Showing 111001 words to 114000 words out of 325849 words
"Tarbiyya? Kai tarbiyyar ce da kai da har zaka wa wani? Dallah malam fitar min anan wurin kafin ranka ya b'ace."
K'asa yayi da hannunshi kamar zai kama kunnen Hamna hakan yasa Ummy yin k'asa da sauri da niyyar rik'e hannun, cikin azama ya saka d'aya hannu ta sama ya kama kunnenta ya murd'e, wata uwar k'ara ta saki a kunnen Ummy ta fashe da kuka tana k'amk'ame ta, k'ok'arin yakice hannun ta fara yi amma ina ta kasa, shi kuma Hamna data bud'e bakin nan yayi nasarar buga mata hannu dole tayi shiru ta rufe bakin da hannaye yana fad'in "Wallahi kashedi na k'arshe zan miki, idan kika yarda kika sake fita daga gidan nan babu hijabi sai na ci k'undun ubanki, kuma wallahi tun a inda na had'u dake zan fara bugaki har cikin gidan nan, tunda dai ba kya jin magana ke, munafuka kawai."
Sakinta yayi ya juya ya bar d'akin Ummy ta bishi da bala'i amma ko a jikinshi, da fitarshi kuma sai ga colonel ya iso har cikin gidan yan rakiyarshi suka shiga, saida zai shiga d'aki ya dakatar da su ya shigo ciki, saida ya gaisa da mutane sosai da yara kafin ya shiga dan yin wanka.
Ya gama wanka ya saka dogon wando da singlet zai saka riga Zeinabu sarkin tsegumi tace "Amma dai kasan duk cikin sabgar nan da za ayi mu akafi cuta ko?"
Da mamaki ya juyo ya kalleta ya dakata da saka rigar yace "Me? Cuta fa kika ce? Cutar me aka mana?"
Zaune tayi bakin gado tana fad'in "To kayi tunani mana ka gani, mu fa yara uku zamu aurar lokaci d'aya, kuma biyu daga ciki mata ne, ka kuma san auren mata yafi na maza kashin kud'i, kaga kywa ai zamu shiga uku."
Kallon anya kuwa matar nan nada hankali ya mata? Dan shi dai inba hauka ke damunta ba baiga abun mita ba anan, da mamaki yace "Zeinabu yaushe kuma gidan nan muka fara rayuwar tsiya da talauci? Yanzu ke duk a lamarin nan kud'in da zaki kashe ne matsalarki? Ba wai farin ciki da 'ya'yanki zasuyi aure ba, meyasa kike hakane? Ke nama ji zamu kashe kud'in, babu kud'in ne na kashewa? Ko kuma ke aka ce ki fito dasu ki kashe bare ki wa mutane iya shege, sannan meyasa bakiyi tunanin d'an uwana ba da kuma matarshi Sa'ada? Su fa duka yayansu maza ne wanda su zasu kai, ke kuma d'an ki d'aya ne zai kai biyu kuma mata zasu kawo miki abun arzik'i, mtssss, wallahi Zeinabu matsalarki tayi yawa."
Mik'ewa tayi jin k'orafinta yau ma bai karb'u ba ta nufi k'ofar fita tana magana k'asa k'asa da fad'in "Aikin banza, ai nasan dama ba tunani gareka ba bare ka hango abinda na hango mana, indai har zamuyi yanda akeyi ne ai mazan idan sun kawo mana sai mun kusa ninka musu abinda suka kawo a cikin gara."
Tana daf da kaiwa k'ofar taja tsaki tare da murgud'a mishi baki, da k'arfi ya juyo dan tabbatar da gaske ne abinda yaji wai, ita ma sai bayan tsakin ya fito ta fahimci bala'in data jawowa kanta, ai da wani irin k'arfi yayo kanta zai cabkota amma hukuncin ubanjigi saita zame ta juya da gudu ta fad'a ban d'aki duk da k'ok'arin shi na son cabkota, tana shiga da iya k'arfinta ta maido k'ofar ta rufe daidai yana kawowa, kile tasa ta rufe gam shi kuma ya shiga bubbuga k'ofar yana fad'in "Zeinabu ni? Ni kike wa tsaki! Zeinabu yaushe kika raina ni haka? Allah ki bud'e k'ofar nan ko na karyata."
