Galala ya kalli Ummy, me take nufi? Ganin baiyi niyar mik'ewa ba yasa Ummy kallon Hamna tace "Yar albarka tashi canza kayanki, zanje da kaina na d'auko miki kayanki adadin da kike buk'ata."

Wata dariya ya shek'e da ita yana mik'ewa tsaye yace "Eh lallai Ummy ba zaki iya zama alk'aliya ba, kuma da nasan wariyar da zaki min kenan da ban kai uwata wajen bikin nan ba har sai an gama wannan yak'in."

Mik'ewa tayi ita ma ta ja rigarshi tana fad'in "Muje waje a barta ta huta, saina bata maganin ciwon kai tasha saboda damuwar nan daka saka mata."

Juyowa yayi ya kalleta yace "Ke yanzu zaki iya zama babu ni a kusa dake? Kinfa san abinda nake baki kina ci cikin dare."

Ita kanta Hamna saida ta dara tace "Bana so, ka ci kayanka kai kad'ai."

Tsaye yayi ya rik'e k'ugu yace "Ummy kin kassara min zuciyata wallahi, zan fita yanzu amma ba zan sake dawowa nemanta ba, amma Ummy ki tabbatar kin ware mata gadonta, dan zan dinga kawo mata ziyara."

Kallonshi tayi tace "To bismillah kaga yanda zanyi da kai."

Saida ya kai k'ofa ya juyo ya kalleta yace "An dake ni kuma an hanani kuma, ke dai baki da imani wallahi ko kad'an."

Ummy ce tace "Zama da kai ne yasa ta rasa nata ita ma."

Ko da ya shigo da dare da sabuwar waya ya saka layikan nashi a ciki, yana zaune yana duba sak'onnin dake shigo mishi ta WhatsApp yaga bak'uwar lamba ta turo mishi hotuna, shiga yayi dan ganin wanene, tashin hankali sanda ya bud'a hotunan, Amie ta turo mishi hotunan ta tsirara, wanda ke da kayan ma kamar ba'a saka ba na d'aukar hankali ne, da sauri ya lik'e idonshi yana fad'in "Ya salam."

Bud'ewa yayi ya shiga ya goge su duka tare da bloquรฉn d'in lambar, kiran lambar yayi ko da ta gani ta d'auka jiki na rawa, na yan Maradi ya mata ta hanyar cewa "Ke dan mai... me kike nufi da ni? Na miki kama da d'an iska irinki? To saurare ni da kyau kiji."

Saida ya gyara zama yace "In kika k'ara kula ni ma ko a hanya wallahi daga ubanki har kakanki na ashirin sai sun zubar da hawaye, in kika k'ara tuna ko sunan matata ma sai yan uwanki sunyi nadamar kasancewarsu yan uwanki, In kuma kika sake aiko min hoton rub'abb'ar fuskar nan taki mai kama da gurb'ataccen tumatir Allah saina watsa miki asid kin k'arasa dahuwa, shegiya b'abb'akar banza ke ba kyau ba ba kyan jiki ba har ki tsaya kina bariki, to ki kiyaye ni kafin ki fara nadamar sani na da kikayi, yanzu ma wallahi na raga miki ne dan ni dan ni fad'a da mace ba aikina bane, amma da namiji ce ke da tuni na nemi inda kike na cire miki k'ashin baya, 'yar banza mai kama da agwaluma."

*Kuyi hak'uri da jaruminku, bakin ya saba da...*

Amie da tunda ya fara magana tayi shiru take saurarenshi, saida taji ya kashe wayar ta bi wayar da kallo, ya ci mutumcinta sosai fa ta yanda ba zata iya mantawa ba, amma ya zatayi daya wuce tayi wuri ta aje shi, dan tasha jin labarinshi wurin Hamna tun kafin su b'ata, tasan in tace ma tayi dashi ita ce a kasa da cizon yatsa.

Ko da ya gama fad'a shima ya aje wayar ya mik'e ya shiga wanka, daya fito shiryawa yayi cikin kayan bacci ya fesa turare ya fice wajen matarshi. Da sallama ya shiga ya same su duk zaune a falon, kusan Hajia ya zauna yana kallon Nazifa dake kusa da Hamna suna kallon waya yace "Ke tashi samo min abinci."

Mik'ewa tayi a ladabce ta shiga madafa, kallon Hajia yayi yace "Hajia jikar nan taki bata san meye miji ba, kiga fa babu ruwanta da na ci abinci ko ban ci ba, ita dai data samu ta cika tunbi shikenan ni na mutu dan yunwa."

Ko kallonshi ba bare ta tanka masa, haka ma Hajia bakinta taja tayi gum, jin babu wanda ya kula shi yasa yace "Hajia yau wace rana?"

Kallonshi tayi tace "Yau talata."

"To juma'a insha Allahu zamu koma sabon gidanmu."

