Showing 6001 words to 9000 words out of 325849 words
da kallo, tab'e baki tayi tana gunguni tana fad'in "Kamar dai ba *Sa'ada* ce ta haife shi, ita faran faran da mutane, shi kuma sai shegen tsamin rai, Allah ya sawak'e maka."
Yana shiga ya mayar da k'ofar ya rufe, makullin mota da wayarshi ya aje akan tamk'amemen teburin dake gabanshi tare da zagayawa wajen wani d'an dogon k'arfe ya zago fara kuma doguwar rigarshi ya saka, abin sauraren numfashi ya d'auko kamar zai saka a kunnuwa sai kuma ya sagalashi a wuya, kujera ya ja ya zauna ya gyarawa abin auna hawan jini zama, wani k'aramin coffre ya bud'e ya d'auko wani farin gilashi ya saka a idonshi, masha Allah, abinka ga kyakyawa kuma farin mutum, sai yayi kyau cikin shigar kamar ka daga da bredi, matsalar d'aya ita ce d'aurewar fuskar nan da babu annuri a cikinta, wani babban littafin ya d'auka ya ciro alk'alami a jikin rigarshi ta ciki ya fara rubutu, ba jimawa da fara rubutun kuma aka k'wank'wasa k'ofa tare da bud'awa aka shigo,sam baiyi alamar yasan da zuwan mutum ba saboda ko d'agowa baiyi ba, har saida matar ta zauna tare da kafeshi da ido, saida ya gama abinda yake ya d'ago a hankali ya sauke ido akan matar na yan dak'ik'u, hannu ya mik'o mata alamar ta bashi katinta da kuma takardun rahoton lafiyarta, da sauri ta mik'a mishi saboda ita tsoro ma ya bata, saida ya gama dubawa da rubuce rubuce bai kalleta ba yace "Ki kwanta kan gadon can."
Tashi tayi ta nufi wajen gadon da aka keyawa ba'a iya ganin wanda ke ciki ta kwanta, tashi yayi ya fara dubata na wasu mintoci kafin ya dawo ya zauna, dawowa tayi ta zauna ita ma tana kallonshi yana ci gaba da rubutu, ya jima kafin ya mik'o mata takardun sai takardar siyan magani yace "Wannan takardar ki bawa wannan likitar dake zaune."
Wata takardar ya mik'o mata yace "Wannan kuma asiyo wad'annan magungunan yanzu, dukansu kina buk'atarsu domin zasu taimaka miki."
Mayar da kanshi yayi k'asa ya fara rubuce rubuce, tashi tayi ita kuma ta fita jiki na rawa dan tayi abinda yace, da haka Ammar yake duba duk wani majinyaci daya shigo har saida lokacin tashinshi yayi, ak'alla awa biyu ya d'auka a asibitin kafin ya tattara ya nufi gida a gajiye, wasu mintuna ne suka kawo shi gida, yana zuwa kuma a k'ofar gida ya samu Hamna tare da wata k'awar ta akan moto da alama tafiya zatayi, tsaki yayi ya shige ciki kai tsaye kuma b'angarensu na samari ya wuce, tun a falon ya tarar da su Amar da su Junaid, kallonsu kawai yayi ya nufi na shi d'akin, Junaid ne yace "Likita bokan turai, baka so a mutu baka so a zauna lafiya, daga asibiti ake halan?"
Tsaye yayi ya rik'e k'ugu ya kalleshi kamar zaiyi magana sai kuma ya wuce, Jibril ne yace "Oh mu 'yasu, mu dai mun shiga uku kam, jama'a namiji da jan aji da yanga kamar wata sabuwar bazawara, wannan naga mai auren shi a duniyar nan."
Dariya Amar yayi yace "Za kuwa ka ganta da idonka, ai irinsu kuma Allah yake had'awa da masu shegen surutu."
Karaf Jibril yace "Kamar irinsu Hamna ba."
Wata harara Junaid ya wurgo masa yace "Ka rufa mana asiri kafin zaman d'akin nan ya gagare mu, yana jin wannan maganar a bakinka Allah saiya maka tiyata a baki."
Dariya suka saka inda suka ci gaba da tattaunawa cikin nishad'i, amma abin haushi duk hirar dangin nan da suke Ammar na d'aki na jin hayaniyarsu yayi shiru har bacci ya d'auke shi.