Wata irin jijjiga ya wa k'ofar da yasa ta fara motsi da k'arfi kamar zata karye, Zeinabu kam ciki ya d'uri ruwa sosai, tasan inhar ya bud'e to saiya karyata kam, yana cikin jijjiga k'ofar da k'arfi Sa'ada da tun farkon fara bubbuga k'ofar shi taji dan tana falon zaune ta kira Junaid tace ya zo, yana zuwa d'akin ya bud'a ya shigo da sauri ya tunkaroshi ya rik'e shi yana fad'in "Yi hak'uri dan Allah Abba, kayi hak'uri, muje ka rabu da ita."
Wani kallo ya ma Junaid ido jawur ya fizge ya shak'i wuyan rigarshi yana fad'in "Dan ubanka waya kawo ka? Me ma ya shigo da kai? Ka zo ne ka shigar ma uwarka? To yau saina kasheta a gidan nan, nace saina kasheta idan ya so nima a kashe ni."
Yanzu kam Junaid ya fahimci uwar tashi ta kwanto musu kura, turashi yayi ya kaiwa bango karo ya sake kama murfin k'ofar ya jijjiga da k'arfi, cikin d'aga murya yace "Shikenan, ai kin k'i bud'ewa ko, to bari kiga yanda zanyi da k'ofar."
Da sauri ya juya kayanshi daya shigo dasu ya fitar 'yar k'aramar bindigar dake jikin kayan ya zaro ya nufo k'ofar, Junaid na ganin haka ya shiga gaban k'ofar yana sake bashi hak'uri amma saiya ture shi gefe, ganin abun yafi k'arfin shi yasa shi fitowa yayi daidai da fitowar Hajia, da sauri yace "Hajia dan Allah ki zo kafin Abba ya kashe Umma, wallahi ranshi ya b'ace."
Da azama ta tako ta shigo d'akin tana fad'in "Kisan kai? Karfa yaran nan ya ja mana masifa a gida."
Tana shigowa daidai colonel yasa k'afa da k'arfi ya bangaje k'ofar, Zeinabu na jin ya bud'e ta dafe kanta da hannaye ta k'ame wuri d'aya ta rintse ido jin fitsari na zubo mata daga tsaye, shi ma kuma yana ganinta gabanshi ya saita bindigarshi ya nuna mata yana fad'in "Me na fad'a miki? Bance miki ki bud'e ba kafin na shigo da kaina, to yau zzzz..." Bai k'arasa ba Hajia ta shiga tsakaninsu tace "Ka kashe ni Hussein kafin ka kasheta, tunda so kake ka jawo mana abun kunya."
Ganin Hajia gabanshi ya sa shi kaucewa cikin hassala ya buga bindigar a bango ya saketa ta fad'i shi ma kuma ya kaiwa bangon duka da hannunshi, a hankali Hajia ta dafa kafad'ar shi ta shafa, shiru yayi bai juyo ba hakan yasa ta kama hannunshi suka fita zuwa falo, Junaid kuma kallon mahaifiyarshi yayi cikin ladabi yace "Umma dan Allah ki rage duk wani abunda kika san Abba baya so, duk zafin zuciyar Abba kana iya zama kayi hira da shi ku fahimci junanku, amma ko yau Abba zai shigo gari sai kaji hayanuyarshi kin b'ata masa rai."
Haushi ne yasa Zeinabu cewa "Kai ni fita ka bani wuri, tunda kana bayan uban naka saika zo ka bashi kashi."
Tsaki tayi ta mayar da k'ofar ta rufe duk da bata rufu da kyau ba dan ya riga ya b'allata, shi kuma fita yayi ya samu mahaifin nashi zaune ya tangale gwiwoyin hannunshi kan cinyoyinshi ya dunk'ule hannunshi yana dukan d'aya hannun, Hajia ce kawai zaune tana kallon tv da tunanin idan ya sauko sunyi maganar da zasuyi akan tafiyarsu ta gobe, suna haka su Alhaji suka shigo tare da lieutenant, bai ma kowa magana ba kuma suma basu damu ba sun san kayan ne suka motsa, zaune sukayi sai Alhaji daya kalli Junaid yace "Ka kira min uwar 'yan biyu, idan ka dawo ka kira min su kansu yan biyun."
Sama ya haura ya samu Sa'ada can ya kirata ya dawo, b'angaren su ya nufa ya kira Ammar da Amar suma suka zo, Alhaji da kanshi ya kira Husseina da Labaran da suke tattaunawa suma kan auren Jibril da Jamila, saida suka had'u ya kalli kowa da kyau kafin yace "...
