Showing 204001 words to 207000 words out of 325849 words

Chapter 69 - BADAKALA

Start ads

20 Aug 2025

595

Middle Ads

bi bayanshi da motarshi saiya kaiwa lieutenant tashi a can ofishin shi, Jano na daidaita motarshi zai fita ya fito daga tashi motar ya same shi, saida yasa ya sauke gilashin suka kalli juna yace "Jano karka manta, a dalilinka na tab'a shiga prison, dan haka kaima ka shirya shigarshi ko da na kwana d'aya ne, ka dai san nasan shige da ficenka da kuma sana'ar da tafi shigo maka da kud'i."

Saida ya nuna mishi yatsa yana kalkad'a shi yace "Ka kula."

Wucewa yayi ya barshi nan, tare da yaron da ya zo suka tafi shi a motar lieutenant har suka isa. Yayi mamaki sosai da aka ce wai Ammar na son ganinshi, Ammar dai daya sani? A gaskiya ba dan Ammar d'aya ya sani ba a duniya idan ka cire *sahabi Ammar bin Yaseer wanda suka fara shahada a musulunci* da sai yace shine amma ba nashi ba, dan nashi in ya zo kai tsaye yake shiga ko da yana tare da bak'i ne, izinin shigowa yasa aka masa, saida ya ganshi ya dai tabbatar shi d'in ne, cikin nutsuwa ya zauna kan kujerar dake fuskantarshi ya bashi makullan yace "Abba gashi, nagode."

Shima cikin yanayin kulawa yace "Har ka dawo ne? To ya ake ciki?"

"Ba komai Abba." Ya fad'a babu walwala tare dashi, saida ya gyara zama ya kalli lieutenant yace "Abba, akwai wata masaniya da nake son baku kan wani mutum, bansan ko kana so ba?"

Kallonshi yayi da murmushi, ko ma wanene tashi ta k'are cewar lieutenant, amma sai yace "Zamu so mana idan ya shafi aikinmu."

Sai kuma kawai ya mik'e zai fita yace "Shikenan, zan nemo." K'ofa ya tunkara lieutenant ya bishi da kallo, me yake nufi kuma? Ganin zai fita yasa yace "Ammar."

Juyowa yayi da fad'in "Na'am." Saida ya kalli agogo yace "Da k'arfe hud'u na yamma ka same ni gidan gona ta dake kusa da *Olga oil*."

Da d'an murmusawa yace "To Abba."

Fita yayi da wayarshi a hannu yana neman wata lamba, saida ya shiga mota ya zauna sannan ya aika kiran, bayan an d'auka sun gaisa ya fara mishi wasu tambayoyi, sun d'an jima suna magana kafin daga bisani yace "Ka tabbatar motar kayanshi ce ake d'orawa?"

Daga d'aya b'angaren aka ce "Na tabbata yallab'ai."

"Ya yanayin lodin yake?" Ya tambaya, daga can tace mishi "Eh to, kwalayan (karton) indomie ne da lipton, sai atampopi daga sama da shadda, sai kuma buhunan shinkafa a sama."

Wani murmushin da shi kad'ai yasan ma'anarshi yayi yace"Nagode, zan sake kiranka."

Yana kashewa ya tayar da motar ya d'auki hanyar, wannan binciken k'wak'wafin shi ya wuni yana yi, daga nan zuwa can daga can zuwa nan, waya kuma har ya gaji da amsawa duk saboda son kawo k'arshenshi, sai misalin *12:30* ya d'auki hanyar komawa gida cike da gajiya, kai tsaye b'angarenshi ya nufa da makulli a hannu da waya, da wata zazzak'ar sallama ya shiga sai dai babu kowa bare bare a amsa mishi, falon yasha gyara sai k'amshin turaren wuta yake na jonawaa lantarki, ga kwanukan abinci da aka jera wurin ya k'ayatu, murmushi kawai yayi ya aje makullin da waya akan teburin tsakiyar falon ya shiga d'akinta. Tana tsaye gaban madubi tana d'aure k'ananan kitsonta, yana ganinta ya fad'ad'a murmushinshi da fad'in "Wow, duniyata."