*Washe gari*
Jiniyar motoci ce ta tashi wasu daga cikin mutanen gidan, daga ciki har da Ammar da Hamna da kuma Amna, sanin ko waye yasa Hamna ko suturta jikinta bata tsaya yi ba daga kayan baccin dake jikinta ta fito, da gudu take saukowa daga matakalar tana fad'in "Abbanmu ya zo, Abbanmu ya zo, Abbanmu ya zo."
*GVR* de Maradi (gwamnan Maradi) *Harouna Suley Hassan Gaga* (Gambo) kenan, mahaifin Hamna da Amna, wanda suke kwashe watanni basu saka shi a ido ba saboda yanayin aikinshi, yanzu haka ma yayi sammakon zuwa ne sabida k'arfe *09:00* zai halarci wani taro na k'addamar da wata sabuwar gidauniya da za'a bud'e, shiyasa ya zo dan ya samu ko da awa biyu ne da iyayenshi, 'ya'yanshi wanda yan uwanshi ke kula dasu da kuma sauran 'yan uwa, kuma bayan rabuwarsu da mahaifiyar su Hamna ya auri wata mata mai sunan *Salamatou*, yar asalin garin Niamey ce bazabarma (zarma), suna tare da ita acan babban birnin niamey, shiyasa ganinshi ma ke zama aiki, dan ko a waya ka kirashi sai ka taki sa'a kake samunshi.
Masha Allahu, gaskiya 'yan biyu akwai kyau kuma kyauta ce ta Allah, uwa uba kuma 'yan uku, cikin d'an takon hanzari yake shigowa falon tare da yi wa masu tsaron lafiyarsa alamar su jira shi, Hassan da Hussein da suka fito cikin shirin fitarsu kowane da kayan aikinshi ne ke tunkarowa suma saboda ganin d'an uwansu rabin jikinsu, sak iri d'aya su ukun, kayan jikinsu ne kawai ya banbanta su, sai dai kuma shi Gambo ya d'an fisu kumari, ganin irin farin cikin dake kan fuskokinsu yasa ya yanke shawarar k'in fad'a musu abinda ya kawoshi, zaiyi shiru har kowa ya gama tafiya wajen aikinshi, kafin su dawo kuma yasan ya bar garin, rumgume juna sukayi dukansu saboda farin ciki, ba jimawa suka raba jikinsu suna kallonshi, Hassan ne ya d'an bugi tunbinshi yace "Meye haka kai kuma? So kake ka zama luti ka barmu, wato kana so a dinga cewa kaine babba garemu ko?"
Murmushi yayi ya gyara babbar rigarshi ta shaddarshi ruwan madara wacce ta dace da shi yace "Ai babba babba ne, kaifa ka fara zuwa duniyar nan kafin mu, kaga kuwa dole mu baka girmanka."
Cikin had'add'en fuskar da babu annuri Hussein dake gyara d'amarar shi ta kakinshi na soja yace "Girman guda nawa ne, ko na minti biyar fa bai kai ba."
Kallonshi Hassan yayi ya kai hannu yana k'arasa sakawa Hussein d'in mab'allan rigarshi kamar wani yaro yana fad'in "Soja mazan fama, ai ka ma rik'e girman nawa na bar maka."
Dukansu ne suka juya saboda muryar Hamna dake kiran Abbanmu ya zo suka kalleta, ganin riga da wando ne a jikinta na bacci yasa Gambo daka mata harara har yana mata nuni da yatsa yace "Maza kije ki canza kayan nan, wai ke yaushe zakiyi hankali ne?"
Cak ta tsaya tare da turo baki gaba, juyawa tayi harda bubbuga k'afa ita bata so ba, Hassan ne yace "Daga zuwanka fa ba zaka fara takura min 'ya ba."
A lokacin Hussein na gyara zaman jar hularsa mai d'auke da lambar girma yace "Idan ya takurata ka kira ka fad'a min, zan nuna maka inda nake ajiyar bindiga ta."
Yana fad'a yasa kai zai nufi d'akin Hajia dan gaisheta cikin wani irin tako kamar wani ingarman doki, (ni fa sai lokacin ma na ce duk d'abi'un shi kamar Ammar, ko kuwa Ammar d'in ne kamar shi) da sauri Gambo yace "Ina kuma zuwa bayan na zo?"