Duk yayi maganar ne yana kallon Hamna, duk da bata kalleshi ba shiru tayi daga danna wayarta, sanda tayi k'ok'arin kallonshi kuma saita lura da wajenta yake kallo, dan haka bata yarda ta kalleshi ba, Ummy ma kallonshi tayi ba tace komai ba sai Hajia da tace "Ammar da gaske kake?"

A lokacin Nazifa ta fito ta sunkuya ta mik'o mishi abincin, saida ya karb'a ya fara ci yace"Allah kuwa Hajiata, tafiya zanyi daga nan mu barku ku sarara kuma."

Cike da rashin jin dad'i tace "Ammar bana so ku bar nan wallahi, in na bari kuka tafi kamar ban cika burin marigayi ba na son zama a waje d'aya, kuma kaga yanzu kana tashi daga nan sauran ma zasu ce zasu tashi."

Gyara zama yayi yana kallonta yace "Hajia kiyi hak'uri dan Allah ku ba kowa dama ya d'an matsa, ni na miki alk'awari zumuncinmu ba zai lalace ba sanadiyar tashinmu, na kuma miki alk'awarin ko da na tashi daga nan kullum zan dinga zuwa kowace safiya ina gaishe ki, haka ma kafin na kwanta saina tabbatar da na zo kin ganni na ganki sannan."

D'an lab'e baki tayi tace "Shikenan, Allah yasa alkairi."

Su Ameer ya kalla dake kewaye da Husseina tana musu tatsuniya ya kalla yace "Heyy, duk wani wanda yasan mallaki na ne shi ya had'a kwomantsanshi, dan babu wanda zan bari."

Murmushi ta saki daga nan zaune dan ta fahimci ina zancen ina ya nufa, har ya gama cin abinci suna ta hira dasu Husseina da Hajia, bayin Allah dariya har rik'e ciki sukeyi, sun daddage sai biye mishi suke yi kam, idan ya fad'i wani abu ita kanta Hamna da Ummy sai sun murmusa ko har ma su dara, amma duk da haka bata kalleshi ba bare ta mishi magana. Saida dare yayi sosai kowa yayi haramar nufa inda zai kwantar da hak'ark'arinshi, ta mik'e ta nufi d'akinta na yan mata wanda Nazifa ce a ciki yanzu da Huda shima ya bi bayanta, tsayawa tayi ta juyo ta kalleshi tace "Ya dai kake biyata malam?"

Wani kallo ya mata yace "Ke kike bina ko ni ke binki?"

Girgiza kai kawai tayi ta wuce, ko da suka shiga suka same su kwance kan gado d'aya Huda har ta fara bacci, wucewa yayi ya kwanta kan gadon Hamna, kallonshi tayi da mamaki cikin rad'a tace "Meye haka malam? Baka ga yara ne?"

Rintse ido yayi yace "Ban gansu ba."

Juyawa tayi ta kallesu sai taga Nazifa ta mik'e zata fita, da sauri tace "Ke dawo kwanta wajenki, ina zakije ke da nan ne wajen baccinki, bak'on daya mana haure shine zai fita."

Ko da ta fad'a ta shige ban d'aki da kayan baccinta a hannu, da murmushi ya bita ya kalli Nazifada ta dawo ko ta koma ta kwanta, bata jima ba ta fito ta aje kayan data canza kan kujera, kan gadon da suke kwance taje ta shige tsakiyarsu tana fad'in "Ku matsa min nima."

Bud'a ido Huda tayi ta kalleta ta hangi gadonta, saida gabanta ya fad'i ganin tonton d'in ta kan gadon a dakinsu, juya baya tayi ta yanda take kallon k'ofar shigowa ta matsa mata, wajen k'afafunsu ta maido kanta ta d'ora matashi ta kwanta, ta lik'e ido taji muryarshi tsaye a kanta yace "Ku matsa min nima."

A tsorace suka tashi zaune tare ban da Hamna data san halin kayanta, kallonshi sukayi ya kuwa tsaya kusan kanta rik'e da pillow shi ma, Nazifa ce tayi saurin wuntsilawa ta sauka daga gadon ta nufi hanyar fita, da sauri Huda ta tashi ita ma ta bi bayanta suka fice Nazifa na fad'in "Yau mun shiga uku, to su kna d'akinsu wai?"

Cikin turo baki Huda tace "Muje d'akin Hajia kawai mu kwanta."

Ko da taga sun fita ta mik'e ita ma da niyyar bin bayansu, da k'arfi yayi tsalle ya fad'a kanta hakan ya tilasta mata fad'awa kan gadon da k'arfi, da k'arfi tace "Aouch."

Kafin ta bud'a ido taji yayi kwance kanta gaba d'ayanshi ya kuma sakar mata nauyinshi, yanda ya tausheta yasa ta kasa yin numfashi mai kyau, bud'a ido tayi ta kalleshi tace "D'aga ni."

Girgiza kai yayi yace "Zaki koma d'akinmu?"