Da sauri ta juyo ta kalleshi, murmushi tayi ita ma tare da takowa cike da kunyar kayan data saka, tana zuwa ta narke a jikinshi tana sauke numfashi a hankali, ni'imtaccen k'amshinshi turarenshi ne ke ratsa hancinta, shafata yake tare da mamatsa bayanta yana cika hannu da tsokar bayanta ido rufe, har tsakiyar kanshi yake jin duk wasu albarkatun jikinta na sake samun matsuguni a na shi jikin, turaren na kwantar mishi da hankali sosai, a hankali ta d'ago kai ta kalleshi, kallon tattausan fuskarsa wacce ke canza launi duk sanda ta so yasa ta lumshe ido, saida ta d'aga k'afafunta ta kai bakinta daidai na shi ta sumbata, babu wata k'ara ko sauti, saidai tasirin sumbar yasa ya lumshe ido, lokaci d'aya suka bud'e ido a tare suka kalli juna, murmushi ta sakar masa tace "Ka gaji ko yah Ammar?"

Girgiza kai yayi cikin sanyin murya yace "A'a ba yah Ammar ba, ki saka min wani sunan na daban."

Saida ta jujjuya matsakaitan idonta tace "Umm! Kamar wane kenan kake so?"

Murmushi ya mata yace "A ganinki wane sunan na cancanta? Ni dai kinga na baki sunan duniyata, saboda kin zama dunuyata, ni kuma fa me na zama naki?"

Saida ta k'ara rik'e k'ugunshi da kyau da hannayenta tana kallon k'asumbarshi sannan tace "Nima ka zama duniyata, sabuwar rayuwata kuma farin cikina."

Raba jikinshi yayi da na ta ya d'an turata gefe ya k'ura mata ido, kallonta yake kamar zai had'iyeta, dogon wandon jeans bleue dark da riga bleue light mai hannaye iya damtse, dogayen takalmi bak'ak'e sai yar gajerar kwalliya da tayi, juyawa yayi yana zagayata dan ganinta da kyau, masha Allah duk da tana da gaba sosai, amma kuma sama suke can mak'ale da k'irji, bayan nan kam tubarkallah yau data saka wando ya zauna mata daram akansu sai abun ya bayar da citta. Kiran sallah a masallacin dake jikin gidan nan ne yasa yace "Bari na dawo daga masallaci, ina nan tare dake sai la'asar zan fita."

Ban d'akinta ya fad'a yayi alwala ya fito, gabanta ya tsaya ya danna mata wata mahaukaciyar sumba a goshi sannan yace"Saina dawo."

Tare suka fito daga d'akin shi ya fita ita kuma ta zauna zaman jiranshi.


Tunda Ummy ta shiga d'aki bata sake fitowa ba, har asibiti ake ta kiranta wasu k'ananan ma'aikatan na tambayarta kan wani abu idan ya shige musu duhu, har akayi sallah azahar aka gama bata fito ba, damuwa da halin da take ciki yasa Zeituna shiga d'akinta dan ta gani, da sallama ta shiga Ummy kuma naji bata amsa ba, dan haka bata shiga ba saita tsaya daga k'ofar tace "Ummy Ammar kina lafiya? Naga har anyi sallah kuma baki fito ba."

Tasowa tayi daga inda take ta zo ta bud'e k'ofa, kallon kallo sukayi sai yanayin damuwa tare da ita, cike da kulawa tace "Ummyn Ammar lafiya ko? Ko ba kya jin dad'i ne?"

Saida ta rufe d'akin ta fito ta fuskanceta sai kawai ta d'auketa da wani wawan mari, dafe kumci tayi lokaci d'aya ta saki k'ara, Zeinabu da fitowarta kenan daga sallah taji saukar marin, da sauri ta matso tana kallonsu da mamaki, Nana ma dake kan ajiye abinci a tebur ita ma k'ura musu ido tayi, Inna ma saukar marin taji ta tsaya, ba tare data bari ta d'ago ba Ummy ta nunata da yatsa tace "Wannan shine abinda ke faruwa, bana son munarfici da iyayin tsiya."

Tsaki tayi ta bita da harara ta fita harabar gidan, Zeituna data kasa had'a ido da ita saida taga fitarta ta tafi a guje d'akinta, Inna ce ta bi bayanta har d'akinta, tana zuwa ta sameta ta zauna kusanta tace "Amarya kiyi hak'uri, hakan zaman ya gada dama indai ance zo mu zauna to zo mu sab'a ne."

Saida ta share hawaye sosai ta kalli Inna tace "Ba komai Inna, ni ai ba bak'uwar zafi bace, kawai ki kwantar da hankalinki."