Ko juyowa baiyi ba yace "Zuwanka kuma ba zai dakatar dani daga tafiyar nan da zanyi ba."
Wata tattausan murya ce daga bayansu aka ce "Yallab'ai ga shayin."
Hassan ne ya juyo ya sauke idonshi akan kyakyawar matarshi, hannu yasa ya karb'a yace "Nagode uwarsu Ammar."
Murmushi ta sakar masa mai tsadar gaske tare da kallon Gambo tace "Sannu da zuwa gwamna, ya hanya?"
Da fara'a ya amsa mata da "Alhamdulillah madame, ya muka same ku?"
"Lafiya lau muke? Ya mutan can d'in?"
"Lafiya lau, ya 'yan rigamarki (su Hamna ba)?"
Murmushi tayi tace "Yara na ai sun girma yanzu sun daina rigima."
"To zan gani dai, dan banga alama ba sai dai ko Amna."
Hassan ne ya mik'a mata kofin shayin tare da karb'ar hularshi kalar shud'i ya d'ora akai ya daidaita mata zama yanda a dace, (ikon Allah, idan dai na fahimci wani abu wato duk gidan nan boko ce ta yanke musu cibiya, lallai wasu kayan sai amale), *lieutenant Hassan Suley Hassan Gaga* babban douane na garin Maradi, murmushi ya sakar mata yace "Mu zamu fita kuma sai Allah ya mana dawowa."
Murmushi ita ma tayi tace "To muje na raka ka ko, ko ba kya son addu'ar tawa yau?"
Murmushi yayi daya bayyanar da hak'oran shi yace "Zan iya hak'ura da tenue (kaki) na amma ba dai addu'ar ki ba."
Wucewa sukayi ya dafa kafad'ar Gambo yana fad'in "D'an lukuti saina dawo."
Murmushi kawai yayi yace "A dawo lafiya, madame ke ba zaki tafi wajen aikin ba yau?"
Juyowa Hassan yayi yace "Ai saita fara iza k'eyata gaba take tafiya."
Dariya sukayi suka fice shi kuma ya nufi d'akin Hajia dan ya fara kai mata gaisuwa, Hamna ce ta sake fitowa ta d'oro hijab akan kayan baccinta sai Amna a bayanta, kallonsu yayi da sauri Amna tace "Bonjour (ina kwana) Abba."
"Bonjour." Ya fad'a yana tafiya ya d'ora da "Attend moi ici (ku jira ni anan), je salut mes parents (zan gaida iyayena)."
Amna ce dai ta amsa da "Ok Abba."
Yana isa a lokacin kuma Hussein ya fito, sallama ya mishi ya fito da zuwan saiya dawo, ganin su Hamna zaune a falon yasa ya kallesu yace "Yarana ya dai?"
Gaishe shi suka fara yi, kafin suce wani abu kuma Ammar ya shigo ba sallama, hasalima fuskarshi had'e take saboda yaga kankana a wurin, amma yana ganin kawunshi sai kawai ya k'ame wuri d'aya tare da sara masa wai shi a dole soja ne, shi ma colonel d'in sara masa yayi tare da dafa kafad'ar shi yace "Bien réveillé (ka tashi lafiya)?"
Cikin k'amewa irin ta sojoji ya amsa da "Oui chef."
Kamar wanda suka had'u a filin daga haka shima colonel d'in yace "Da kyau, yanzu kaje ka fara da motsa jiki, kar ka ci abu mai nauyi sosai, sai ka wuce wajen aiki, compris (ka fahimta)?"
Da k'arfi ya amsa da "Tout de suite (yanzu kuwa) chef."
Sai lokacin ya saki jikinshi tare da d'an fad'awa jikin kawun nashi suka yi gaisuwa cikin nutsuwa, sai lokacin yace "Tonton (kawu) na d'auka hutu ka zo mana ai, ya kuma zaka fita yanzu?"
Ba tare daya saki hannunshi da sukayi musabaha ba yace "Ba jimawa zanyi ba, wani taro ne zanje anan *gazawa*."
Ba karsashi yace masa "Saika dawo tonton."
Fita yayi daga falon ya wuce inda zashi, Ammar kuma juyowa yayi inda su Hamna suke zaune, ai yana kallonsu sai kuwaHama ta bushe da dariya, Amna baiwar Allah tana so ta dara amma ba dama, k'ara tsumimiye fuska yayi yana kallonta baice komai ba, ita ko dariya take shek'awa kamar zararra harda tashi daga kan kujerar ta koma bayan Amna tana fad'in "Oui chef, hhhhhhhhhh, tout de suite chef, wayyo cikina harya k'ulle, yer uwa."