πππ
17/06/2020 Γ 22:08 - Ummulkhairi: π©ββ€οΈβπ¨π©ββ€οΈβπ¨π©ββ€οΈβπ¨π©ββ€οΈβπ¨π©ββ€οΈβπ¨π©ββ€οΈβπ¨π©ββ€οΈβπ¨π©ββ€οΈβπ¨π©ββ€οΈβπ¨π©ββ€οΈβπ¨
*BADAK'ALA*
π©ββ€οΈβπ¨π©ββ€οΈβπ¨π©ββ€οΈβπ¨π©ββ€οΈβπ¨π©ββ€οΈβπ¨π©ββ€οΈβπ¨π©ββ€οΈβπ¨π©ββ€οΈβπ¨π©ββ€οΈβπ¨π©ββ€οΈβπ¨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
π¨βπ©βπ§βπ¦ _*AHALI NA*_π¨βπ©βπ§βπ¦
π³πͺ *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```
_Bismillahir rahamanir rahim_
_19_
"Abinda yasa na taraku dama dan na fad'a muku wani abun alkairi ne daya tunkaro mu, insha Allah nan da kwana uku zamu sake yawa a gidan nan."
Shiru kowa yayi sai kallonshi da suke babu wanda yace wani abu, Husseina ce tace "Masha Allah, ah lallai abun farin ciki tunda zamu k'aru ne, amma ta ina?"
Kallon Hajia yayi data tsura mishi ido tana jiran tajiba daidai ba ta fara masifa, had'e rai yayi sosai dan karta kawo mishi wasa kafin ya kalli Sa'ada yace "Sa'ada, kiyi hak'uri abisa abinda ya faru, laifina ne bana mijinki ba, kamar yanda zaki ji yanzu shima haka kawai yaji na yanke hukuncin, amma na tabbata idan kuka ji dalili na zaku fahimce ni, nasan kina da ilimi kuma ba yarinya bace ke, idan har kin kama girmanki hak'ik'a zakiji dad'i sosai anan gaba, 'ya na d'auke ki kamar yanda babba yake d'ana, ina fatan kema zaki min biyayya."
A ladabce ta kalleshi ta kashe murya tace "Abba insha Allahu ba zan baka kunya ba, nima a uba nake kallonka wallahi, ka isa ka zartar da kowane irin hukunci a kanmu bamu da ja akai."
Cikin jin dad'i yace "Alhamdulillah, nagode da kika fad'i haka, dama ba wani abu bane, yarinyar nan dake muku aiki Zeituna, ita ce a wani mawuyaci hali da tale buk'atar taimako, shiyasa yau d'in nan na nemawa *Baba na* aurenta, kuma kawunta ya amince nan da kwana uku za'a d'aura auren bayan sallah juma'a insha Allahu."
Kowa kallonshi ya sake yi, kusan tambayoyin d'aya ne suke yawo a zuk'atansu, Zeituna? Lieutenant kuma? Meyasa sai shi to? Wani murmushi Sa'ada ta k'irk'iro tace "Masha Allah, Abba wannan abun farin ciki ne daya kamata mu godewa Allah, gaskiya naji dad'i har raina wallahi, Allah yasa alkairi ya bamu zaman lafiya, gata kuwa yarinya mai nutsuwa da ladabi, dan ko ido bata had'awa dani."
Kamar daga sama Ammar dake zaune k'afa d'aya kan d'aya yana danna waya yace " Amma ai tana had'awa da mijinki ko? Kinga Ummy karki fad'i abinda kika san ba haka bane, mu maza munfi kowa sanin yanda kuka tsani kishiya kamar yanda kuka tsani mutuwarku."
Kallonshi kowa yayi amma shi hankalinshi na kan waya bare ma ya ga kallon da bai masa ba ya sake magana, Husseina ce tace "Amma Ammar ai sai mu jinjina mata tunda har zata iya k'ok'arin b'oyewar ma."