Murmushi tayi tace "Hakane amarya, Allah ya baki hak'uri da juriya, insha Allahu zaki zama fitilar gidan nan da zata haskaka kowa."

Murmushi ita ma tayi tace "Ameen Inna."

Tashi tayi tace "Ni zan koma wajen aiki."

Zata fita daf da k'ofa suka had'u da lieutenant zai shigo, gyara mata yayi ta wuce tana mishi sannu da zuwa, amsawa yayi da mutumtawa kafin ta fice shi ya shigo, da kulawa ya kafeta da ido ganin kamar tayi kuka yace "Lafiya amaryata? Meya sameki?"

Da murmushi tace masa "Sannu da zuwa, amma yana ganka a wannan lokacin?"

Matso da ita yayi gabanshi yana shafa fuskarta yace "Meya same ki Zeituna?"

"Ba komai fa." Ta fad'a tana neman zillewa, sake rik'ota yayi yace "Ni fa ba yaro bane, kinsan da haka?"

Kallonshi tayi cike da yamutsa fuska tace "Ciki na ne yake d'an min ciwo, amma kuma yanzu ya daina."

"Kin tabbata ya daina?" Cike da tabbatarwa tace "Ya daina."
Sakinta yayi ya nufi wajen wata drower dan d'aukar abinda ya kawoshi.

*Bayan* sallah la'asar ya gama shiryawa zaije gidan gonar, a falo ya sameta da wayarta a hannu, yana zuwa ya sunkuya ya sumbaci bakinta ya d'ago, kallonshi tayi tace "Sir har ka shirya?"

Saida ya shafi k'asumbarshi ya tsaya da kyau gabanta yace "To ya? Nayi kyau ne?"

Saida ta mishi da hannuπŸ‘Œtace "Ka had'u ba kad'an ba, sai fatan Allah ya kad'e idon mak'iya a kanka."

Murmushi ya mata ya juya yace "Saina dawo."

Mik'ewa tayi tabi bayanshi har bakin k'ofa, saida ya sake rumgume ta sannan ya juya zai tafi sai kuma ya tsaya ya juyo, kallonta yayi yace "Kin kira kankana ne tunda ta tafi?"

Saida ta d'an bud'a baki tace "A'a."

"Me yasa?" Ya tambaya yana kafeta da ido, saida ta turo baki tace "Yah Ammar k'aryata ni fa tayi gaban mutane, bayan kuma nasan bata son tafiya."

Saida ya wani tausasa murya yace "To sai me? Ki kirata kiji ya take, kinji ko?"

Yana fad'a ya fita ya barta, ciki ta dawo ta d'auki wayarta ta zauna ta kira yer uwarta, a lokacin bata tunanin ganin kiran Amna amma sai gashi ta gani, da farin ciki ta d'auka ta kara a kunne tace "Banyi tunanin zaki kira ni ba?"

Daga b'angaren Amna tace "Pourquoi?"

Daga kwance Hamna tace "Parce que je sais qui tu est."

Murmushi tayi ta gyara zama tana fad'in "Kamar yanda na sanki ba, fad'a min ya kike?"

Bata tsaya dogon tunani ba tace "Tante Aissata, elle est très méchante."

Dariya Amna tayi tace "Je sais, shiyasa ma na hanaki tafiya dan nasan babu yanda za ayi kiji dad'in zama da ita."

Hamna dake kwance a gado tace "Manta da ita kawai zanyi maganinta, fad'a min ya kike?"

Saida ta sauke numfashi tace "Lafiya ta lau."

Daga b'angarenta murmushi tayi tace "Est ta nouvelle vie?"

Cike da farin ciki tace "Bansan ya zan kwatanta miki irin farin cikin da nake ciki ba, ina cikin farin ciki sosai rabin jikina."

Da mamaki Hamna tace "Da gaske? Ammar fa Amna?"

Dariya tayi tace "K'warai kuwa shi, zakiyi mamaki idan kika ga yanda muke zaune dashi."

Zaune ta tashi tace "Amnaaa, anya kuwa? Kamar ya koya miki son shi ko?"

Cikin murmushin daya sub'uce mata tace "Si je le te dit la vΓ©ritΓ© je le te dit oui."