Ta fad'a tana tab'o Amna ta ci gaba da fad'in "Allah dai wani ya zare a gidan nan saboda bai samu abinda yake so ba, kullum shine fad'in, oui chef, a vos ordres chef, caca-caca, kai haba ina."
Kwabar dake gefenshi ya kallasai kuwa yayi sa'ar samun faranti na tangaren, d'auka yayi ya saita daidai kan Hamna zai jefa sai kawai kawunshi Gambo ya fito tare da Hajia da kuma Alhaji, sauya akalar farantin yayi cikin dubara ya aje shi mazauninshi, Hamna na ganin haka ta mishi gwalo tare da kwaso wata shegiyar shoki ta watso mishi a fuska tana fad'in "Eh, eh-eh-eh shokiii."
K'wafa yayi a zuciyarshi kawai ya juya ya bar d'akin, lokacin kuma Hajia Husseina da Soueba suka fito tare suma, da haka har falon ya sake cika da iyalin Gaga yara da manya, saidai kowa yana haramar tafiya sabgar gabanshi ne, yara da matasan école (school) suka nufa, sai samarin dake fitowa cikin nasu shirin tafiya ma'aikatunsu.
Hamna da suka saka mahaifinsu tsakiya sai shagwab'a suke masa, Ammar da Amar ne suka shigo tare, k'are musu kallo Hamna keyi tana son banbance boss da kuma Amar a ciki, dan dukansu riga ce chemise a jikinsu kuma fara k'al, kuma dukansu basu b'alla botira biyu ba na sama, haka ma wandon jikinsu mai duhu ne sai dai ba kala d'aya ba, zaka fahimci hakane idan sun matso kusa da kai, sannan takalmin k'afar su iri d'aya ne da kuma gilashin idonsu fari mai kyau, a ciki ba zata iya cewa ga boss ba dan bata gama fahimtar Ammar ne ya saki fuskarshi ko kuma Amar ne ya had'e rai kamar boss, cikin takonsu na zataran maza majiya k'arfi suka k'araso kusan kawunsu, mik'ewa yayi tsaye suka rumgume juna da su cikin farin ciki da k'aunar juna, saida suka raba jikinsu Gambo ya kallesu da kyau yace "Yaran nan raina min hankali zakuyi ko? To a ciki ina Ammar?"
Wani ikon Allah sai kawai Amar ya d'an saci kallon Hamna lokaci d'aya kuma ya d'auke kanshi, ai kuwa Hamna sai cewa tayi "Abba ga boss nan." Ta fad'a har da nuna shi da yatsa.
Tare suka kalleta amma tana had'a ido da Ammar d'in sai taji gabanta ya fad'i da k'arfi, Gambo ne yace "Waya saka dake?"
Turo baki tayi shi kuma ya sake kallonsu sai Ammar daya matso kusanshi yace "Tonton."
Murmushi yayi yace "D'an soja ya aikin na ka?"
Cikin gimtse hak'ora ya amsa da "Pa mal (ba wuya) tonton."
Kafin yace wani abu ya sake cewa "Tonton je dois mon aller (ina so zan tafi), j'ai une visite dan quelque minute ( ina da wanda zan gani nan da 'yan mintuna)."
Kafad'ar shi ya dafa a lokacin Amar yace "Amma dai tonton zamu sameka gida ko?"
Kallonshi yayi yace "Pourquoi tu demande ça (me ya sa ka tambaya)?"
Kallonshi shima yayi yace "Parce que hier j'ai reçu une carte d'invitation en fecebook dans mon counte (saboda jiya na samu wani katin gayyata a fecebook a ma'ajiyata), ce pour cela je demande (shiyasa na tambaya)."
Kallonshi kawai gwamna yayi dan ba zai iya cewa ba haka bane, sai Ammar daya kalli Imminsu wacce ke cikin shirinta yace "Ummi yau ba zaki fita asibitin bane?"
A tak'aice ta amsa da "Ina bayanka."
Kallon gwamna yayi yace "Tonton sai mun dawo."
"Ok yarana, Dieux vous bénisse (Allah ya muku albarka)."