Sai lokacin ya d'ago ya kalli lieutenant ya kalli Alhaji yace "Alhaji, yanzu domin Allah meyasa sai Abba zaka had'a ta dashi? Shin kaga yarinyar kuwa? Ita fa yarinya ce shi kuma tsoho, me zai sa idan taimakonta kake so kayi ka k'i had'a ta da d'aya daga cikin matasa majiya k'arfi? Amma ace sai uwar mu ce kawai ake sha'awar ganinta da kishiya, to gaskiya ni dai ban amince da auren nan ba, ai ga Jamil nan, ya isa aure shima, a had'a shi da ita ma tunda shine Hajiar makka bata wa mata ba, idan yarintar shi kuke gani ku had'a shi da ita nan da kwana ukun kuga idan ba'a nuna muku bayyanar ciki gwajin da za ayi mata fa kafin bikinmu, dan haka kawai ku bar maganar nan."
Lieutenant ne ya kalle shi yace " To marar kunya fitsararre, kenan duk wurin nan kai kafi uban kowa bakin iya magana, wai ni wa ma ya gayyato shi wurin nan ne da har zai zo yana mata iya shege?"
Gyara zama Ammar yayi yace "Ni fa ina zamana aka ce na zo, kasan meyasa aka ce na zo? Saboda nine babban d'an ka kuma sanyin idaniyarka na farko, ana so aji ta bakina ne kuma na fad'a ni dai ban yarda a had'a k'azamar yarinyar nan kishi da uwata ba."
Lieutenant zaiyi magana Alhaji ya kalli Ammar yace "Ammar wannan fa hukuncin dana yanke ne, yanzu ja zakayi da ni kenan? Bayan shi kanshi uban naka ya amince."
Mik'ewa yayi yace "Da alama ba zamu fuskanci juna daku ba, amma yarinyar nan tana shigowa gidan nan a matsayin matar ubana kuma kishiyar uwata wallahi saina rabata da mak'ogwaronta in yaso ayi duk wacce za ayi."
Colonel da har yanzu Zeinabu yake hangowa shi dai kallon kowa kawai yake, juyawa Ammar yayi zai fita Hajia wacce farkon al'amarin ita ma daru taso tayi, amma ganin babban jikan nata ya nuna bai yarda ba alhalin gata zaune yasa ta shirya b'ata mishi rai, cikin gadara tace "Ka ce baka yarda ba? To yanda da baka yardan ba ya za ayi kenan? A fasa?"
Juyowa yayi yace "Eh haka nake nufi."
Murmushi ta masa tace "To bari kaji Ammar, wallahi auren nan kamar anyi an gama, yar aikin gidanku zata shigo gidan nan a matsayin kishiyar uwarka, za'a ware mata d'aki kamar yanda aka ware ma uwarka, ubanka zai raba musu kwana, a gaban idonka dana uwarka zai shiga d'akin amaryar shi sai dai in kunga haka ku had'e zuciya ku mutu, kai idan da rabo ma nan da wata tara sai kunga sabon k'anenku da idonki."
_Ina fatan dai kun fahimci inda yayi gadon rashin kunyarshi da fitsara?_
Wata dariyar rashin mutumci ya mata yace "Hajajju mutan makka, ban miki musu ba cewa madarar mahaifina zata iya tasar d'an adam ba, amma gamsar da ita matar kam w..."
Cak ya tsaya da kalamanshi saboda saukar marin akan kumatunshi, Ummy ce tsaye gabanshi tana huci dan ba zata iya saurarenshi ba, da yatsa ta nuna masa k'ofar fita tana fad'in "Fita daga d'akin nan, ka fita nace."
Kallon Ummy yayi idonshi jawur da su kamar zai kama da wuta, cikin wani irin yanayi ya kalli Ummy kai kace ramawa zaiyi yace "Ummy mari na fa kikayi? Akan maganar k'azamar yarinyar da tsabar datti da za'a d'auke ta a jefa a cikin ruwan *Madarunfa* babu abinda zai hana ruwan yin bak'i k'irin, shikenan na fita."
Kallon Alhaji yayi wanda shi kanshi baiji dad'in marin ba yace "Alhaji na zo ne saboda ance kai kake nema na, amma ba dan haka ba da babu abinda zai sa na zo dan duk nan ciki bayan kai babu wanda zai iya kirana domin magana ta arzik'i."
Juyawa yayi zai fita cikin k'arajin murya Ummy ta fashe da kuka tace "Fita d'an iska kawai, duk nan ciki waye sa'anka da zaka zauna kanawa fitsara da rashin kunya."
Tsayawa yayi ya juyo da k'arfi da niyyar magana amma kuma zuciyarshi bugawa take da sauri, k'urawa Ummy ido kawai yayi kamar zai cinyeta d'anya, bubbuga k'irjin ta tayi tace "Eh na fad'a, kai sarkin zuciya ko? Ranka ya b'ace ne? To zo ka dake ni Ammar."