Kamar sukar mashi taji a zuciyarta, tsam tayi kamar zata saki wayar, zuciyarta saida ta buga saboda jin abinda ta fad'a, to ita meye makomarta kenan? Tana d'auke da banzan cikinshi fa, ba zai yiwu ba gaskiya, dole tayi gaggawar tsayar da wannan abun haka, ba zata juri jin wannan kunyar ba, jiki a sanyaye Hamna ta amsa mata da "...


*Alhamdulillah*

*Yawan sharhi yawan rubutu.*
14/10/2020 Γ  00:58 - Ummulkhairi: πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨
*BADAK'ALA*
πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

πŸ‘¨β€πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘¦ _*AHALI NA*_πŸ‘¨β€πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘¦


πŸ’«βœ¨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝

β˜† *[ T.N.A]* β˜†πŸ–ŠοΈ


_Bismillahir rahamanir rahim_

_45_


"Abun mamaki, na d'auka zaku jima baku saba ba."

Murmushi tayi tace "Nima haka."

Hamna ce tace "Amma dai kina shan duka da rashin kunya?"

Dariya tayi sosai kafin tace "Toi mΓͺme tu le sais."

Fira sosai sukayi cike da kewar junansu kafin daga bisani suyi sallama. Ammar ma fitarshi wajen lieutenant yaje, shi kad'ai ya samu kan makeken lallausan karfet kishingid'e cikin k'ananan kaya yana sha iskar mangwaro dake kad'awa, zaunawa yayi shima yana fad'in "Abba barka da hutawa."

Zaune ya tashi yana fad'in "Har ka iso?"

"Um Abba." Ya fad'a yana d'aukar roban ruwa ya d'aga kai yana tsiyayawa yasha, saida ya gama ya kalleshi yace "Abba ka ce na zo, lafiya dai ko?"

Tank'washe k'afafu lieutenant yayi ya kalleshi a nutse yace "Ammar, ina so ne na sani, meye matsalarka a rayuwa?"

D'aga kai yayi ya kalleshi ido cikin ido, kamar mai son fahimtar wani abu sai kuma ya kawar da kansa yace "Soyayya, da kuma k'auna."

Mamaki ne ya cikashi sosai na abinda ya fad'a, kallonshi yayi sosai yace "Ban gane ba."

Murmushi yayi yace "Ba zan iya cewa komai ba Abba, kayi tunani ka fahimci abinda nake nufi, amma ka sani nayi jarumta sosai da har ban iya gallabarku ba, yara irina da suka rasa abinda nima na rasa wasu su kan kashe kawunansu, wasu su kan kashe 'yan uwansu da ake nuna musu fifiko akansu, wasu kuma su fad'a shaye shaye da tunanin samun mafitar matsalarsu, wasu suna zama 'yan ta'adda ko kuma su fi k'arfin iyayensu, wasu kuma a wayi gari su k'i iyayensu su tsanesu, idan sun girma zasu iya mantawa da su suma, Abba duk abu d'aya yakan iya jawo wannan matsalolin, rashin samun kulawa daga iyayen da suka haifeka, wanda ma basa ganinsu a doron duniya ya suka k'arata bare kai da kake ganinsu kuma sunyi watsi da kai?"

Wuri d'aya ya kafe da ido yana kallo da daskarewar tunani ta yanda baya tuna komai a k'walwarshi, jin shirun yayi yawa yasa Ammar kallonshi, murmushi yayi ganin yayi kamar gunki ya rik'o hannunshi, suna had'a ido ba tare daya daina murmushin ba cikin rawar murya mai kama data kuka yace "Abba, ka daina kirana d'an iska bana jin dad'i, bana son kana hantarata musamman a gaban mutane, ina so ka dinga sa min albarka kana min addua'r alkairi."

Sakin hannunshi yayi ya sunkuyar da kai, siraren hawaye ne yaji sun taho mishi, hannu yasa ya share ya d'ago ya kalle shi, tausayin shi ne ya kama shi sai kawai ya zuro hannu ya dafa kanshi, sake kallonshi yayi sai kawai zuciyarshi ta karye ya fashe da kuka, cikin tashin hankali ya matso kusanshi ya fara share mishi hawayen yana fad'in "Kai lafiya? Meye na kuka kuma? Yi hak'uri mana kaji, na daina daga yau ba zan sake ba."