Saida suka sunkuya suka gaishe da Alhaji da Hajia wacce ta hakimce kai kace wata matar gwamna ce, ta tsufa amma bata jin ta tsufa saboda ta tilasta yara suna yin aikin da take so, kowa ya ji k'ara (alerte) a counte d'in shi ita ma sai taji, ko sutura da take sawa kawai ya ishi gidan wasu cefanai na tsawon wata d'aya, saboda k'arfin hali waya ma cewa tayi sai babba take so wanda ake shafawa da hannu, shiyasa in ka kalleta kallon garaje ba zaka fahimci tsufanta ba, yanda Ammar ya gaisheta ne yasa ta yamutsa fuska ta kalleshi tace "Da ka rik'e gaisuwar taka ai, idan baka sunkuya ka gaisheni ba to ubanka har k'asa zan sashi ya duk'a ya gaishe ni, kuma bai zama lalle na amsa ba, imbécile kawai."
😂 *(Romo kenan)*
Ammar kuma da dama shi dai yake jin haushin hana shi abinda yake so da tayi shiyasa basa shiri, juyawa yayi zai wuce ya kalli Ummi data mik'e ita ma, daf da ita ya matso zai wuce ya fita murya k'asa k'asa tace "Ban yafe maka ba in har baka gasheta da kyau ba."
Cak ya tsaya tare da cije leb'e da k'arfi, shi dai ya rasa wace irin rayuwa ce wannan, komai k'ank'antar abu sai Ummi tace ban yafe ba, k'wafa yayi cikin zuciyarshi ya sake juyowa yaje gabanta, zai sunkuya ta d'aga mi shi hannu tace "Wallahi ka durk'usa saina tsinkeka da mari a wurin nan, ni zaka rainawa hankali, in tsuguna in haifi ubanka amma kana jin haushin gaisuwar fatar bakin da zaka min wai har sai uwarka ta saka ka, kenan albarkacinta na ci? To bana so ka rik'e tsiyarka, amma ka tambayi ita kanta uwar taka, ta shigo gidan nan ne saboda ni na zab'i ta shigo, sannan tana zaune a gidan nan ne har yanzu saboda ina so, kuran waya d'aya tak ya isa ya jefa uwarka a layin zawarci."
Ammar dake tsaye zuciyarshi sai bugawa take, hannunshi na dama sai rawa yake yana ji kamar ya kai mata haura guda, k'ara damtse leb'en shi yayi sosai ya kalleta da jajayen idonshi, a hankali ya d'auke idonshi ya kalli gefenta sai kawai Ummi, k'wayar idonta ya kalla ya ga sun cika taf da hawaye, da ido ta mishi alamar "Hankalinka ya kwanta yanzu?"
D'auke idonshi yayi yana ji kamar ya k'urma ihu, tafin hannunshi yasa ya dafe goshinshi yana d'an murza idonshi da yatsunshi ta k'asan gilashin shi, saida ya sauke ajiyar zuciya har sau uku kafin ya sake kallon Hajia, zai kuma durk'usawa dan bata hak'uri cikin tsiwa tace "Na fad'a maka wallahi saina mareka idan ka durk'usa gabana."
D'ago kai yayi daga shirin sunkuyawar ya sauke a kanta, a ranshi yace "Wai ni ya zanyi da tsohuwar nan ne?"
Ummi ya kalla danya nuna mata shifa ba zai zauna anan ya b'ata lokacin shi ba, sai yaga har yanzu wannan kallon ne take masa, ya kuma sani ita ma yanzu in suka je asibiti abinda zata mishi kenan, wani k'aramin tsaki yaja wanda bai ma san ya fito fili ba, muryar Alhaji ta dawo dashi yana fad'in "...
*Tsaka mai wuya Ammar (ka sunkuya Hajia ta mareka, ka k'i sunkuyawa Ummi tace bata yafe ba).*
_Ku bashi shawara_😂
18/05/2020 à 13:48 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
_Bismillahir rahamanir rahim_
_3_
Alhaji ne yace "Kai Ammaru, wuce dan Allah ku tafi wajen aikinku kaji, sai kun dawo."
Da sauri Hajia ta kalleshi wato ita zai rainawa wayo, Ammar na jin haka ya juya cikin takon k'arfi ya fice daga falon, cikin sanyin jiki Ummi tace "Umma sai mun dawo, Abba