Girgiza kai ita ma tayi tace "A'a, har sai na yarda babu komai tsakaninka da Amie."

Da k'arfi yace "Babu komai kankana, taya kike tsammanin zanyi iskanci a waje bayan ina da ke? Sannan na rasa da wanda zanyi iskancin ma sai k'awar ki? Na yarda ni mahaukaci ne kuma ba mutumin kirki ba, amma bana neman mata Hamna kuma bana shan ko da sigari bare k'waya."

K'afeshi tayi da ido tana kallo, kallon tausayi da jin k'ai da rahama, wa yace shi mahaukaci ne? Dan tana fad'a masa haka ai kawai tana fad'a ne, me yasa zai yarda shi mahaukaci ne kuma ba mutumin kirki ba? Bata ji dad'in abinda ya fad'a ba, a hankali cikin fitar da wahalallen numfashi tace "Wa yace kai ba mutumin kirki bane?"

Saida ya k'ank'ance idonshi yace "Ke mana, haka kike kallona ai."

A hankali ta d'aga hannunta ta shiga shafa fuskarshi a hankali tana kallonshi, cikin taushin murya sosai tace "Kai mutumin kirki ne Abban yarana, duk gidan nan muna alfahari da kai, dalilinka ne abubuwa dayawa suka canza, ka daina wa kanka wannan kallon, kaji? Ka daina bana so."

Yanda ta k'arashe maganar da matuk'ar shagwab'a da kashe murya yasa shi jin zuciyarshi ta k'ara narkewa, murmushi ya saki yace "Amma duk da haka ai baku sona."

Idonshi ta kalla tace "Waya fad'a maka, muna sonka yah Ammar, muna k'aunarka dukanmu."

D'aya hannun tasa ta tallabo fuskarshi suna kallon juna sosai tace "Ammar *ina sonka*, d'azu nayi niyyar fad'a maka haka, amma wannan Amien..."

Ture shi tayi daga jikinta ta tashi zaune tana kallonshi, shi ma kallonta yake yana jin kamar ya fasa ihu yau Hamna ce tace tana son shi? Yana kallonta ta tashi tsaye tana fad'in "Saina fara cin uwar yarinyar nan kafin hankali na zai kwanta, sai naji abinda ya had'ata da mijina."

Tasowa yayi yana k'arewa fuskarta kallo yana fad'in "Hamna ni kike kira mijinki? Wuuuuu duniya dad'i, Hamna yau nine kike so? Kishi na kike?"

Da sauri ya d'auki wayarta dake kan kujera ya bud'e ya shiga danne danne, tana kallonshi ita dai sai ji tayi ya saka wak'ar *Umar m Shareed* mai taken *soyayya akwai dad'i*, aje wayar yayi sai kuwa ya shiga kwasar rawa ba kunya ba tsoron Allah, da fari da mamaki ta fara kallon yanda yake rawar, amma sai abun ya fara bata dariya, zaune tayi bakin gadon tana kallonshi, tsakaninshi da Allah yake rawar kamar ya ga *Adam A. zango* a gari, bata ankara ba taji ya jawota yana juyata a dole ita ma tayi rawar.

Tun tana tirjewa tana so ya rabu da ita har wata wak'ar ta shigo wacce ta iya taka rawarta fiye da zaton mai karatu, (in baku manta ba tun a farkon littafin ita d'in gwanar rawa ce da iya shoki๐Ÿ˜‚), biye masa tayi suka shiga rawa har da dariya kamar mahaukata.

Ummy da tasan sai sun tsula tsiya tunda taga ya shiga d'akin, kuma a gaban idonta su Nazifa suka fito, ta jima tana k'wank'wasa k'ofar amma basu ji ba, kuma gashi tana jin dariyarsu da sautin kid'a, dan haka kawai ta tura k'ofar ta shiga idonta rufe dan kaucewa mummunan gani, a hankali ta bud'a ido ta hange su sun cake sai kwasar rawa, rik'e baki tayi tace "Inna lilliahi wa'inna ilaihi raju'un."

Da sauri suka tsaya suna kallonta, ko da ya ga Ummy ce ya matso yana fad'in "Ummy albishirinki?"

Ta d'auka zai ce Hamna ce ke da ciki, sai kawai ta kalleta tace "Hamna wace lalacewar ce kuma wannan? Rawa a daren nan?"

Laushi tayi kamar ba ita ba tana k'yabta ido, jinjina kai Ummy tayi tace "To maza d'auki kayanku ku koma b'angarenku kafin ku tara mana aljanu, tunda abun ya zama iskanci, nan kike ta kumbura ke hushi kike ashe d'aurin duniya ne."

Langab'e kai tayi tace "Allah Ummy da gaske ne, yanzu ma da zan ga Amie saina tattaka ta."

Kallonta Ammar yayi yace "Wai ke ba zaki fita harkar yarinyar nan bane?"

Zaburo mishi tayi tace

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login