Tafukan hannaye yasa ya rufe fuskarshi ya kwantar da kanshi kan k'afar lieutenant, daddab'a shi ya fara yana rarrashi, da k'yar ya tsagaita da kukan amma bai d'aga daga k'afarshi ba, sun jima haka kafin ya tashi zaune suka fara hira, sosai suka ji dad'in wannan lokacin saboda hirar fahimtar da sukayi, har ta kai ta kawo lieutenant yana sanar dashi harkokinshi na yau da kullum, k'aratowar magrib tasa su d'aukar makullan motarsu suka bar wurin.


*Bayan wata uku*

Rayuwa tayi dad'i sosai a b'angaren Ammar da Amna, zama suke na fahimtar juna da girmamawa, duk da kalmar so bata tab'a shiga tsakaninsu ba amma wata kalmar idan ya zage damtse ya mirgino mata ita kanta har kasa d'auka yake, babu kasawa a salon kulawar da yake nuna mata, haka kuma babu kasawa a salon muguntar da yake mata, zamu iya cewa soyayya ce da kuma wahala, yanzu haka har ta saba da muguntarshi, ba wuya zai kai mata k'ulli ko zagi, kuma a take a wurin zai ce ta yafe mishi, dan haka bata sa wannan a matsayin abun damuwa ba.Yanzu haka Allah ya azurtasu da samun k'aruwa, ya rub'anya kular da yake mata, shiyasa ya daina tab'a lafiyar jikinta idan dai ba kashe arna yake ba wanda baya wasa da kashe su. A b'angaren Abba ma yanzu komai yayi daidai, aiki kam lieutenant shi ke abinsa, amma kasuwanci kuma duk ya damk'a ragamar hannun Ammar da Amar, shima kuma Amar yana ganin tashi kalar cutar, sai dai kuma shima ya saba kamar yanda matarshi ma ta saba.

Jamila ta gama k'osawa da halin da matar yayan nata take mata, so da dama idan suka had'u saita dinga mata shagub'e da jirwaye mai kama da wanka, tana ninketa ta baibai da wasu maganganun da bata iya gane su ba, ga Huda da take ta k'ok'arin tusata a gurin mijinta ko yaushe, tana hana su shak'at ba dare ba rana, gashi shi kanshi Jibril d'in ta fahimci ya d'an canza daga yanda yake, sai dai har yanzu ta kasa tambayar kowa sai k'unsar bak'in cikinta take ita kad'ai, amma yanzu kam daf take da tayi magana dan abun ya gundureta.

Hankalin Ummy ya tashi sosai ganin har anja watanni ba'a maganar dawowar Hamna gidan, hakan yasa kawai ta shiga ta fita har saida ta kasance d'aya daga cikin wanda zasu tafi information a *France* na wata shida, tayi murna sosai dan haka ta kira Hamna ta fad'a mata komai, a wannan rana basu kwanta ba saida Hamna ta samu mafita kan yanda zatayi ta bar gidan nan, ba gidan kad'ai ba duka garin, dan ita kanta tana so ta tafi kafin cikinta ya shiga wata na biyar har a gane halin da take ciki, gashi masifar Aissata ta isheta, jarabar yau daban ta gobe daban, uba kuma ba mai zama gida ba, ko yana garin ma saita kwana ta wuni basu had'u ba ko a tsakar gidan.

Cikin ikon Allah ko da ta fad'a ma Gambo tanti *Gishata* (k'anwar Ummy) take neman alfarmar taje *Agadez* (asalin Ummy in baku manta ba) ta dinga kwana a wurinta saboda mijinta baya nan, girman Ummy da kuma kimarta na yanda ta raini yaran yasa bai iya mata musu ba yace ya amince ta tafi, amma karta bari Hajia taji dan zatayi fad'a, dad'i sosai taji na barinta da yayi. Da kanshi yasa dreba ya d'auketa sai Agadez inda suka had'u da Ummy anan ita ma da shirin tafiyarta. Gishata tayi mamakin ganinsu lokaci d'aya, bata sare ba saida Ummy tace France zasu je, tambayarsu tayi sai Ummy tace kawai tayi hak'uri idan sun dawo zasu fad'a mata, amma ta musu alk'awari d'aya shine ko wani ya tambayi Hamna karta nuna ta san inda take, sannan ita ma Ummyn bata so kowa yasan ta zo, hankalinta ya tashi da tunanin abinda ke faruwa, amma sai Ummy tace tayi alk'awarin fad'a mata komai idan suka dawo, sannan kad'ai ta d'an nutsu tare da musu fatan alkairi a sanda

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login