Husseina ce ta mik'e ta kamata ta zaunar da ita tana fad'in "Dan Allah Sa'ada ki daina zubar da hawaye akan d'an da kika haifa a cikinki, shin kinsan tasirin da hakan zai masa kuwa?"
Cikin kuka ta kalli Husseina tace "Hajia menayi? Wane laifi na aikata a duniya dana cancanci haihuwar Ammar? Shi fa ba k'aramin yaro bane, amma kullum saiya b'ata min rai a gidan nan hankalinshi ke kwantawa."
Ammar da har yanzu ke tsaye yana kallonta idonshi ne suka sake rinewa, bugun zuciyarshi kuma ya sake nunkuwa, had'e hannunshi yayi ya dunk'ule shi cikin b'acin rai da neman wanda zaiyi masifa da shi ya juya, ai kuwa tvn Hajia ya kalla ya gabzawa dunk'ulellen hannun nan, abinka ga tvn zamani kuwa wacce ke manne a jikin bango sai kuwa ta gabce ta fad'o k'asa inda ta bugi k'aramin teburin glishin da aka d'ora dΓ©coder da kuma remonte, a tare kayan duk suka fad'o suka watse, juyowa yayi lokacin da wasu hawayen bak'in ciki da takaici suka zubo daga idonshi cikin muryar da zata tashi hankalin mai sauraro ya rik'e murfin k'ofa yace "Idan har kun tsane ni ku kashe ni mana, me ma yasa kika bari na zo duniya baku kashe ni ba? Ku kashe ni mana na huta kuma ku huta, naji ni d'an iska ne, fitsararre, marar kunya, bana da anfani a gareku, baku ga anfanin haihuwata ba, to na mutu mana ina ruwanku?"
Idan ka cire Hajia da lieutenant dukansu mutanen wurin mik'ewa sukayi tsaye saboda tsoron ganin halin da yake ciki, k'ofar daya rik'e sosai ya turata da k'arfi ta bada wata k'ara mai k'arfi, juyawa yayi kamar zai tashi sama ya bar d'akin ya nufi b'angarensu, Amar da d'an sauri ya fito da niyyar bin bayanshi Hajia tace "Shalele rabu da shi, ai dai kasan zuciyar ce ta motsa ko? Kuma kafi kowa sanin cewa yana hucewa kan wanda ma bai ji ba bai gani ba, dan haka rabu da shi karya illatala, ka barshi har ya sauko zai zo ya biyani tvn nan daya fasa bak'in munafiki kawai, dama yana jin haushin kallon da nake."
Lieutenant ne yace "Rabu da shi, ba mai kai ba kar wanda ya kuskura ya tanka masa har zuwa lokacin da zai sauko."
Alhaji dake tsaye ne cike da nuna rashin jin dad'i yace " Dan Allah magana mai dad'i ta dinga fitowa daga bakinku zuwa kanshi, ba kusan komai k'aramtar kalma kuka fad'eta tasiri take akan yaranku ba, kuma ya kamata ace kuna hak'uri dashi, yanzu nan kunsan dan kwana uku ba zai kula kowa ba."
D'an k'aramin tsaki yayi ya nufi d'akin shi inda Hajia ta bishi da harara da gunaguni kuma daga lieutenant har colonel babu wanda bai gani ba, duk da hakan bai musu dad'i ba amma hak'ura sukayi, Sa'ada ma da sauri ta tashi ta shiga d'akin ta tana ci gaba da kuka inda lieutenant ya bi bayanta, Hajia ma mik'ewa tayi ta nufi d'akin Alhaji dan suyi magana, hakan ne ya bawa Amar damar fita ya bi bayan d'an uwanshi da tunanin shi kawai ke kan hannunshi daya rotse yake zubar jini amma shi yaga bai ma damu ba, colonel kuma kallon Junaid yayi wanda shi dama tunda aka fara magana tsaye yake yace "Saika wuce ka d'auko min rigata d'aki, dan inhar zan shiga babu abinda zai hana ni gota uwar nan taka."
Da sauri Junaid ya juya ya shiga d'akin, akan gado ya d'auko rigar ya fito har lokacin Zeinabu na ban d'aki, yana kawo masa ya saka fita yayi ya bar gidan shima.
Yana shiga kai tsaye d'akin magungunanshi ya shiga, zaune